《SHIN SO DAYA NE? (Complete)》CHAPTER SEVEN
Advertisement
💘SHIN SO DAYA NE? 💝
TARE DA ALKALAMIN
📝
HAFSAT AL-MUSTAPHA
_Watpadd:Hafnancy_
🌼BABI NA BAKWAI🌼
Page 30-35
Ido cikin ido muke kallon juna ayayin da kowannenmu ke raya wasu al'amura acikin zuciyarsa agame da juna.Kyawun Dr. Mubarak ya wuce yadda nake ta tsammanin gani. Namiji ne tsayayye mai cikar zati da kamala...kwarjininsa mah har wani kashe min idanuwa yake wanda hakan ya sanya nayi saurin kawar da idanuwana daga kallonsa.
Na koma kallon Jasmine wacce tana jin muryarsa ta ruga da gudunta wurinsa tana fadin"Daddy oyoyo wato dazu shine ka tafi ka banni ina ta nemanka ko? "
Lakatar karamin hancinta naga yayi yace"Am sorry babyna nayi laifi ayafewa Daddy... "
Tace"Toh Daddy na yafe maka amma wacece waccan antin mai kyau sosai...? "
Tayi masa wanna tambayar tana nuno ni da 'yar yatsarta ayayin da ni kuma na kasa kunnuwa naji ko mai zai fad'a mata.
"Kawar mominki ce... " hakan naji ya fada tare da nuna Hanan wacce naga yana gama fadin hakan ta juya tabar dakin.
Gabana sai fadiwa yake.... Daddy? Mommy? Kawar mominki?.... I juz nid answers to dix questions da zuciyata ke tambayata akai.
Kaina akasa ina tunanin abinda Mubeen ya fada, "Kawar mominki ce.... " wannan maganar shi yafi tsaya min arai.
"Bugun zuciyata sannu da zuwa..... Please Zahra juz tell me dat am not dreaming....tell me dat ganinki da nakeyi agabana yanzu its reality..." Maganarsa ce ta katse min gajeriyar tunanin da nake.
Hadiye wani katon abu kamar dutse nayi wanda naji ya tokare min mak'ogoro, nace"Mubeen u ain't dreaming.... Its ur Fadima Sa'ad sitting before u.... "
Murmushi naga yayi, sannan ya juya yana kallon Suhaima wacce sai kokarin son boye fuskarta take atsakanin cinyarta, amma kash! ta makaro don ya riga ya ganta.
Nunata yayi da 'yar yatsa yana fadin"Hey! Lil sis I caught u...wato ke mai wayau wai zaki boyemin kada na ganki koh? ... Haha ai tun awaje na gama capturing faces dinku... Gaskiya kina matukar kama da My Zahra.. "
Dago kanta tayi tana dariya, tace"Kai yaya Mubeen wallahi kayi mana wayau sosai... Wato Kai kana ta kallonmu mu bamu sani ba....don't worry ai muma zamu rama"
Yace"Yo! Bah gashi kuma din kun raman ba? Ko kuwa ba kallona dukanku kuke ba yanzu?"
"Hey! Caught one looking at me now... " Ya nuna Ash queen da yatsa wacce kallonsa take amma fuskar nan tata cike yake da alamun tambaya.
Dariya muka sanya duka sai kace wurin shakatawa muke ba gidan rasuwa ba.Anan muka kawo karshen barkwancin da wasannin, muka soma gaggaisawa tare da masa gaisuwar rashin da yayi.
Advertisement
Yace"Oya baby Zahra sauko kuci abinci.... Lil sis, mal. Aysha asauko pls kada abincin yayi Sanyi.. " (Dama yasan Ash queen don ina yawan bashi labarinta)
"Ni akoshe nake.... " hakan na fadi cikin wata irin cool voice wanda ni kaina ban san cewar inada ita bah.
Hararar wasa naga ya jefeni dashi, yace"Ai wallahi baki isa ba.... Baby Jasmine samo min bulala na Zane beautiful antin nan naki don naga bata son taci abincin.. "
Jasmine ce naga tana kokarin fita samo bulalar, ban san sanda nace"Jasmine dawo zanci.... " bah
Dariya akayi duka, yace"Better... "
Shi da kansa yayi serving namu akan plates din da Hanan ta kawo. Tuwon shinkafa ne da miyan taushe wanda yake tashin kamshin spices, miyan yasha namomi dasu ganda.Dayar kular dana ga ya bude wanda Hanan ta kawo daga baya,Fish pizza ce, yana kokarin zubawa kowa ah plate na dakatar dashi "No, ka barshi tuwon mah is okay.... "
Bai kalleni ba balle nasa ran zai tankani, sai dai kawai naga ya cigaba da abinda yakeyi. Ya zubawa kowa nashi sannan ya turawa kowa agabansa yana fadin"Pls ku saki jikinku... Relax and feel at home... Idan kun gama zan dawo don nasan an soma nemana awaje... "
Yana gama fadin hakan ya juya ya fita ayayin da dakin ya rage daga ni sai Suhaima da Ash queen. Ash queen na gama ganin ficewarsa naga ta sauko saman cushion tana gyara zumbuleliyar hijabinta, tayi zaman cin abinci tana fadin"Wallahi Fadima ni matsalata dake kenan akwai iya black market.... Yadda nake ganin wannan fish pizzar nake hadiyar yawu 'yar banza da yanzu ya wuceni Kenan don da'ace wani ne da kika ce wannan tuwon ya ishemu toh wallahi da kila ya sanya ayi waje dashi....... "
"Ai ke wallahi Ayush ba'a iya zuwa bakunta dake awuri.. " acewata Kenan.
Suhaima na gani itama ta sauko kasa ta janyo tata plate din pizzar tana fadin"Ai nima wallahi ina kallo dai pizzar nan bazata wuceni bah.... "
Baki na bude cike da mamaki nace"Laah!! Hadda kema din? Tot u will ghat ma back ashe duk line d'aya kuke da Ash? "
Ash queen tace"Kanwata rabu da ita kinji muja girkinmu ita kuma ta cigaba da shy shy dinta. "
Shiru nayi kawai abina ayayin dana mah dauko wayata ina dan danne danne. Sakon Mubeen ne ya shigo, the message goes lyk diz,
"Baby Zahra please I want to have a talk with you... Idan kin kammala cin abincin please Hanan zata kawoki inda nake don ALLAH.. "
Advertisement
Mikawa Ash queen wayar nayi don taga sakon,atare suka karanta da Suhaima.
Ash queen tace"Yauwa gara mah kije kiji ta bakinsa kam becuz I have alot of questions for u relating to dix Mubarak amma sai mun bar gidan nan sannan zamuyi discussing... I guess u know beta than I do kan tambayoyin da nakeson na miki... But for now juz go and see him first idan Hanan din ta shigo.... "
Hanan ce ta shigo dakin taga kowa nacin abincinsa amma ni sai tabe taben waya nake.Rokona ta hau yi kan na dan taba wani abin mana koda kadan ne. Dakyar dai ta sami na tsiyaye lemun kwali ah cup nasha amma duk nacinta naki naci abincin.
Mummy ce tayi sallama ta shigo dakin rike da hannun Jasmine.Muka amsa mata sallamarta. Cike da fara'a tace"Takwara sannunku da zama... Kune da wani dawainiya haka da yawa... Ai ko zuwa gaisuwar da kukayi its okay ai basai kunyi wata hidima ba... Allah ya saka da alheri.. "
Kaina aduke na amsa cike da kunya"Haba mummy wannan ai ba wani abu bane..... Allah dai yayi masa aikin gafara
"
Tace"Ameen thumma amin.... Yanzu d'an gidan nawa ya sameni yamin bayaninki da kyau wai ashe ke friend d'insa ce daga Zaria......"
Da sauri na d'ago kai muka shiga kallon juna da Ash queen da ita Suhaimar, kafin na maida kallona zuwa ga Hanan wacce naga tayi saurin dauke kanta daga kallon da nake mata.
"Ehhhh.... Ha.. Ka..ne mum... my" Na sami kaina da stammering ayayin maida mata da amsar tambayarta.
"Assalamu alaykum mummy kizo kinyi baki suna falon baki... .... "
Da sauri na dago kaina na zubawa halittar daya shigo dakin wanda shine wanda yayi furucin nan.Zan iya cewa tunda nake arayuwata ban taba ganin namiji mai kyauwu,hankali da nutsuwa ba kamar wannan don yadda yayiwa mummy furucin nan anatse yayita. Atake Anan naji kawai ya birgeni.
"Toh Injiniya gani nan zuwa.... "
Idanuwanmu suka hade ayayin daya juya zai fita, ahankali ya furta"Sannunku..... " wanda idan bawai ka kasa kunnuwa bane toh tabbas bazaka iya jin meya fada ba.
Azuciyata nace"Nasan koh ba'a fada min ba wannan shine
Mummy ta mike tana fadin"Don Allah kuyi hakuri ina zuwa." Ta fice ayayin da Jasmine ta bi bayanta.
Magana muke son muyi atsakaninmu amma presence din Hanan awurin ya hanamu.
Hanan tace"Anty yaya na jiranki awaje wai kizo please..."
Kallonsu Ash queen nayi, Ash queen din ta min Signal alamar inje din.
Kallon Hanan nayi sannan na furta"Toh muje... "
Ahankali na mike nabi bayanta muka fice daga dakin. Tunanin abubuwa barkatai suka bi suka min yawa agame da Mubeen because ni banga wani kwakkwaran bayani da yayiwa 'yan'uwansa agame dani ba don zan iya cewa kamar Hanan dince kawai tasan relationship din dake tsakanina dashi....."toh Wai meke shirin faruwa dani ne? " tambayar dana yiwa zuciyata kenan wanda na tabbatar amsar tambayata yana tattare da
So nake nayiwa Hanan tambayoyi Amman sai na sami kaina da jin nauyinta.
Har kofar gida muka fito alokacin duk mazan dake zaune akofar gidan duk an watse.
Juyowa tayi ta kalleni tace"Anty waccan Ash colour din motar Shine aciki, nan zan barki kije ki sameshi....... "
Idanuwana ne suka kai gun motarmu, da sauri na tuna cewar tare dafa driver muka zo kuma ni ban ganshi awajen bah.kafin nakai ga tambayar Hanan batunsa kawai juyowar da zanyi naga har ta shige cikin gida.
Sannu ahankali na soma takawa zuwa gun motar da ta min kwatance. Motace k'irar 'Mercedes benz ML350'.
Ina kaiwa gun motar naga ya fito yana fadin"Babyna dan shigo muje mu sami wani wuri muyi magana.... Promise not to spent more than 30mins there..... "
Ahankali na furta"Mubeen how can I trust you? "
Cike da mamaki yace"Fadima u mean u don't trust me or what? .... Na rantse da wanda raina ke hannunsa I mean no harm to u.... I juz want to reveal to u the real da kike tare da.... Please Fadima trust me..... "
Ahankali na saukar da ajiyar zuciya, nace"Shikenan muje tunda har kayi rantsuwa da Allah... Amma ka sani idan har ka cutar dani tabbas iyayena bazasu taba yafe maka ba.... kuma ka cika alkawari please kada mu wuce 30mins... "
Yace"Hmm Fadima kenan duk naji..... "
Daga hakan muka shige motar ya tadata muka bar layin...................... 📝
Hafnan's POV
I know dat u guys are really confused as I am now.... Buh lets chill and watch out for Episode eight which will answer the following questions.....
(1)where is Mubeen taking Fadima Sa'ad to?
(2)Is he really hiding his relationship with Fadima from his family?
(3)Who is Hanan to Dr. Mubarak? cuz as we can see she's the only one dat knows abouh his relationship with Fadima Sa'ad, and lastly
(4)Where is Mal. Iroro?
Yanzu wasar zata soma armashi.....
YOURS
©QUEEN HAFNAN©
Advertisement
- In Serial28 Chapters
Imperial Academy
Higher than a commoner and lower than most nobles, Morgan Kiath is unable to fit in amongst the other students and even after a few dull months at the Imperial Academy he has not made a single friend. Yet his monotone life is about to change when he meets Marith Sian a thoughtless foreigner with little regard for Imperial traditions and hierarchy. In no time at all Morgan’s rather bleak existence is given colour by Marith and the friends that are inexplicably drawn in around the foreigner. Soon Morgan even meets his future master, the enigmatic Archmage Aspartos Mudreth and once more his life shifts in direction.Follow Morgan on his rather unexpected journey as he attends the Imperial Academy, fights an incurable disease and is apprenticed to an Archmage who is more than a little out of the ordinary.
8 132 - In Serial10 Chapters
Hero's Exodus
Over the last five years, children of Earth have been brought to various worlds, becoming Heroes in their own rights. And ever since a few months ago, they have been returning. With new bodies and the abilities to cast magic, they have disrupted the flow of everyday life. Leoric, a human turned Ice Elf, has finally returned after hundreds of years, with only a few years passing on Earth. Brought in by a mysterious organization who seeks to protect the Heroes, Leoric longs for the chance to see his family again and somehow return to society. And to do that, he vows to combat anything that stands in his way. Be it fellow Heroes, this mysterious organization, or the unknown dangers to come.
8 84 - In Serial44 Chapters
Rebirth and Second Chance [Dropped]
Keltor enjoyed his life until the day he died but he was reborn into a new life and a new world that teaches him many things before finally returning to his original world but that's when things really begin. I've stopped writing for this, but it's possible at some point I may post a new chapter. I'll leave this story up.
8 151 - In Serial11 Chapters
The Blessed Princess
Long long ago, there was a time of eternal harmony, when pain and anguish ceased to exist. The world was united as one under the rule of a glorious goddess. But this goddess made a stupid mistake, and chaos rained through her lands. Her people fought and fought, and she lost control over her creations. To sustain peace, she destroyed herself, and her remnants scattered throughout the lands and into the souls of her people. Her last words were to her daughter, the goddess of love, whom she had cherished, "Though I cannot fix the mistakes I've made, I can wish my people to be happy. No more endless pain. No more raging wars. Love, please. Save my world. Restore hope into the eyes of those I've created." She became the forgotten goddess after her world lost its ruler. First Princess Azulia was born a human with a shocking resemblance to the forgotten goddess. Her hair was ink black, and her eyes glimmered like priceless sapphires. Her features were uncanny in similarity to the goddess, even in the way she held herself. Though the goddess's eyes were more like icicles, Azulia's resemblance was enough to make you think twice. Azulia was raised with the mindset that she would be the future Empress of Hydrangea. It was a destiny placed out in front of her and carefully sorted out. Those around her directed her life like a pawn. Until one day, comes the beak of time, and her destiny points in another direction. Azulia must learn to break the tension her family shapes and create a destiny of her own. Her world depends on it, even if it means she must destroy herself.
8 118 - In Serial17 Chapters
Chasing Rainbows
(🌈#2) A quirky love triangle between two gays and a girl who's busy chasing rainbows even though there's no pots of gold on the other end- just chaos. Rainbow-colored chaos./on-going.
8 190 - In Serial20 Chapters
Sweet as Venom
Gabriella left home to find freedom. But ended up finding something completely different; and that was Saxon.
8 157

