《ƘADDARAR RAYUWA》K page 102
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 102
Madina jirginsu ya sauka kafin su isa masu taryarsu sun isa wajan a gajiye gabaki dayansu, wani dan madaidaicin gida flat mai kyau suka sauka,
Yana dauke da falo daya dakuma uku, angyare gidan gabaki dayansa, an goge ko'in duk da cewa akwai ma'aikata aciki kullum cikin gyaransa akeyi amma na wannan lokacin dabanne saboda zuwannasu,
Gabaki daya cikin dakunan dake part dinnasu dayane kawai abud gabaki daya an sakala musu key tasan hakanne alokacin databi dakunan tana dubawa, a tunaninta zata sauka a dakinta daban shima nasa daban,
Sai wajan da ma'akatan gidan ke zaune suma nasu dakunan acan yake,
Ala dole haka tashiga dakinsa yake buden wanda tanada tabbaci shine zasu sauka acikinsa,
Kafin suyi komai bayan saukarsu saida sukaci abinci yareema yace bazai iya jira sai yayi wanka ko hutawa ba kafin isowarsu anyi musu abinci anshirya komai jiran isowarsu kawai akeyi, Sawwama ta lurada Yareema sam baya wasa da cikinsa yanajin duku-duku zai nemi abinci,
Ta ta shi tabarshi dakin tashiga kai tsaye tawuce toilet tayi wanka tagyara jikinta dake bata sallah kuma saukar dare sukayi kawai saita kanta kankanin lokaci bacci ya dauketa,
Sai Bayan tayi bacci yashigo yayi wanka shima yayi sallolinda suke kansa ya kwanta,
Kwanansu uku agarin kamar yanda suke gudanarda rayuwarsu a can haka sukeyi anan babu wata shakuwa babu hira daya fahimci idanya zauna kusada ita yana takurata sai kawai yadaina zaman gidama gabaki daya,
Shekarun da yayi yana jinya yaga komai na duniyar ya canja masa gabaki daya, shiyasa fitarma bata damunsa bacci kawai ke hadasu waje daya,
Tunda suka tafi kwana 3kenan bata kira su Mama ba sukuma sunyita nemanta basa samunta saida ta samu hakan yasa batasan zancen zuwansu Sadam ba, saida ya canja mata layi zuwa na wancan kasar kafinnan tasamu takirasu,
Anan mama take fada mata zuwansu Sadam dakuma abunda yafaru bayan rabuwarsu sannan ta shaida mata yanzu sunce sunason abasu yaran zai amshi kayansa,
Sawwama har kuka tayi na tausayin Sadam, Sadam mutumne da kome tazama a rayuwarta bazata taba mantawa da shi ba shine jigon rayuwarta gabaki daya ta tausaya masa sannan tacire son zamada yaran gabaki daya tabar masa idan tasamu hali zata ringa zuwa dubasu sa'i-sa'i adalcin da zata yimasa kenan,
Ta shaidawa Mama itakam a wajanta babu wani damuwa a debi yaran abashi kawai,
Mama da kanta takai yaran Har gidan Dady cikeda kewarsu tayi musu sallama tabar yaran,
Sadam yanajin labarin ankkawosu yafara shirin komawa harda yarannasa kuma yake shirin tafiyar, saida yagama komai ana washe gari zasu tafi yacewa matan su shirya zai kaisu su gaida dady da mummy Kiri-kiri Abida tace masa bazata jeba Hafsace ta shirya ita kadai suka tafi,
Sai lokacin Mummy ta kare mata kallo tabe baki kawai tayi amma taso tayi magana akan zuwa datayi taki fitowa ta gaisheta ganin dady da Sadam a wajan ya sanya bata daga zancen ba,
Advertisement
Da zasu tafi Sadam yadubi dady yace "Dady gobe tashin safiya zamuyi angama shiryasu yakamat muwuce danmu koma mugama shirya abunda bamuyiba,
Dady yace "kayansu kawai za'a dauko ina tunanin komai yana shirye mummy ta kalle su da rashin fahimta tace "wai tafiya zakayi da yaran?
Eh sadam yabata amsa,
Ko menene amfanin tafiya dasu Sadam? Tunda ba mahaifiyarsu bace acan ai saika barsu nan wajanmu,
Dady ne ya karbe zancen da fadin menene amfanin karbosu toh idan ba tafiya zaiyi da yaransa ba?
Mummy ganin dady zai iya kunya ta ta gaban sirika yasanya taja bakinta tayi shiru, Sadam ya tattara yaransa suka tafi washe gari sassafe yabar kasar."
—————
Zaman Yareema da Sawwama yananan ayanda yake ba sabo bare wata shakuwa tashiga tsakani, sun dauki tsawon lokaci a irin wannan zaman, Yareema ya fahimci cewa idan bawai ya tabuka wani abun a zamansu bane Sawwama batada niyyar canjawa zamansu,
Yau kafin magrib yadawo ba kamar yanda yasaba fita koda yaushe sai bacci zai dawo dashi ba, yana zaune cikin gidan kuma Sam yaki barinta ta tabar wajan aiki yake sanyata tana gama wannan zaice takama wannan, daya fita Sallar magrib shine tasamu sarari bai dawoba sai bayan yayi isha'i,
Yana isowa yasameta tana shirin cin abinci ya zauna shima ta zuba masa ta rigadhi tashi yayi mata alamu tadawo tazauna babu musu tadawo tazauna baice mata komaiba saida yagama yamike yace tabiyshi tabishi abaya saida ya sanya ta kunna TV sannan ta mike zata shige ciki,
Dawo nan ya fadi babu musu tadawo tatsaya tana jiran yasake sanyata wani aikin, da hannunsa ya nuna mata gefe yace tazauna, dake wajanda yake nuna mata yayi kusa dashi ya sanya ta nemi wani wajan gefe ta zauna, murmushi yayi ya sanya hannu ya jawota gabaki daya tadawo tsakanin kafofinsa runtse idanuwanta tayi ganin haka ya sanyashi sakin murmushi mai sauti,
Hannunsa ya sanya ya zagayeta sannan ya makala wuyansa anata bakinsa dai-dai kunnenta ya hura mata iska a kunne da sauri ta bude idanuwanta tana kokarin kwacewa amma dake ba rikon wasa yayi mataba hakan yasa takasa kwacewa,
Meyasa kike guduna ko har yanzu baki yafemin bane ya rada mata cikin kunne,
Girgiza kai tayi dasauri,
"Toh menene? Ya tambaya
Bbu tabashi amasa atakaice,
Bakyajin dadin zama danine?
Tayi shiru bata bashi amsa ba hakan ya tabbatar masa batajin dadin zama dashi,
Ajiyar zuciya ya sauke cikin muryar lallashi yace zan gyara in sha Allahu zakiji dadin zama dani fiyeda kowane namiji dakika sani a rayuwarki,
Kai kawai ta gyada masa,
Yajuyoda ita ya tallafi fuskarta kwayar idanuwanta suna kasa amma idanuwanta suna bude,
Dago idanuwanki ki dubeni yace yana kallon ko zata iya dagowwn, kamar yanda yayi tunani dama yasan abune mawwuyaci ta iya kallonsa,
Sakin fuskarta yayi yace "bansan komai gameda keba ko zaki iya sanar dani wasu abubuwan daya kamata nasani? Ga mamakinsa girgiza kai tayi, ko meyasa? Ya tambaya, a hankali ta bude baki tace "zaka sani in sha Allahu lokacine zai nuna hakan, jinjiga kai yayi kawai ganin ya sassautawa rikon da yayi mata ya sanya tayi saurin mikewa batareda ta kalleshi ba tace "zanje na kwanta, mikewa yayi yace "muje tare kamo hannunta yayi suka shiga gabaki daya,
Advertisement
Suna shiga ciki ta zare hannunta daga nasa tace "bari nayi wanka,
"Muje na rakaki yafada hankali kwance, dasauri ta dago tadubeshi suka hada idanuwa nadan lokaci ya sakar mata murmushi tayi saurin kawarda fuskarta, yaji dadin data dago ta dubeshi abunda ya dade yanaso yaga tayi amma taki sai yau,
Ganin dagaske yakeyi zai iya rakata toilet ya sanya ta bude baki tace "kazauna kawai yanzu zan fito,
Lankabarda kansa yayi yace "shikenan tunda bakyaso,
Saida ta dauki rigarda zata sanya sannan tafada wanka, bata dauki lokaci ba tafito danji takeyi kamar zai shigo, saida ta tsantsane jikinta ta sanya doguwar rigar baccinta sannan tafito,
Tana zuwa ta haye gado ta kwanta batasan wainar daya toya ba dan har bacci yafara debenta tajishi ya hayo gadon,
Mirginota yayi tadawo jikinsa ya shafa mata addu'a sannan ya kwanta, gabanta sai dukan uku-uku yakeyi,
Can cikin baccinsaya fara daukanta taji yakira sunanta Hafsa! Uyumm ta amsa cikin muryar bacci,
Agida Sawwama ake cemeki? Uhm kawai tabashi amsa,
Zan iya kiranki da Sawwamaty?
A'a tabashi amsa kai tsaye, dan ambatanda yayi kawai saita taji faduwar gaba,
Ko meyasa ya tambaya yana maison jin ba'asi,
Saboda Yaya sadama dashi yake kirana,
Waye kuma Yaya Sadam?
Baban twins tabashi amsa,
Mirginawa yayi samanta yazamana yana sama tana kasansa, sautin numfashinsu kawai akeji a hankali yace "to ai mi daban shi daban,
Bude baki tayi zata bashi amsa ya hade lips dinsu waje guda a hankali yake bida ita cikin zuciyarta ta rigada tasani kuma tayarda komai nasa yayi dai-dai da zubinta akaro na biyu yasake mantar da ita duniyar da take ciki, zata iya fada ta nanata salonsa daban yake,
A wannan daren saida ya tabbatar yasama musu nutsuwarda ta gamsar da zukatansu sannan komai yalafa."
Cikin kankanin lokaci shakuwa mai karfi tashiga tsakaninsu sai dai ya lura rashin maganarta harda yanayinta tun can baya bawai zallan batason zama kusa dashi bane,
A yan zai yanda tasake dashi ya tabbatar cewa abaya maa laifinsa ne daya jata ajiki toda ta dade ta sakewa dashi."
——————
Watansu shida acan labarin mutuwar waziri ta riskesu a waya kawai yayi musu ta'aziyyya dan bazai koma can kasar kwana kusa ba."
Sawwama saida ta shekara biyu da auren Yareema ko sau daya bata taba batan wata ba,
Abun yafara damunta amma shikam ko ajikinsa,
Yadade da shigowa yana tsaye akanta bata saniba saida ya zagayo ta gabanta sannan ta sanda shigowar tasa, tsugunnawa yayi agabanta akan guiwowinsa yacire hannun tagumi tabishi da kallo,
Tashi yayi ya zauna akan kujerar cikeda kulawa dakuma damuwa da halinda yaganta yace "Allah yasa banine na bata miki ba? Wace damuwa kike ciki haka da har zan shigo ina tsaye akanki bakima san na shigo ba, inada tabbacin Sawwamaty matata ko doso gida nayi takansan cewa mijinta ya kusa zuwa gareta, menene kikeso wanda nakasa baki?
Bana fata wata rana ace na gaza yimiki wani abun dahar zai sanyaki cikin damuwa,
Murmushi tayi ta shafo fuskarsa, yanzu babu sunanda takejin dadinsa kamar yakirata da Sawwamaty,
Tun tana samun kanta da faduwar gaba harta daina hakan ya tabbatar mata da cewa yanzu shi kadaine kawai a zuciyarta,
Jan hancinta yayi yana binta da kallon tuhum, ganin tanaso ta fuske ta share zancen ya sanya ya kafeta da idanuwa, tagane abunda yake nufi shiyasa tafara kame-kame, kamo hannunta yayi yana murzawa a hankali yace "kwantarda hankalinki ki fadamin menene?
Bazata iya yimasa karya ba dan haka tace "yanzu shekara biyu kenan amma, dakatarda ita yayi danya gane yanda ta dosa,
Yace "Nace miki kidaina damuwa akan wannan amma kinaso kiringa batamin raina,
Yaranda kika haifa mana ni sun isheni ko haka Allah yabarni nagode masa, Da zarar munkoma zan Dauko Muhammad yadawo wajanmu da zama,
Twins ma mahaifinsu akwai dalilin dayasa yafimu bukatarsu shiyasa bazan nemi yabani suba,
Amman nayi alkawarin duk hutu zan ringa daukosu sunayi a wajanmu,
Turo baki tayi tace "Allah yasa abamu su,
Za'a bamu kina shirunki, dariya tayi kawai,
Tabbas maganar Yareema nacewa zai kyautata mata fiyeda kowani namiji data sani a rayuwarta ta tabbata kuma haka maganar mutane dasuke fadin kirinsa itakam yanzu tagani, aganinta wannan yabo da mutane suke yiwa halayya irinta Yareema yayi kadan domin halinsa ya zarce haka fii da aniya."
Dake lokacin aikin Hajji yazo ya sanya suka wuce saudi duk shekara acan sukeyi Mai martaba tareda Umma da sauran yan uwa Duk suna zuwa,
Wannan karon hardasu Hajiya tazo mususa Muhammad kamar yanda tayi alkawarin zata basushi daga baya."
Zagayowar wata shekara ya biyama Mama da Baba suma sukazo suka sauke farali."
Saida sukayi shekara uku a Madina kafinnan suka dawo gida lokacin angama yimus gininsu a cikin fada, tsararren ginine mai kyawun gaske wanda ya kumshi parts har guda uku,
Da dawowarsu kai tsaye acan suka tare,
Bayan sun dawo da wata daya suka tafi can kasarda Su Sadam suke,
Dake anrigada an sanarda zuwannasu ya sanya su Sadam suka shirya sai dai yana tunanin tayaya zai fuskanci Sawwama bayan tsawon shekaru da sukayi basa tare?
Shin idan ya ganta zaiji babu dadi?
Zai shiga dimuwa da damuwa?
Kokuma zuciyarsa tarigada ta yafe Sawwama ya manta da ita a sahun auratayya?
Amma tayaya zuciyarsa zata iya mantawa da Sawwama? Sawwamarsa fa?
Wacce yake matumar so da kauna Uwar yayansa wanda Kaddara ta gifta ta raba tsakaninsu,
Hafsa kawai ya sanarwa zuwan Sawwama banda Abida dan baisan tayi masa shirme, itakuwa Hafsa hankalinta kwance tafara shirin tarbar bakinta domin ita a yanz gani takeyi Sawwama tagamma mata komai tunda tadauki yaranta tabata wanda take jinsu kamar itace ta haifesu a cikinta,
Zaman yarannan a wajanta ya sake jawo hankalin Sadam gareta yakara mata girma da kima a idanuwansa, batajin a halin yanzu tanada wani abunda zata sakawa Sawwama dashi."
✔️eote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial17 Chapters
The Star and the Darkness
“When the darkness is at it’s darkest, a star shines brightest.” Humans look up at stars in admiration for the way they shine, but when a star falls to the earth do humans still worship it? What will happen when the brightest star is thrown from the sky into a place she knows nothing of? Praised like a goddess in a temple? Hunted like a prized deer? Devoured by the beasts of the wild? Or maybe something else? A creature that should have been left asleep walks the earth in search of that which was his, restless and unyeilding.
8 130 - In Serial25 Chapters
The Big Bang System
Our protagonist dies at a young age to an unfortunate accident but is startled when she then wakes up in a small wooden shack. Opening the door, what she sees, or rather doesn't see, shocks her... Big Bang System initialising. if you want to ask questions or if you have any suggestions feel free to join the discord https://discord.gg/789xxnv
8 74 - In Serial31 Chapters
Primordial Dimensions
„Finally“ he thought, stepping through the spatial membrane, into the vast and dangerous `Primordial Dimension` where life and death are infinitely close. Having lived a rather short first life that ended unexpectedly, Shane found himself in the body of a newborn baby, within a strange foreign world. Terrifying existences with all kinds of abilities inhabit the planet, caused by the Primordial Dimension´s appearance. Even though humanity was on the brink of extinction, the Primordial Dimensions provided an unimaginable opportunity to reach higher realms, while imminently threatening them with the possibility to be conquered by unknown races. But who would have thought that the destructive and cruel Primordial Dimension where monstrous existences emerged from, would one day become humanity´s ray of hope? Follow Shane Suro on his journey through the vast Primordial Dimensions where he learns about freedom, friendship, cruelty, and betrayal.-->If you want to read more, go check out webnovel.com
8 120 - In Serial11 Chapters
Finding Truth
An excerpt from one of the tracks of the show NAAMKARANN in my own vision, my own plot and my own words... What happened AFTER the media got to know about Juhi being Neil's ex girlfriend and that he has a child with her?? How did Avni and Neil deal with the cunning plans of vidyut and Juhi? Will they succeed in overcoming the hurdles in their relationship? Read on to know the thrilling story of how AvNeil solved their own case with criminal minded people!
8 96 - In Serial36 Chapters
KARNANANYA
MAHABHARAT , the epic saga of every human emotion intimately weaved with dharma ( righteousness) and karma. A tale which changed the course of entire history and led to the downfall of the biggest empire, Aryavrat. But what if the ruination of Aryavrat could be stopped? What if there's no war but yet dharma could be established?What if there's a breach in this saga ? What if it's rewritten by someone with the strength of the entire universe and heart fragile than glass? Let us be part of a history where a woman doesn't has to get insulted and demeaned to establish dharma. A saga where a brother need not kill another one . A chronicle of equality, women rights, dharma, karma , sacrifice, friendship, might , love & time travel . A story rewritten by the Mother of the universe , Devi Adi Shakti ; a tale of change, destiny, dreams and vision. The tale of Legendary Warrior KARN , born with the glory of sun & calm of moon and a girl from Kaliyuga, possessing fire of sun along with beauty of moon . Both determined to change people's perception , challenge societal norms and establish dharma .
8 151 - In Serial8 Chapters
Stardust // Poe Dameron [ON HOLD]
"it's that heart of gold and stardust soul that make you beautiful." - r.m. broderick[ Poe Dameron x OC ]{ The Force Awakens - The Rise of Skywalker }*slow updates
8 254

