《ƘADDARAR RAYUWA》K page 104
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
ALHMDLLH ALLAH YANUNA MANA KARSHEN WANNAN LITTAFI KAMAR YANDA AKA FARA LPY YAU ALLAH YAKAWO ANGAMASHI LPY,
KUSKUREN DANAYI ALLAH YAYAFEMIN,
WANDA NA BATAWA DALILI RUBUTUN WANNAN LITTFI YAYAFENI AJIZANCINE IRINNA D'AN ADAM, NIDAI NAYAFEWA KOWA ALLAH YAYAFE MANA BAKI D'AYA."
Page 104
Ta dauki tsawon lokaci bata sake yimasa maganar karin aure ba domin wancan lokacin babu yanda batayi dashi akan ya amince ba amman yaki ita aganinta idan tabawa zancen lokaci zaisa ya fahimceta kuma ya amince,
Shiyasa zata bari tasmau lokacin daya dace da zancen idan yaki kuma tasamu Umma dan Ummar da kanta ta fada mata Nabila mutumiyar kirki ce,
Ta tabbata idan Umma tayi masa magana zai amince."
Sauri takeyi tagama shirya abincin da take masa na musamman don tarbarsa tayi wankata shirya kafin su iso don sunyi tafiya shida mai martaba satinsu daya basa nan, daga ita har yaran sunyi kewarsa sosai, dan tun aurensu bai taba tafiya yakwana basa tare ba,
A gaggauce tayi wanka ta fito tashirya sannan ta gabatarda Sallar isha'i domin bata yitaba tana kan aiki tayi dare a aikin,
Karfe tara dai-dai yashigo gidan Tana zaune a falo dama tun datsu tanajin motsi take lekawa ko shine wani lokacinma ba motsin bane kunnenta keji mata kamar motsin saita mike,
Dasauri ta mike ta karasa gareshi kafin ta karaso ya bude mata hannayensa tana zuwa ta shige hadeda sauke ajiyar zuciya maida hannayen yayi ya rufesu ya kankameta sosai tayi luff a kirjinsa tana shakan daddadan kamshin dake jikinsa,
Ajiyar zuciya ya sauke ta dago ta kalleshi shima ya kalleta hure idanuwanta yayi ya lumshe ta sake budesu akansa, Ta maida kanta ta kwantar dai-dai yanda zuciyarsa take bugawa a hankali ta furta "zuciyarka tana bugawa da sauri, tayi kewarki dayawane shiyasa take bugawa dasauri,
Murmushi mai sauti tayi sannan tace "to ai gani nan saita sassauta bugu, lips dinsa ya goga akan nata sannan ya Saketa ta kamo hannunsa kai tsaye yanda ta shirya masa abinci ta wuce dashi dan tasan halinsa a yanzu abincin kawai yake bukata,
Saida yaci ya koshi dam sai santi yakeyi yana fadin irin wannan gara haka toh gaskiya zan ringa tafiya idanna dawo nasamu tarba ta musamman,
Uhm-uhm nikam rufamin asiri basai ka tafi kabarni da kewarka ba kana zaune agida ko kana kwance akan gadonka zanna shirya maka gararda tafi wannan,
Dariya yayi sannan yace "nima dai jikin naji da bama tare dare tsayi yake yimin, nima nawa wajan hakanne tafada sannan ta tattare kayanda sukaci abincin dan itama jiransa tayi yadawo tukunna,
sannan suka tashi suka wuce daki rage kayan jikinsa yayi zai shiga wanka ya dubeta yace "zo muje ki rakani nayi wankan, kafada ta noke masa yace "shikenan tunda bazai taimaka minba yawuce kai tsaye yaje yayi wankansa ya fito tana zaune tana jiransa ta fito masa da jallabiya ta ajiye gefen gado,
Tana kallonsa tatashi zuwa gaban mirror tadauko mayin da yake shafawa ta zauna tace "karaso ba taimaka maka ka shafa mai,
Barshi na gode wanda ya iyayin wanka da kansa shafa mai ai bazai bashi wahala ba, dariya dayi kawai danta fahimci zancennasa,
Zuwa yayi ya suri man ya ajiye agefe yace "barshi tukunna saina sake wanka na biyu,
Yana fadin haka bai jira amsarta ba yayi mata rumfa akaro na biyi tare suka sakeyin wankan suka fito suka shafa man amma jallabiyar data dauko masa kam saida aka sake wata dan anyi bidiri akanta,
Kwana biyu da dawowarsa yana zaune a falo shida yaranda itakuma tana kitchen dan tanada musu abunsha,
Advertisement
Tashigo hannunta dauke da tray da glass jug mai ruwan garai ana iya kallon abunda yake ciki da kananun cups guda biyu,
Ta dubi Hameeda tace "dauki kaninki kuje kidauka muku abunshanku yana falo na harda snacks na hada muku karku dawo idan kungama zamuyi magana da abbanku, mikewa sukayi su dukansu kafin Hameeda takai kofa Muhammad yafice danyaji zancen snacks,
Sai bayan sunfita ta dauki cup din tazuba masa ya karba yakai bakinsa ya shanye ya ajiye hadeda Hamdala ta dubeshi tayi murmushi shima ya maida mata murmushin, zameww yayi ya kwanta akan kujera itama ta kwanta akansa amma ta dago fuskarta tana kallon tasa,
da magana a bakinki inajinki,
Uhm Dama maganar auren danace maka inaso kayi kaga ita Nabeela anrigada ansan halinta nima ai bazance maka ka auri wacce ba'asan Halinta ba, dan Allah kaduba lamarin,
Tsayawa yayi yana kallonta na wani lokaci sannan ya tuntsure da dariya dukan kirjinsa tayi a hankali sannan taturo baki tace "abun dariyama nazama maka?
Eh yabata amsa atakaice,
Tashi take kokarin yi ya riketa ta hade rai tace "sakeni mana,
Maganarkice kawai tamin dadi tunda har kikace bazaki sakani na auri wacce ba'asan halinta ba,
Abuna na farko zan fara da baki Hakuri bazan iya kara aure dan wani dalili daban ba,
Abu na biyu itafa nabilarda kike fada banma santa ba bana iya tuna rayuwarda nayi da ita, dode bansaniba banajin ko hannunta na taba rikewa a zamanmu da ita,
Yaci gaba da fad'in ranar
Naje na sameta munyi magana saida Gaban Sawwama yafadi dam jin wannan maganar, kuma zancen danake miki yanzu har tayi aurenta danni dai bazan iya auranta ba koda kuwa hakan zai faranta miki rai,
Kamar yanda na fada miki inaso zaman gidana yazame miki zaman wanda baki tana irinsa ba kuma inaso zaman ya kasance ya fita daban dako wani irin aure da kika tabayi a rayuwarki,
Inason aurena yazamana shine aure na karshe da zakiyishi mutuwa kawai zata rabamu kuma ina fata ace alokacin da mutuwar zatazo mun tsufa mun ajiye jikanu yanda bazaki sakeyin wani aurenba, koda mutuwa mukayi inaso kizama uwargidata agobe kiyama,
Hafsa ina sonki ina matukar sonki bazan iya hada soyayyarki data wata mace ba, ni adalin namiji ne shiyasa nakeso na amshe sunana matsayin adali banaso na sauka a hanya,
Yana magana Hawaye suna zarya akan kumatunta itakam wace irin Godiya zata yiwa ubangiji? Aduk lokacinda ya kwace wani abu wanda take kallon batada kamarsa a wajanta saiya sauya mata da wanda yafishi,
Ita dai Allah yagani tana sa'ar mazajen aure adalai wanda sukasan kima da darajar mace tana addu'a yayanta su zama kamar iyayensa yanda matansy zasuyi alfahari dasu,
Kifa kanta tayi ajikinsa kuka yanaso ya kwace mata amma bataso hankalinsa yatashi dan haka saita hadiyeshi."
Cikin kidima da tashin hankali take kwala masa kira kafin ta iso dakin a bakin kofa sukayi kicibus hankali tashe yana ganinta ya rukota cikin tashin hankaki yake tambayarta Sawwamaty yayane menene yafaru,
Tana kuma take fadin wani abune yakemin motsi aciki, kafin ace me shima ya kidime arude yakai hannunsa cikin aikuwa yaji abun ya bugo da sauri yakoma daki yadauko Hijab ya mika mata yace "muje hannunsa yana rikeda nata suka fice kai tsaye asibiti suka wuce ana zuwa aka basu gwaje-gwaje sunanan zaune office din likita, likitan yace tazo tahau gado zaiyi scanning hannunta yana rikeda na Yareema yafar da hasko cikin saiga yaro yana wulgawa a cikin,
Likita ya saki murmushi itada Yareema suka hada ido da dumbun mamaki,
Bayan yagama scanning suka jira sauran test yaduba ya tabbatar cikine da ita harna wata hudu,
Likitan yace "nayi mamakin da akce baki gane cikine dakeba kua haihuwa kamar yanda kikace bata farko ba sai dai har yanzu naga alamun yarinta tattare dake amma duk da haka yaci ace kigane,
Advertisement
Bakya al'ada ne?
Wata biyune kawai banyiba kuma dama nasaba haka shiyasa,
Likita yace "eh wata biyun farko wasu matan dama suna al'ada,
Amma babu wani symptoms da kikaji har saida yafara motsi?girgiza kai tayi tace "ai idan inada cikin nakanyi laulayi sosai wannan kuma banji komai ba,
Jijjiga kai yayi yace "ai kowanne ciki da yanayin yanda yake zuwa wasu harsu haihuwa ko amai basayi sau daya,
Yareema sai yakejin Abun kamar amafarki wai yau Sawwama ce dauke da cikinsa? Zata haifsa masa yara hamdala kawai yake yiwa ubangiji,
Dr Yayi musu bayanin yanda zasu kula da cikin da ita kanta sannan yabasu wasu yan maganinda zasu taimaka sannan suka koma gida."
Kafin su isa Dr yayiwa mai martaba albishir dan yasan zai samu kyautarsa mai tsoka,
Umma ma tayi murna sosai nan aka fara bata kulawa ta musamman duk yanda Yareema yake kulafucin cin abincinta haka ya hakura ya hanata aiki ko A shinfida ma yadaina takura mata kamar baya wanda itakuma hakan yana damunta saida tafito tayi masa magana akan hakan abincinma tace "itakam zata dawo yin kayanta tunda ba laulayi takeyi ba, babu yanda ya iya haka yabarta amma ba kullum ba,
Wata rana dauke mata gabaki daya dawainiyar yakeyi."
——————-
Sawwama ta haifo danta kyakkyawa nai kamada mahaifinsa yaci sunan mai martaba ajere-ajere haka saida ta haifi yara uku duka tsakaninsu bayafin shekara daya mace biyu aza aciki yayiwa Baba takwara Hamisu ta ukun kuma sunan Hajiiya,
Acikin wannna shekarun abubuwa sun faru ciki harda auren Aysha autar Hajiya,
Da Ruma itama tayi aure,
Hajiya suwaiba A sannu a sannu Allah yayita aikoo mata da ifitila'i dafarko Salim babban danta yayi accident yarasu haka yaranta sukayita karewa a hankali a hankali, daga baya saita dawo kamar zararriya gatadai tananan amma saita ringa maganganu babu tsari,
Itakuma tanan Allah ya hukuntata alaifin data aikata,
Mai martaba tsufa ta cinmasa yakama rashin lafiya ganin haka ya sanya rana daya ya sauke daga kan karagar mulki yabawa Yareema,
Daga Yareema har mahaifiyarsa da matarsa gabaki daya basuso hakanba amma babu yanda suka iya mai martaba ya rigada ya yanke hukuncinsa,
Hajiya Babba najin Wannan magana saida ta yanke jiki tafadi abunda taki jini shine ganin Yareema akan karagar mulki gashi yau Allah yabarta araye taga wannan rana taso ace mutuwarta ta risketa kafin ganin wannan rana amma haka Allah yabarta taganta ita a ganinta wannan hukuncin yafi kowanne hukunci tsauri acikin hukuncin da kowannensu yasamu, Hajiy Babba jira dai bakisan tanadin da Allah yayi miki agidan kiyama ba,
Haka Hajiya Babba tacigaba da rayuwa tana kallon wannan kayan Bakin cikin gashi jinya takeyi koda sau daya Hankalinta bai taba gushewa da zata manta waye akan karagar mulki ba Yareema ne ada, Ahalin yanzu yadawo sarki, koda na Dakika daya wannan lamari bai taba bacewa a kwakwalwarta ba yananan zaune daran kullum sai jininta yahau karshe ta kasance kullum jininta yana sama, ko bacci da dare bata iyabi Yareema ne kawai yake kwakwalwarta, kullum addu'arta tamutu amma ina al'amrin ba haka bane Allah ya barta araye dan ganin abunda bataso." (Alokacinda take yiwa Yareema itama batas ta kasheshi so tayi kawai tabarshi araye yayita wahala, akai-akai suke zuwa tisa asirin da suka masa akwai lokacin da Waziri yasamu akasi haka yareema yafara kokarin tashi bakin halinta da muninsa yasa tsawon shekara da shekaru sau daya tataba mantawa da wannan lokaci nayin shirka)
Duk wannan halinda take ciki ita dayanta ne sai masu yimata aiki dan wanda suka hada hannu da ita ganin duniya ta juya mata baya tuni suma suka juya mata bashi,
Gashi Mai martaba ta lafiyarsa yake dan an dagashi gabaki daya daga kasarma zuwa Madina tareda wata daga cikin matarsa."
——————-
A kidime Mummy take kallon Dady da matarda take gefenta da mamaki sai takeji kamar a film wai dama dady yana da aure harda yara uku bai taba gaya mataba saida ta suma dan tashin hankali,
Bayan tadawo hayyacinta Dady yace "kiyi Hakuri amma halinki yasa bazan iya zama dake kadai matsayin mata ba yanzuma halin rayuwa da mutuwa shiyasa nafito na sanar dake sannan nakawo miki ita kiganta,
Allah yagani tun abunda kika aikata shekarun baya kika ficemin araina narasa yanda zanyi shiyasa na sake aure a wannan shekarun,
Mummy tana kuka tace "atadalilin Sawwama ka kara aure? Idan ita Sawwamar nayi mata rashin kyautatawar da ake fada kai me nayi maka? Aakwai wani abunda na rageka dashine? Ina girmamaka inabin umarninka,
Shiyasa har abada bazan taba son wannan yarinya ba aurenta bai kareni da komai ba,
Dady yace "aurenta tabbas ya kareki sai dai kice idonki ya rufe baki ganiba kuma kin zurfafa kiyayyar yarinyarnan yayi yawa da zakiji maganata dakin rage ko kadanne saboda yanzu tayiwa Sadam nisa sanin kanki ne bazata taba dawowa gareshi ba,
Mmummy takaici yasa takasa tankawa dady itaba yanzu tatafi gidana tagirma wa yaji toh itadai sai dai tayi zaman yaranta amma bashiba,
Gasu hassana da Hussaina ta matsa sai sunyi karatu bazasuyi aureba haka mazan auren sukayita fitowa tana korarsu karshe dai yanzu har masters sun gama amma suna zaune babu wanda yayi maganar aure samarinma sun daina fitowa da zarar sunzo anayin maganar su turo sai su gudu dama bata musu lokaci kawai sukazoyi,
Data kira Sadam da fada masa shi kansa baiji dadin abunda dadyn nasu yayiba babu wanda zai hanashi kara aure amma ai da saiya sanarda iyalansa."
—————-
Sadam Gabaki daya ya kwashi iyalansa suka zo kasa zasuyi hutun shekara Hafsa tana shirin kaiwa Hamdan kamar yanda suka saba duk hutu itake kaishi yace wannan karon Abida takaishi,
Rai baiso ba haka tashirya tatafi tayi mamakin irin rayuwarda taga Sawwama tana ciki tanaji ana fada amma a zatonta zuzuta lamarine saida tazo ta ganewa idonta,
Sai ciccin magani takeyi Sawwama dariya kawai tayi dan Abida dai ahankali kawai dai tun lokacin data mata barazana ansamu sauki,
Sawwama ta karbeta sosai har itama abidan tadan saki jiki da zata tafi tasa aka hada mata sha tat da ta arziki tadawo gida."
Sawwama ita ta shirya ta maida yaranta dan akwai bikin Hindatu karshen wata shiyasa zata tafi dasu gabaki daya Har yarinyar Dr Sajida kanwar Muhammad kenan a wajansu tayi hutu yanz zumunci sukeyi sosai atsakaninsu da Sawwama ana huti take aiko mata da yarinyar wajan dan uwanta."
Mai martaba Haleefa kamar yahana Sawwama tafiyar Haka yakeji domin bata saba tafiya tabarshi ba gashi duk ta tattare masa yaransa."
Awannan bikinda zasuyi Mai martaba Halifaa ya yiwa baba kyautar gida Babba gudumawar bikinsa sun rigada sun tare dan acikina za'ayi bikin,
Mahaifin Baba kuwa Sawwama ta gyara musu nasi ginin yadawo na zamani tabiya musu makka kuma,
Mama wacce ake yiwa kallon kaskanci a zummar tana haihuwar mata itace yanzu tazama abun kallo dalilin yaya mata, kowa yaci albarkacin Yaya mata,
Anyi biki lafiya an watse aka kai amarya gidanta nan Mai martaba Haliifaa yafara kiran waya akan tadawo domin ko daurin aure dayaso basu haduba,
Kwana uku kawai takara akai tadawo ita kadai tabar Muhammad wajan Hajiya ya karasa hutu Hameeda ma wajan Babanta duk ana gama hutu zasu dawo sauran kuwa tabarsu gidansu sai wanda take goyo kawai tadawo dashi dake tasake haihuwa."
Mai samu shigowa gidaba sai dare yana shigowa sai mita yakeyi yana fadin tatafi tabarshi ba yara shi kadai yatsina fuska tayi tace "eh ai dama zamada mace daya yagaji haka harararta yayi yace "naji kuma bazan kara matar ba kinyiwa kanki daga yanzu kindaina zuwa biki,
Tabe baki tayi tace nikoh tsoro kakejine, eh tsoro nakeji sai akayi yaya
Haba kaifa sarkine, ni sarki a wajansu ba amma wajanki ni mijine, Ta bayanta yazo ya rumgumeta yana fadin me kika tanado minne,
Dayawa amma fadi me kakeso,
Ya sanya kansa a wuyanta yana shakar kamshin turarenta yace "ki karanci zuciyata nasan kinsan abunda nakeso,
Juyowa tayi suka fuskanci juna tareda hade labbansu waje daya,
Sawwama saida ta haifawa Haalifaa yara bakwai atakaice yaranta goma ciff,
Haka rayuwa tacigaba da tafiya musu cikin so da kaunar juna."
Sawwama&Haliifaa live a happily ever after."
TAMMAT BI HAMDULILLAHI
Alhamdulillah dukkan godiya ta tabbata ga Allah madaukakin Sarki daya bani ikon kammala wannan littafi."
Wannan littafi na sadaukar Dashi gabaki dayansa Ga Mahaifina Da Mahaifiyata Allah yakara muku lafiya da nisan kwana, ina alfahari da kuka kasance kune mahaifana iyaye nagari."
Gaisuwq da Jinjina Gareki Anty Rashida My biggest supporter, Allah yasaka miki da alkahiri yabaki zuri'a dayyiba, Allah yabaki yaranda zasu zame miki sanyin idaniya."
Gaisuwar ban girma gareki Addana Maryam Bawa Allahua raya mana zarah yayi mata albarka🥰
Anty ummi Allahya kare gabanki da bayanki Allah ya raya miki zuri'a, Allah yashiga tsakaninki dakowani irin mugun abu,
Anty Sadiya ina matukar kaunarki Allah ya raya mana yaranmu yayi musu albarka."
Hafsat Bawa My babysis Sawwama taci wannan suna ta dalilink Allah yabaki miji nagari."
Meelar gumel mutumiyar arziki Allah yasaka miki da dumbin alkhairansa."
————
Zayanb Bawa Novels ina gaisuwq gareku
Nagode sosai Masoyana masoyana littafaina Saimun Hadu acikin novel dina nagaba BIBIYATA YAKEYI."
Ku bibiyeshi kamar yanda kuke bibiyar dukka Rubutuna."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial39 Chapters
Memories of Eternity
This is my first story A person with the weight of a universe on his shoulders. A sole survivor of a cosmic disaster, carrying on the legacy of his people. What will happen when he wakes up from his slumber in a new, but familiar universe? And what will he do when he has passed in his legacy, when he has fulfilled his purpose? All Selene ever wanted to do was have a peaceful time as Head. But when a strange planet suddenly appears in the galactic core, she knows it will get very hot very fast. What will this anomaly bring her, and why are the Conduits singing? All chapters marked with a (M) are from the perspective of the MC All chapters marked with a (S) are from the perspective of Selene All chapters marked with a (G) are from the perspective of George All unmarked chapters are from various other minor characters' perspectives, as well as from an outside perspective.
8 234 - In Serial29 Chapters
Knight-Merchant: Reincarnated into a Fantasy World. (LitRPG)
Reincarnated into a fantasy world, Jeremiah, an old soldier turned successful engineer of a futuristic universe, must become something he never was and live another life in the strange world of Arden. LitRPG. Full Blurb: Dying while trying to save a young girl's life during a store robbery, Jeremiah, a middle-aged former soldier who fought hard to find peace and happiness in the wake of the aftermath of a bloody and universal-scale war, finds himself the victim of a suspect paperwork mix up in the afterlife. Told that he won't be able to be reunited with his wife and daughters even after death, at least until the issue is resolved, he is given the chance to enter the litRPG world of Arden to pass his time. Having found solace in the full-dive reality games of the future, Jeremiah reluctantly agrees, but he soon finds that this world is no game. Born with a low Luck stat, our hero is thrust into the middle of the reality spanning machinations of an outer god-like entity known only as The Corruptor. As the bleak truth of the new and harsh world sets in, he will have to fight for every inch of ground he's given, but if there's one thing an old soldier knows how to do... it's to close with and destroy the enemy. Determined to find the same peace he once did in his birth universe, Jeremiah and his family, both newly given as he's born into Arden and freely chosen as he fights his way through it, will struggle against dragons, demons, and Fate herself--along with much worse entities--to claim a lasting happiness of their own.
8 249 - In Serial16 Chapters
Dark Mage: The Offer
Over a millennia ago a dark mage sealed the first contract with the Demon Emperor. He opened a rift and Demons spilled into the world before collapsing. The demon race has tirelessly warred with the human race since that time and slowly expanded its territory into the human lands it has conquered.A youth lives quietly in an unassuming village. Having lost his mother, he has lived under the kindness of those that used to be strangers. He has learned diligently, trying to repay their love and care. However, a darkness approaches and our 'shy hero' will have to learn to confront it while walking in its shadows. He is a dark mage and he will have to learn of the responsibilities that status entails as well as its struggling reputations amongst the human populace.
8 185 - In Serial43 Chapters
My meme collection
Look, I'm bored okay.This is my meme collectionNot my memes bye luwlThank you Pinterest
8 208 - In Serial47 Chapters
Full Moon {A Sesshomaru x Reader} ^w^
You are a full blooded dog demon. A female one at that. You have two swords. Shi is the blade of Death, while your other sword, Ha is the blade of darkness. They can be combined to make a naginata and can be used as one. The Naginata is called Shinha also known as Death blade. You are powerful and you travel alone. That is until little Rin finds herself in trouble and begs someone to let you come along. Who is this someone? Find out in this wonderful Book.(Description of you)Hair: Long and silverDress Attire: Blue short Kimono with a tanish brown obi and ankle length boots (like sesshomaru) Swords: Shi and HaLikes: Children, Traveling, ignoring Jaken, protecting Rin, hitting Jaken, Sesshomaru, and annoying Inuyasha.Dislikes: When Jaken calls her names, Kagura with Sesshomaru, other demons, humans, emotions.Alwight let's get this party started! Start readin now!
8 126 - In Serial512 Chapters
After Fishing For 10 Years, I Became A Saint Without Knowing How To Raise Beasts
Yu Chi transmigrated to a world covered with savage, barren lands, where more than 10,000 races fought to ascend to the top. He began his life in this world in imprisonment. While the others had completely forgotten about his existence, he took out a bamboo stick that he had been carrying with him since his previous life. The souls of ancient divine beasts could be found in various savage lands and rivers. His bamboo stick could communicate with these ancient souls. When he fished at the Death Sea of Hades, he got the voice of Naga Siren. When he fished at the Ice River of Skeletons, he received the attack power of Blobfish. When he fished at the Lake of Grotto-Heaven, he obtained the golden eyes of the Five-Talon Divine Dragon. When he fished at the Cliff of Hanging Candles, he acquired the fire of the Nine-Tailed White Fox. In the blink of an eye, millions of years had passed. Deities and pet beasts from various corners of the world came to congratulate Yu Chi on his wedding. A prominent figure couldn’t help but ask, “Why are you so terrifying?” As Yu Chi stared at his gorgeous wife, the memories of him fighting millions of devils in the Underworld flashed in his mind. He then smiled and replied, “There’s nothing I can boast about. I was just lucky.” Thank you for reading After Fishing For 10 Years, I Became A Saint Without Knowing How To Raise Beasts novel @ ReadWebNovels.net Read Daily Updated Light Novel, Web Novel, Chinese Novel, Japanese And Korean Novel Online.
8 342

