《ƘADDARAR RAYUWA》K page 103
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 103
Already sun san address nasu Sadam kafin su isa sun rigada sunyi booking motarsa zatazo ta daukesu ta yanar gizo sun rigada sun tura address din batareda bata lokaci ba suna sauka suka motar ta daukesu tafiyar minti hamsin ce tsakanin filin jirgin da gidansu Sadam Har kofar gidan motar ta ajiyesu suka karasa suka danna bell,
Shiru na wani lokaci suka sake dannawa, bude kofar akayi Hameeda ce Sawwama tatsaya kallonta kawai yarinyar ta girma sosai ga tsayi yanzu tana 7years kenan amma girmanta kamar wacce takai 10yrs, Hameeda ta ihu tace "Ammie da mugun mamaki Sawwama ta juya tana kallon Yareema bata taba tunanin Hameeda zata ganeta ba, Tabudi baki zatayi magana Hameeda ta daka tsalle ta dale ta da murna itama Sawwaman ta kankameta,
Hamdan ne yabiyo bayanta yana dubawa yaga mahaifiyarshi da murna ya karaso yana fadin Ammie, Sawwama cikeda fara'a tace "na'am hamdan amminka ce, cikin nutsuwa ya taho ya rumgumeta Hafsa wacce take tsaya bayansu dan tun kwala ihun Hameeda suka fito tace "kubar Ammintaku tasamu karasowa ciki, hamdanne ya saketa ya riko hannunta Hameeda kam kamar za'a kwace mahaifiyartata taki sakinta,
Yareema kallonsu yakeyi cikeda sha'awa uwar da yaran sai duka suka bashi tausayi,
Suka shige ciki gabaki dayansu suka zauna kan kujera daya daga Itada Yareema Hameeda ta dale cinyarta shikam dama muhammad na makale da Yareema,
Hamdan ne yace Hameeda bazaki sauka ma Ammie a cinya ba kina bata wahala ya kalli Sawwama yace "Ammie ki tureta Sawwama tayi murmushi ta riko fuskarsa tace zo kaima ka zauna kaji bazakuyimin nauyi ba,
Kamar wanda yake jira yazo ya shige jikinta,
Saida Hafsa tayi magana kafin tadago ta dubeta ita harta ma manta da zamanta a wajan, cikeda fara'a Sawwwama ta gaisheta ta amsa itama fuska a sake,
Sai can Sadam ya fito dake shi bacci ma yakeyi tunda bai fita aiki ba baiyi expecting zuwannasu da wuri haka ba,
Saida gabansu su duka yafadi, da suka hada ido karfin guiwa tasamu ta sakar masa murmushi saida yayi ajiyar zuciya sannan shima ya sakar mata murmushi,
Sawwama ta girma ta zama cikekkiyar mace Sawwamat daya sani ya aura a shekara GOMA SHA SHIDA itace tazama haka idanba ace matsayinda take dashi wajansa ya sanya bazai iya mantataba toda tabbas bazai iya gane Sawwama ba,
Daga ganinta zaka tabbatar tana rayuwa cikin jin dadi mai cikeda kulawa da tarayraya, yanzu Sawwama matar manya ce tabbas domin idan wanda baisan Sawwama ba yanda ta juyo ta rikide baza'a taba cewa tunda can ba cikin dukiya aka haifeta ba,
Ya karaso ya zauna gefen kujerar Yareema yabashi Hannu sukayi musabaha,
Bayan sun gaisa ta kalleshi tasakawa zuciyarta dakiya tace "Yaya sadam ina wuni?
Lafiya Alhamdulillahi yafadi alokacin yake kamo hannun muhammad wanda hankalinsa yake kan yan uwansa da suke jikin Amminsa,
Muhammad yaje jikinsa yanata yimasa wasa,
Advertisement
Jin hayaniyarda tayi yawa ya sanya Abida fitowa dan ganin wanda sukaso dafarko bata gane Sawwama ba saida ta isa wajan gabanta yafadi ganin Sawwama tsabar idanuwanta ya rufe bata lurada wanda yake gefen Sawwama ba ta yatsine fuska tafara zantuka, tace "toh wajanwa kikazo kuma? Bayan naji labarin kinyi aure? Aurenne ya mutu kokuma mijinne yasake mutuwa?
Sawwama tayi murmushi mai cikeda takaici tace wajan Wajan Yarana nazo,
Tabe baki tayi tace "koh wajan uban yaranba,
Siririn tsaki Sawwama taja tace "ko wajan ubansu nazo ai ban fadi ba,
Ranta yafara baci tadubi Sadam tace "Yaya sadam har yanzu wannan bata daina halinta ba?
Yaya kake iya zama da ita?
Zata sanya maka ciwon zuciya,
Sadam ya sunkuyarda kai kawai yarasa mai zaice shikma baisan wace irin mace bace Abida,
Gidan ubanwa zai kaini da kike gaya masa wannan maganganun?
Afusace Sawwama ta sauke Hameeda dake gefentata cafko hannun Abida tayi hanyar waje,
Babu wanda yayi kokarin yin magana bare asamu mai dakatarda ita,
Ita kanta Hafsa kallon ikon Allah kawai takeyi ashe karamin kishi Abida keyi da abida, bata taba kallon tasantsan kishi a fuskarta ba irinna yau dataga Sawwama,
Suna kaiwa waje Sawwama ta banko kofa ta rufe babu mai iya jiyosu ko ganin abunda sukeyi,
Sawwama tasaki hannun Abida data biyota kamar rakuma, cikeda bacin rai tafara magana tace "Ashe har yanzu kina wannan halin dabbancin naki?
Wai sai yaushe zakiyi hankali? So kike kisa sakawa Yaya sadam ciwon zuciya?
Abida zata kuntuma mata Ashar tayi saurin dakatarda ita tace "A'a yanzu ba daa bane ki iya harshenki, koda wasa, yakamata ace yanzu kiyi hankali kisan cewa na girme miki a tsara,
Ba wannan ba abunda na jawoki na fada miki kashesi jan kunne dakuma shawara yakamata ace yanzu kinyi hankali kinbar wannan kauyancin,
Da mamaki Abida take kallon Sawwama, Sawwaamarda abaya ko yatsa aka sanya mata bazata ciza ba yau itace take kashedi,
Kuma niba wajan mijinki nazo dukda banace banzo danna ganshi ba saboda inada aurena inada iyalina acan gefe kuma inajin dadin rayuwata, toh Amma babu yanda na iya har indai bazaki canja hali ba bazan iya kallon Yaya sadam cikin matsala ba zan iya kashe auren nazo na aureshi, tunda dama bawai nadaina sonsa bane yananan acikin zuciyata ko kadan bai raguba sai dai kawai soyayyar ta rikide daga da aure zuwa ta yan uwantaka,
Yanzu mijina nake matukar so ammahar indai bazaki canja hali ba banda wani zabin daya wuce na dawo cikinku mu zauna, ke shaidace akan irin sonda nake yiwa Yaya Sadam tunda har zai iya rikidewa yakoma kan wani daban, yanayi zai iya dawo dashi muhallinsa na baya, indawo na rungumi yarana, su girma gaban uwarsu da ubansu amma faruwar hakan ya danganta daga sauyawarki,
(Sawwama tafadi wannan kalamanne kawai saboda tanaso ta samarwa sadam zaman lafiya a gidansa Bawai zan zata iya rabuwa da Yareema ba, eh tabbas dagaske ne soyayyar Sadam bata ragu azuciyarta ba saina tausayinsa daya karu kan soyayyar amma ahalin yanzu ba soyayyar aure takeyi masa ba, Sadam shine jigon duk wani abunda tazama a rayuwarta shine wanda ya daura rayuwarta akan hanya, hakkine akanta itam tayi iyawarta dannema masa zaman lafiya acikin gidansa)
Advertisement
Jikin Abida har bari yakeyi jin kalaman Sawwama gani takeyi kamarma yanzu tazo kashe aurenne ta dawowa Sadam,
Calm down Hajiya Abida bawai kashe auren nawa zanyiba idan kika zauna zaman lafiya dashi nima zan zauna lafiya agidana har Abada in sha Allahu,
Ga mamakin Sawwama sai taji Abida tace "kinyi alkawari? Koda yake ba abun mamaki bane idan akayi la'akari da yanda ta tsorata,
Uhm eh nayi alkawari cewar Sawwama amma zan ringa waya da yarana danjin halinda ake ciki, shikenan nima nayi alkawarin bazan sake tada masahankalinba, kin kyautawa kanki Sawwama tace hadeda shigewa gaba tafara tafiya kai tsaye tabude kofar takoma dake ba'ayi locking dinta ba,
Abida tabiyo bayanta suum-summ zata wuce daki sai tajiyo muryar Sawwama tana fadin kizo kugaisa da mijina dasauri Abida ta juyo suka gaisa tawuce daki,
Kowa yanaso yaji Abunda yasa Abida sanyi haka amma babu wanda ya iya tambaya."
Kudi sosai Yareema ya kashewa twins ya saya musu abubuwan tsaraba kala-kala,
Kwana biyu sukayi agidan amma Abida bata shiga harkarsuba sam abun har mamaki yake bawa Sadam da Hafsa sanin rashin mutumci irinna Abida,
Zamanda sukayi Sadam Ya fahimci cewa Yareema na matukar son Sawwama da abunda ta haifa gabaki daya, yanayin yanda yake tarayrayarta sai yakeji inama da awajansa tasamu irin wannan kulawa haka amma yanzuma bai baci ba zai bawa matansa dai-dai gwargwado danya dauki darasin yanda ake lailaya mace kamar kwai."
Ya lura Sawwama tacire duk wani abu aranta ta dauki Kaddararta ta rumgmi gagarumin sauyin da ubangiji yayi mata,
Suna Hira da Yareema,
Sadam yake ce masa lallai Sawwama tayi sa'ar miji Allah yayi mata sauyi yadubizyciyarta,
Murmushi Yareema yayi sannan yace "nikuma gani nakeyi kamar nine mai sa'ar ba itaba domin ban taba cin karo da mace mai kyawawan dabi'u kamarta ba, murmushi mai ciwo Sadam yayi yace "kuma bana tunanin har Abada zakaji wannan karon,
Sawwama nada kyakkyawar zuciya Cewar Yareema kuma bata manta halaccida bakinta tacemin bazata taba mantawa dakaiba domin kai shigone arayuwarta, a hankali a zamana da ita saida nafahimci wanenen kai,
Nasan cewa KADDARAR RAYUWA ce tazo mukj ahaka amma soyayyar da kuke yiwa junanku banaji akwai abunda zai rabata, tacemin har Abada bazata daina sonka da ganin girmankaba sai dai soyayyar da take maka yanzu tasha bambam data baya,
Eh ai dole zata sha sun bambamta cewar Sadam soyayayrda takemin abaya yanzu tadawo kanka domin ka kwaceta,
Dariya dukansu suka saka,
Haka idan suka zaune sukeyi sun ringa hirarraki kenan,
Kwanansu 5 suka shirya tafiya, Hameeda tayi kuka ba kadanba saida su dukansu sukaji babu dadi babanta yayiwa Yareema Alkawarin ana hutu zai kawosu sannan da zarar Hameeda tagama primary zai basu ita gabaki daya danya lura tana matukar son mahaifiyarta,
Godiya sosai sukayi masa har ita kanta uwar taji dadin hakan sosai,
Haka suka tafi cikeda kewar juna har suka tafi Abida bata sake tada musu rikici ba."
—————-
Tun daga wannan lokacin duk hutu sai Sadam ya kawowa Sawwama twins sunyi hutu a wajanta daga karshe ma yabata Hameeda gabaki daya."
Sun shiga na shekara biyar da aure amma Sawwama shiru,
Ranar ta shirya tsaff tasamu Yareema adakinsa sai dai tana taraddadin yanda zai dauki zancenda taje masa dashi,
Zama tayi gefensa saida yagama karanta shafin da yake sannan ya rufe alqur'anin yajiyo ya dubeta, murmushi ta sakar masa shima ya maida mata, matsonan ki fadamin meke tafe dake dannaga bakinann kamar akwai magana,
Wani murmushin tasake saki sannan tamatso ta kwanta jikinsa tayi kasa da murya tace "ina waccar shekarar da mukaje saudi yace "ehem inaji mai yafaru acan?
Mun hadu da wata sunanta nabila mun gaisa ta ganmu tare dakai shine take cemin itace tsohuwar matarka bayan mundawo sai nake tambayar ruma tabani labarinta tanada kirki sosai ta kula dakai,
Se akayi yaya? Ya tambaya da mamakin abunda Zai biyo baya,
Uhmm dama nace ko zaka aureta idan andace sai kaga Allah yabamu yara ta wajanta, tunda kaga auranda tayi bayan naka bata zaunaba,
Da mamaki yake kallonta yace "Anya! Anya kina sona kuww? Kowace mace na gudun kishiya ke kinaso?
Ni nace miki nadamu da yarane? Wanda nake dasu sun isheni, balle me menene na kara aure? Tunda naga aike kin haihu idanma da matsala ko wajena ne, kinga bbu wani amfani kara auren har indai akan hakanne,
Turo baki Sawwama tayi tace "ina sonka mana kaima kasani wannan sai dai kafada kuma kishiya nifa duk aurenda nayi na zauna da ita,
Shafa gashin girarta yayi yace "toh ni agidana karki zauna da ita sai gidana yafita daban kamar yanda nima nafita daban,
Uhmm kawai tace zata mike ya dawo daita yace ai baki idaba dawo nan, indawo inyi mene bayan kaki jin shawarata,
Bari kiga mai zakiyi yafada yana rumgumota,
Kokarin kwacewa takeyi yace "tsaya mana toh kiga nima na gwada sa'ata shammatarsa tayi ta fauce kasancewar tasan yaran basa gida yau zasusha soyayyarsu yanda ransu yake so,
Tana sauka daga gadon tafara tafiya a hankali shima yabi bayanta yana fadinta tsaya ya gwada sa'asarsa ganin yana shirin cimmata ya sanya ta kara sauri taku uku ya kara ya cafkota rumgumeta yayi da karfi saida tasaki nishi, yace ""ni kike kaiwa kasuwa koh? Waina kara aure toh naki sayuwa kici gaba da zamada abunki haka babu maiso,
Tana kokarin kwacewa tace "kabari kagani idan nayi tallah daka wawa za'ayi dan kowa naso,
Tsayawa yayi yana mamaki wai dagaske Sawwama aure takeso yakara?
Shidai baitaba kallon matarda takeso dan karan kanta ayi mata kishiya ba sai ita, shikuma dai ara'ayinsa baida niyyar auren mata samada daya kuma har yanzu hakan yakeji aransa,
Tana kokarin kwacewa ya dauketa cakk bai ajiyeta ko'inba sai cikin dakin nishi ya tsaya yanayi tana dariya yace "Allah kin kara nauyi sosai,
Uhmm ai gara na kara kar nayita cin abinci ba'asan yanda yake tafiya ba."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial21 Chapters
Anathum: Quest for the End
As you wake up with no memories of your past, you are thrown into a world that defies all logic, will you be bested like all the others? Or will you... Anathum is a massive universe that is governed by a mysterious System, within this world, Damien must grow stronger in order to uncover the true purpose of the game everyone is forced to play. - I've always wanted to create a litrpg since I first started reading them a few years ago and today I decided what the hell, any feedback is graciously welcomed. I will try to do daily updates (I feel that if I put that into writing I will be forced to do it!)
8 208 - In Serial18 Chapters
Eve of Gods
Maugus(The Preserver) was defeated by the other two members of the Supreme Gods Trinity in a war over faith by; Brom(The Creator) and Siva(The Destroyer). To save his life, he reincarnates as an Earthling. Ahan, an aimless webnovel writer, finds out that he is the reincarnation of a god from another world. He has lost a war over faith, all of his believers killed and his territory and kingdom divided between the gods. On top of that, he now has to save his last believer, or face death. This is the tale of an earthling-turned-god, who built a battle game server and transported players from Earth straight to the other world using virtual reality, to rise through the ranks of the Gods again, gaining followers and eventually causing another war between the Supreme Gods Trinity: called the Eve of Gods. “Om Namo Bhagavate Vasudevaya.”"I bow down to the Lord who resides in the hearts of all beings."
8 150 - In Serial6 Chapters
Unexpected Friendship
Hazel lost her parents at a very young age since then she had to deal with her protective Aunt Molly and endless bullying but what happens when she meets a Monster Hunter in the middle of the woods? (A/N: This series isn't related to either the movie or the game. This as well as my other books are also readable on Quotev and Wattpad)
8 239 - In Serial16 Chapters
Beyond Mortality
The World is two sided. On one side we see fairness, truth, goodness and the compassion of the Gods. On the other side, we see deceit, corruption, and the uncaring nature of the powerful. Our Main character seeks truth and in that journey, for truth, he sees the world for what it truly is and rebels against it. join him on a journey of truth, revenge, and immortality! I encourage everyone to leave comments and reviews. It will help me in developing and refining the story.The number of words vary between each chaper. I'm not getting a pay reduction or increase regardless of the word count. I just want to create something good. If you have any questions, comment and I'll try to address it. My main website:jakejasblog.wordpress.com I'll be releasing 2 chapters a week to start and if it's well received I'll increase the number.
8 173 - In Serial37 Chapters
Particles of Paradise
Tachibana Yuki (橘幸), sixteen, student, single, a young man who enjoyed playing basketball but reduced to Online FPS games, has his life upturned when a transfer student named Sasaki Naomi (佐々木直美), offers to take him to another dimension named Avalon, where he could learn magic in the Avalon Academy of Magic. How did he end up there? What paths lay ahead of him? And just what is Avalon? Find out answers to all of these with the Protagonist himself in Particles of Paradise. New chapters will come out on every Monday before 2:00 PM IST/10:30 CEST
8 219 - In Serial43 Chapters
I SAID I LOVE YOU
"What did you say?", he asked with quite surprise and amusement in his tone."I love you aadi",i said feebly and weakly."WHAT!!!",this time he nearly shouted..with a bit of anger in his voice ."I SAID I LOVE YOU AADI !! I.....LOVE...YOU(this time i shouted)!Did you here it properly now?", i said.Suddenly,he started lauging like a maniac..."Did u ever look at your face in the mirror....ohh i forgot! Is your family even able to afford a mirror?how did u even dare to confess to me...if possible dont ever show me ur tramp face again",he said!"Please...please just...!",i start to plead."Leave...NOW!",he shouted and i was in tears!-------It started raining,aadi pinned my hands above my head against the car. He had trapped me, his scent overwhelming my senses. I closed my eyes as he got closer and turned my head away. His lips connected with my jawbone instead, he made the most of it and trailed tiny butterfly kisses down my neck and collarbone. He smiled faintly at my gasp of reaction, he lowered the other one to my face and gently pulled my face to face him. He skillfully closed the gap between us devouring my lips and stealing all my ability to think. Without giving a second thought to what I was doing I arched my body into his and kissed him back.He let go of my trapped hands so his could go other places n i pulled him closer."I love you my angel",he said in between the kiss...."what !" ,i asked!.."I SAID I LOVE YOU ANGEL",he replied.I pushed him with all my force..."Angel Please...just please",he said weakly......"Leave Aadi , NOW", i shouted and turned back..through the side window i could see he had tears in his eyes!!*********#32 in general fiction on 10-11-15
8 208

