《ƘADDARAR RAYUWA》K page 102
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 102
Madina jirginsu ya sauka kafin su isa masu taryarsu sun isa wajan a gajiye gabaki dayansu, wani dan madaidaicin gida flat mai kyau suka sauka,
Yana dauke da falo daya dakuma uku, angyare gidan gabaki dayansa, an goge ko'in duk da cewa akwai ma'aikata aciki kullum cikin gyaransa akeyi amma na wannan lokacin dabanne saboda zuwannasu,
Gabaki daya cikin dakunan dake part dinnasu dayane kawai abud gabaki daya an sakala musu key tasan hakanne alokacin databi dakunan tana dubawa, a tunaninta zata sauka a dakinta daban shima nasa daban,
Sai wajan da ma'akatan gidan ke zaune suma nasu dakunan acan yake,
Ala dole haka tashiga dakinsa yake buden wanda tanada tabbaci shine zasu sauka acikinsa,
Kafin suyi komai bayan saukarsu saida sukaci abinci yareema yace bazai iya jira sai yayi wanka ko hutawa ba kafin isowarsu anyi musu abinci anshirya komai jiran isowarsu kawai akeyi, Sawwama ta lurada Yareema sam baya wasa da cikinsa yanajin duku-duku zai nemi abinci,
Ta ta shi tabarshi dakin tashiga kai tsaye tawuce toilet tayi wanka tagyara jikinta dake bata sallah kuma saukar dare sukayi kawai saita kanta kankanin lokaci bacci ya dauketa,
Sai Bayan tayi bacci yashigo yayi wanka shima yayi sallolinda suke kansa ya kwanta,
Kwanansu uku agarin kamar yanda suke gudanarda rayuwarsu a can haka sukeyi anan babu wata shakuwa babu hira daya fahimci idanya zauna kusada ita yana takurata sai kawai yadaina zaman gidama gabaki daya,
Shekarun da yayi yana jinya yaga komai na duniyar ya canja masa gabaki daya, shiyasa fitarma bata damunsa bacci kawai ke hadasu waje daya,
Tunda suka tafi kwana 3kenan bata kira su Mama ba sukuma sunyita nemanta basa samunta saida ta samu hakan yasa batasan zancen zuwansu Sadam ba, saida ya canja mata layi zuwa na wancan kasar kafinnan tasamu takirasu,
Anan mama take fada mata zuwansu Sadam dakuma abunda yafaru bayan rabuwarsu sannan ta shaida mata yanzu sunce sunason abasu yaran zai amshi kayansa,
Sawwama har kuka tayi na tausayin Sadam, Sadam mutumne da kome tazama a rayuwarta bazata taba mantawa da shi ba shine jigon rayuwarta gabaki daya ta tausaya masa sannan tacire son zamada yaran gabaki daya tabar masa idan tasamu hali zata ringa zuwa dubasu sa'i-sa'i adalcin da zata yimasa kenan,
Ta shaidawa Mama itakam a wajanta babu wani damuwa a debi yaran abashi kawai,
Mama da kanta takai yaran Har gidan Dady cikeda kewarsu tayi musu sallama tabar yaran,
Sadam yanajin labarin ankkawosu yafara shirin komawa harda yarannasa kuma yake shirin tafiyar, saida yagama komai ana washe gari zasu tafi yacewa matan su shirya zai kaisu su gaida dady da mummy Kiri-kiri Abida tace masa bazata jeba Hafsace ta shirya ita kadai suka tafi,
Sai lokacin Mummy ta kare mata kallo tabe baki kawai tayi amma taso tayi magana akan zuwa datayi taki fitowa ta gaisheta ganin dady da Sadam a wajan ya sanya bata daga zancen ba,
Advertisement
Da zasu tafi Sadam yadubi dady yace "Dady gobe tashin safiya zamuyi angama shiryasu yakamat muwuce danmu koma mugama shirya abunda bamuyiba,
Dady yace "kayansu kawai za'a dauko ina tunanin komai yana shirye mummy ta kalle su da rashin fahimta tace "wai tafiya zakayi da yaran?
Eh sadam yabata amsa,
Ko menene amfanin tafiya dasu Sadam? Tunda ba mahaifiyarsu bace acan ai saika barsu nan wajanmu,
Dady ne ya karbe zancen da fadin menene amfanin karbosu toh idan ba tafiya zaiyi da yaransa ba?
Mummy ganin dady zai iya kunya ta ta gaban sirika yasanya taja bakinta tayi shiru, Sadam ya tattara yaransa suka tafi washe gari sassafe yabar kasar."
—————
Zaman Yareema da Sawwama yananan ayanda yake ba sabo bare wata shakuwa tashiga tsakani, sun dauki tsawon lokaci a irin wannan zaman, Yareema ya fahimci cewa idan bawai ya tabuka wani abun a zamansu bane Sawwama batada niyyar canjawa zamansu,
Yau kafin magrib yadawo ba kamar yanda yasaba fita koda yaushe sai bacci zai dawo dashi ba, yana zaune cikin gidan kuma Sam yaki barinta ta tabar wajan aiki yake sanyata tana gama wannan zaice takama wannan, daya fita Sallar magrib shine tasamu sarari bai dawoba sai bayan yayi isha'i,
Yana isowa yasameta tana shirin cin abinci ya zauna shima ta zuba masa ta rigadhi tashi yayi mata alamu tadawo tazauna babu musu tadawo tazauna baice mata komaiba saida yagama yamike yace tabiyshi tabishi abaya saida ya sanya ta kunna TV sannan ta mike zata shige ciki,
Dawo nan ya fadi babu musu tadawo tatsaya tana jiran yasake sanyata wani aikin, da hannunsa ya nuna mata gefe yace tazauna, dake wajanda yake nuna mata yayi kusa dashi ya sanya ta nemi wani wajan gefe ta zauna, murmushi yayi ya sanya hannu ya jawota gabaki daya tadawo tsakanin kafofinsa runtse idanuwanta tayi ganin haka ya sanyashi sakin murmushi mai sauti,
Hannunsa ya sanya ya zagayeta sannan ya makala wuyansa anata bakinsa dai-dai kunnenta ya hura mata iska a kunne da sauri ta bude idanuwanta tana kokarin kwacewa amma dake ba rikon wasa yayi mataba hakan yasa takasa kwacewa,
Meyasa kike guduna ko har yanzu baki yafemin bane ya rada mata cikin kunne,
Girgiza kai tayi dasauri,
"Toh menene? Ya tambaya
Bbu tabashi amasa atakaice,
Bakyajin dadin zama danine?
Tayi shiru bata bashi amsa ba hakan ya tabbatar masa batajin dadin zama dashi,
Ajiyar zuciya ya sauke cikin muryar lallashi yace zan gyara in sha Allahu zakiji dadin zama dani fiyeda kowane namiji dakika sani a rayuwarki,
Kai kawai ta gyada masa,
Yajuyoda ita ya tallafi fuskarta kwayar idanuwanta suna kasa amma idanuwanta suna bude,
Dago idanuwanki ki dubeni yace yana kallon ko zata iya dagowwn, kamar yanda yayi tunani dama yasan abune mawwuyaci ta iya kallonsa,
Sakin fuskarta yayi yace "bansan komai gameda keba ko zaki iya sanar dani wasu abubuwan daya kamata nasani? Ga mamakinsa girgiza kai tayi, ko meyasa? Ya tambaya, a hankali ta bude baki tace "zaka sani in sha Allahu lokacine zai nuna hakan, jinjiga kai yayi kawai ganin ya sassautawa rikon da yayi mata ya sanya tayi saurin mikewa batareda ta kalleshi ba tace "zanje na kwanta, mikewa yayi yace "muje tare kamo hannunta yayi suka shiga gabaki daya,
Advertisement
Suna shiga ciki ta zare hannunta daga nasa tace "bari nayi wanka,
"Muje na rakaki yafada hankali kwance, dasauri ta dago tadubeshi suka hada idanuwa nadan lokaci ya sakar mata murmushi tayi saurin kawarda fuskarta, yaji dadin data dago ta dubeshi abunda ya dade yanaso yaga tayi amma taki sai yau,
Ganin dagaske yakeyi zai iya rakata toilet ya sanya ta bude baki tace "kazauna kawai yanzu zan fito,
Lankabarda kansa yayi yace "shikenan tunda bakyaso,
Saida ta dauki rigarda zata sanya sannan tafada wanka, bata dauki lokaci ba tafito danji takeyi kamar zai shigo, saida ta tsantsane jikinta ta sanya doguwar rigar baccinta sannan tafito,
Tana zuwa ta haye gado ta kwanta batasan wainar daya toya ba dan har bacci yafara debenta tajishi ya hayo gadon,
Mirginota yayi tadawo jikinsa ya shafa mata addu'a sannan ya kwanta, gabanta sai dukan uku-uku yakeyi,
Can cikin baccinsaya fara daukanta taji yakira sunanta Hafsa! Uyumm ta amsa cikin muryar bacci,
Agida Sawwama ake cemeki? Uhm kawai tabashi amsa,
Zan iya kiranki da Sawwamaty?
A'a tabashi amsa kai tsaye, dan ambatanda yayi kawai saita taji faduwar gaba,
Ko meyasa ya tambaya yana maison jin ba'asi,
Saboda Yaya sadama dashi yake kirana,
Waye kuma Yaya Sadam?
Baban twins tabashi amsa,
Mirginawa yayi samanta yazamana yana sama tana kasansa, sautin numfashinsu kawai akeji a hankali yace "to ai mi daban shi daban,
Bude baki tayi zata bashi amsa ya hade lips dinsu waje guda a hankali yake bida ita cikin zuciyarta ta rigada tasani kuma tayarda komai nasa yayi dai-dai da zubinta akaro na biyu yasake mantar da ita duniyar da take ciki, zata iya fada ta nanata salonsa daban yake,
A wannan daren saida ya tabbatar yasama musu nutsuwarda ta gamsar da zukatansu sannan komai yalafa."
Cikin kankanin lokaci shakuwa mai karfi tashiga tsakaninsu sai dai ya lura rashin maganarta harda yanayinta tun can baya bawai zallan batason zama kusa dashi bane,
A yan zai yanda tasake dashi ya tabbatar cewa abaya maa laifinsa ne daya jata ajiki toda ta dade ta sakewa dashi."
——————
Watansu shida acan labarin mutuwar waziri ta riskesu a waya kawai yayi musu ta'aziyyya dan bazai koma can kasar kwana kusa ba."
Sawwama saida ta shekara biyu da auren Yareema ko sau daya bata taba batan wata ba,
Abun yafara damunta amma shikam ko ajikinsa,
Yadade da shigowa yana tsaye akanta bata saniba saida ya zagayo ta gabanta sannan ta sanda shigowar tasa, tsugunnawa yayi agabanta akan guiwowinsa yacire hannun tagumi tabishi da kallo,
Tashi yayi ya zauna akan kujerar cikeda kulawa dakuma damuwa da halinda yaganta yace "Allah yasa banine na bata miki ba? Wace damuwa kike ciki haka da har zan shigo ina tsaye akanki bakima san na shigo ba, inada tabbacin Sawwamaty matata ko doso gida nayi takansan cewa mijinta ya kusa zuwa gareta, menene kikeso wanda nakasa baki?
Bana fata wata rana ace na gaza yimiki wani abun dahar zai sanyaki cikin damuwa,
Murmushi tayi ta shafo fuskarsa, yanzu babu sunanda takejin dadinsa kamar yakirata da Sawwamaty,
Tun tana samun kanta da faduwar gaba harta daina hakan ya tabbatar mata da cewa yanzu shi kadaine kawai a zuciyarta,
Jan hancinta yayi yana binta da kallon tuhum, ganin tanaso ta fuske ta share zancen ya sanya ya kafeta da idanuwa, tagane abunda yake nufi shiyasa tafara kame-kame, kamo hannunta yayi yana murzawa a hankali yace "kwantarda hankalinki ki fadamin menene?
Bazata iya yimasa karya ba dan haka tace "yanzu shekara biyu kenan amma, dakatarda ita yayi danya gane yanda ta dosa,
Yace "Nace miki kidaina damuwa akan wannan amma kinaso kiringa batamin raina,
Yaranda kika haifa mana ni sun isheni ko haka Allah yabarni nagode masa, Da zarar munkoma zan Dauko Muhammad yadawo wajanmu da zama,
Twins ma mahaifinsu akwai dalilin dayasa yafimu bukatarsu shiyasa bazan nemi yabani suba,
Amman nayi alkawarin duk hutu zan ringa daukosu sunayi a wajanmu,
Turo baki tayi tace "Allah yasa abamu su,
Za'a bamu kina shirunki, dariya tayi kawai,
Tabbas maganar Yareema nacewa zai kyautata mata fiyeda kowani namiji data sani a rayuwarta ta tabbata kuma haka maganar mutane dasuke fadin kirinsa itakam yanzu tagani, aganinta wannan yabo da mutane suke yiwa halayya irinta Yareema yayi kadan domin halinsa ya zarce haka fii da aniya."
Dake lokacin aikin Hajji yazo ya sanya suka wuce saudi duk shekara acan sukeyi Mai martaba tareda Umma da sauran yan uwa Duk suna zuwa,
Wannan karon hardasu Hajiya tazo mususa Muhammad kamar yanda tayi alkawarin zata basushi daga baya."
Zagayowar wata shekara ya biyama Mama da Baba suma sukazo suka sauke farali."
Saida sukayi shekara uku a Madina kafinnan suka dawo gida lokacin angama yimus gininsu a cikin fada, tsararren ginine mai kyawun gaske wanda ya kumshi parts har guda uku,
Da dawowarsu kai tsaye acan suka tare,
Bayan sun dawo da wata daya suka tafi can kasarda Su Sadam suke,
Dake anrigada an sanarda zuwannasu ya sanya su Sadam suka shirya sai dai yana tunanin tayaya zai fuskanci Sawwama bayan tsawon shekaru da sukayi basa tare?
Shin idan ya ganta zaiji babu dadi?
Zai shiga dimuwa da damuwa?
Kokuma zuciyarsa tarigada ta yafe Sawwama ya manta da ita a sahun auratayya?
Amma tayaya zuciyarsa zata iya mantawa da Sawwama? Sawwamarsa fa?
Wacce yake matumar so da kauna Uwar yayansa wanda Kaddara ta gifta ta raba tsakaninsu,
Hafsa kawai ya sanarwa zuwan Sawwama banda Abida dan baisan tayi masa shirme, itakuwa Hafsa hankalinta kwance tafara shirin tarbar bakinta domin ita a yanz gani takeyi Sawwama tagamma mata komai tunda tadauki yaranta tabata wanda take jinsu kamar itace ta haifesu a cikinta,
Zaman yarannan a wajanta ya sake jawo hankalin Sadam gareta yakara mata girma da kima a idanuwansa, batajin a halin yanzu tanada wani abunda zata sakawa Sawwama dashi."
✔️eote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial1363 Chapters
VRMMO: The Unrivaled
Lu Chen used to be a ranker of the most popular VRMMO game, Spirit of Grief. After a car accident turned his dreams into dust, his disability left him incapable of escaping the pit of mediocrity he was thrown into. Helpless and defeated, his story ended.Two years later, the Eternal Moon Corporation launched a new VRMMO called "Heavenblessed", and Lu Chen stumbled into another terrible accident that left him in a complicated situation far beyond his ability to handle. That won't stop him from rising to the top, however. Not again.Come witness the rise of the sword-wielding zombie and the relationships he makes during his journey to the apex! For riches and bi- ahem, for career and love!He wields a demonic sword from Hell, he dons armor shining with Heaven's light. His boots stride across the sky as his helmet devours the souls of his enemies. On his left side sits the Goddess of Death. On the other, the Angel of Beauty.From the land of ice and death, a generation of Asura Kings rises, their roars reverberating throughout the world.Tremble in fear, noobs!
8 8156 - In Serial1353 Chapters
Refining the Mountains and Rivers
A young man's life changes when he stumbles upon a mysterious item. Qin Yu had never been a lucky person. Weak of body, bullied by his peers, and with only his friend as his family, he struggles day-by-day to live. But everything changes when he stumbles upon a little blue lamp. An immortal and demonic cultivating adventure.
8 3344 - In Serial2455 Chapters
Mortal Cultivation Biography
A poor and ordinary boy from a village joins a minor sect in Jiang Hu and becomes an Unofficial Disciple by chance. How will Han Li, a commoner by birth, establish a foothold for himself in in his sect? With his mediocre aptitude, he must successfully traverse the treacherous path of cultivation and avoid the notice of those who may do him harm. This is a story of an ordinary mortal who, against all odds, clashes with devilish demons and ancient celestials in order to find his own path towards immortality.
8 1050 - In Serial1503 Chapters
Dragon Prince Yuan
Destiny stolen at birth, the prince of the once mighty Great Zhou Empire, Zhou Yuan, has been plagued all his life by a fatal poison, forced to suffer powerlessly until one day when fate draws him into a mysterious domain where he meets a beautiful girl in green, a bizarre dog-like creature and an unfathomable old man in black.Join Zhou Yuan as he is thrust into the whirlpool of destiny while he seeks the pinnacle of cultivation.
8 1057 - In Serial677 Chapters
Ranker's Return
In the early days of the virtual reality game, Arena, meleegod was the strongest ranked player! He deleted his character and suddenly left. In order to restore his bankrupt family, he returned to Arena!"Do you want to create a character?"
8 1715 - In Serial1525 Chapters
Monarch of Evernight
Qianye rose from hardship but was felled by betrayal. From then, one man, one gun; he tread the path between Evernight and Daybreak and became a legend. Even if Evernight was destined to be his fate, he still intends to become the ruler who dictates.
8 22861

