《ƘADDARAR RAYUWA》K page 101
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 101
Kwana biyunda Sawwama tayi wajan mahaifiyarta ba karamar nutsuwa ta samu ba domin taji dadi sosai dik wata damuwarta takau, dadin dadawa ga yaranta da suke kara debe mata kewa."
Yareema kam yana gidan Hajiya amma gabaki daya hankalinsa yanaga Sawwama azamansu ba hira sukeyi ba ba kuma sun wani shaku bane amma kewarta yakeyi sosai Allah-Allah yakeyi kwana biyun sucika yadauki matarsa suyi tafiyarsu,
Itakuwa Sawwama nata wajan ba hakan bane domin tafi sakewa wajan mahaifanta kwana biyu dake hankalinta yana kwance har wata yar cika tayi,
Shikuwa tunda yakaita bai sake komawa ba amma gabaki daya hankalinsa yana can yasan bata sakewa da zarar ta ganshi takebi dik ta takura kanta hakan yasa yabata sarari nadan kwana biyun ko zata samu nutsuwa amma hankalinsa gabaki daya yana gareta,
Ana washe gari zasu tafi gabaki daya hankalinta yatashi Mama ta lurada hakan tazauna tayita mata nasiha amma dukda haka tana cikin damuwa gashi Sassafe zasu tafi dan zamanda tayida Yaranta na kwana biyu sai takeji wannan karon kamar bazata iya tafiya tabarsu ba ga Muhammad ma wajanta yake domin dashi tataho daga gidan Hajiya."
Bayan tayi Sallar asubahi bata koma bacci ba domin tasan da sassafe zasu tafi kamar yanda yafada mata kafin yakawota Aikuwa Sassafe sai gashi yazo Allah yaso tagama shirinta tun kafin lokacin Baba ma dake yasanda tafiyar sai baiyi gaggawar ficewa kasuwa dawuri ba,
Yana tsaye a kofar gidan bai san yanda zaiyi ya shiga ba domin shi baima da waya saida yazo nan yasiya kuma baida Number dinta Aysha ta matsa zata biyoshi yaki zuwa da ita daya sani dayazzo da ita tashiga ta sanarda zuwannasu yana tsaye mai adaidaita ya iso ya tsaya yana kallo yadaga waya yayi kira bada jimawa ba sai gashi yara sun fito daga gidan sanye da kayan makaranta ajikinsu suka nufi wajan keke napep din, dasauri ya nufi wajan yaran Hindatu tana kallonsa tasaki fara'a domin taganesh mijin yaya Sawwama ne dan ranar daya yakawo Sawwaman sun gaisa tasan cewa shine mijinnata kafin ya karaso itama tafara nufar wajannasa tagaisheshi ya amsa cikin sakin fiska batareeda yayi magana ba tace "kazo mushiga ciki tayiwa mai keke napep magana sannan tajuya tafara tafiya zuwa cikin gidan babu musu yabita abaya tayi masa iso har cikin falon Sannan tashiga a sanarwa Sawwama ta zuwannasa sannann tafito tasameshi zauna tace "Yaya Sawwaman na zuwa, yayi mata godiya ta fice domin ana jiranta,
Sawwama bata dauki lokaci ba ta fito koda ace Hindatu bata sanarda ita yana falo ba jikinta yabata domin daga shigowarsa kamshin turarensa yayi mata maraba,
Mayafi tayafa tashigo falon da sallama ta zauna can gefe dashi idanuwansa yana kanta ita kuma bata yarda sun hada idoba,
Gaidashi tayi ya amsa yana mai sakin murmushi, muryarta cike take da sanyi barinma idan tana tare dashi ya lura tafiyin sanyin gani yakeyi kamar wacce take tsoransa dar-dar takeyi idan tana kusadashi,
Advertisement
Shiru ya biyo bayan gaisuwar tasu a falon suna zaune ahaka na tsawon lokaci karan AC dake falon kawai akeji,
Hameeda ce tafara shigowa falon sai Hamdan yabiyo baya Hannunsa rikeda muhammad,
Yaran su dukansu suka nufeta ta zaunar dasu gefenta ta zabga tagumi kawai tana kallonsu jimamin tafiyarta tabarsu takeyi hakan yasa tahanasu Hameeda tafiya makaranta Yareema ne yayiwa yaran magana suka tafi wajansa banda Hameedah dake jikin mahaifiyarta, Muhammad kawai yasani matsayin danta amma wadannan ma alamu ya nuna masa yaranta ne domin suna mugun kamada ita,
Mikewa tayi ganin yaran sun sake a wajansa ta nufi wajansu Baba a falo ta samesu ta sanar dasu zuwannasa sannan tajuya,
Tare mama da Baba suka shigo yana ganinsu yakoma kasa ya zauna babu yanda basuyi yakoma ya zauna kan kujera ba amma haka yaki zama,
Cike dajin nauyinsu ya gaidasu suka amsa sannan
Baba yayi musu yan nasihohi hakama Mama,
Baba yadubi yadubi Sawwama yace "saiki tashi kutafi koh rana tanayi, Allah ya kiyaye hanya,
Nan danan idanuwanta suka ciko da hawaye dakyar ta iya maidasu tatashi tadauko jakarta zallan Muhammad suka dauka nan Hameeda ta kankameta ta fashe da kuka danta fahimci uwar tafiya zatayi ananne itama takasa tsaida hawayen nata,
Mama tace "ji shahanci wajan Hafsatu ko menene abun kukan?"
Baba shi kansa yaji babu dadi ganin Sawwama tana hawaye daan yasanta ba komai ke daga mata hankali harta nuna ba,
Shi kansa Yareema tabashi tausayi hakan yasa yadubi baba kansa yana Kasa yace "Baba idanda Hali zamu tafi da yaran dukansu,
Baba ya girgiza kai yace "Babu hali domin sai annemi izinin mahaifinsu abari tukunna daga baya duk yanda ake ciki zan sanar daku,
Ni Mama takarbi Hameeda tanata tsala kuka Sawwaa tafice ko Sallama bata tsaya sunyi ba domin idanta tsaya itama kukanne mai karfi zata saka,
Godiya yareema yayi musu sannan yafito dauke da Muhammad a hannunsa,
Ajikin motan ya sameta tana tsaye ta kifa kanta daga can ya bude mata motar tana jin anbude ta shiga ta zauna shima ya shiga yaso yararrasheta amma ganin baiga fuska ba saiya hakura yaja motar Muhammad yana kan cinyarsa,
Ahaka suka isa har zuwa gidan Hajiya kai tsaye part dinta yawuce yayi parking motar saida ta tsaya ta dai-daita nutsuwarta kafn tafito,
Shima yafito yarufa mata baya amma bawani rata bane tsakaninsu domin daga nesa idan ka hanga zaki iya cewa tarema suke,
Hajiya na zaune a falo tagama shirya musu duk wani abunda zasu bukata a tafiyarsu harda Ma'aikaciya guda daya wacce kusan koda yaushe da ita Hajiya take tafiya duk yanda zataje,
Daga nesa ta hangesu saita saki murmushi babu wanda zaice Yareema bashine mahaifin Muhammad ba saboda irin kamarda sukeyi tanadan gaba dasu kadan shikuma muhammad ya lafe kafadarsa kamar wanda yake bacci,
Karasawa tayi wajan Hajiya ta gaidata Hajiya ta amsa tana fadin kun kusa kuyi latti domin sha daya jirginku zai tashi yanzu nake shirin kiranku,
Yareema ya karaso yana fadin gamu mun iso yanzu in sha Allahu zamu tafi babu bata lokaci, yaso su tafi da muhammad kozai dauke musu kewa amma shima Hajiya tace sai daga baya, ransu bai soba amma babu yanda suka iya,
Advertisement
Alokacin aka fara fita da kayayyakinsu aka shigar motarda zata kaisu airport kafin 10:00 sun fice agidan sun nufi airport di."
_____________
Sadam yafito ma suna tsaye a wajan yana jira yaga daddy yadaga waya yakira anzo anshiga dasu sai yaga yatsaya shima sai ya tsaya yana jiran abunda daddyn zaiyi,
kasancewar ranar Baba bai samu yafita kasuwa dawuri ba sai wannan lokacin yasanya ya riskesu a tsaye suna neman wanda zaiyi musu iso, da fara'a Baba ya karasa wajansu sukayi musabaha,
Sadam yasha matukar mamaki dan daga dady har Najeeb babu wanda ya fada masa su Sawwama sun canja gida,
Baba yace "Ashe kuna tafe bismillilah mushiga mana sadam kansa yana kasa domin nauyin Baba yakeji Baba kuwa yasake kamar komai bai faruba,
Suna shiga palour Baba ya kwalama mama yakira Tashigo hannunta daukeda Hameeda wacce har lokacin kuka takeyi,
Yace "Ummi kawo musu ruwa mahaifinsu hameedane sukazo,
Sadam kuwa bin yarinyar Yayi da kallo ta girma sosai tayi wayo,
Dady yace "rikici take tabawa kenan? Naganta a hannu sai jan zuciya takeyi,
Baba yace " rikicin kenan wai mahaifiyarta tatafi shine take kuka,
Jin an ambaci Sawwama saida gaban Sadam yafadi Dady yace "Oh Allah sarki,
Mama ta dauko ruwan da abun sha ta kawo babu yanda batayi Hameeda tasauka su gaisa ba amma taki,
Saida tatafi baba yajuya suka gaisa Sadam jiki a sanyaye ya gaidashi ya amsa sannan ya hada da bashi hakuri,
Baba yayi murmushi sannan yace" Babu komai Sadam wannan kaddarace da Allahya rubutata kuma saita faru sannan bayan haka kai masoyin Mama nace inaji a abunda yafaru kai kafita jin zafi haka Allah ya rubuta,
Dady yace "hakane shiyasa yanzu mukazoda kokon bararmu ataimaka tadawo dakinta su raini yaransu gabaki daya su taso a hannunsu,
Mun dakata ne saboda zafin mutiwa bai gama barin jikinta ba, idan Allah yasa da rabon komawarsu sai kaga an koma kuma anzauna,
Baba yayi shiru kamar mai nazarin wani abun suma duka sukayi shiru suna kallonsa,
Sadam jiki na rawa yace "Baba nayi maka alkawari in sha Allahi bazan sake bari wani abun ya sameta ba dauketa ma zanyi mubar kasar tayi zamanta acan,
Baba ya nisa yace "Ba wannan bane matsalar baban Yan biyu Mamana ta rigada tayi aure,
Dumm sadam yaji kamar anbuga masa guduma har wani dushi-dushi yake kallo,
Baba yaci gaba da fadin "kanin mijinta mai rasuwa da aura da mahaifin shi yaron da mahaifiyar marigayi ciki daya suka fito,
Wani muradadden lamarine wannda Allah kadai yabarwa kansa sani,
Da kunzo dawuri toda zaku samesuma dan basu dade da tafiya ba,
Sadam yakasa magana dady dakyar yabude baki yace" Allah yabasu zaman lafiya, Baba ya amsa da amin
Dakin yadauki shiru sai dady yayi karfin halin cewa Idan babu damuwa munaso rikon yan biyu yadawo hannun mahaifinsu,
Baba yayi shiru sannan yace "toh dama yanzu muka gama magana dashi mijinnata akan yanaso yaran su dawo hannunsa toh nace bamuda wannan ikon saina sameku munyi magana dama ko baku zoba nima zan je can din,
Dady yayi shiru sannan yace "nima zanso ace yaran sun girma gaban mahaifiyarsu toh amma wani lamarin ya gifta dama tun farko na sanar daku har lokacinda mahaifinsu zai bukaci yaransa zan barsu wajanku,
Ita Sawwama ta iya yiwuwa zata haifi goma bayan su amma shi bahaka bane,
Baba ya kalleshi da rashin fahimta,
Dady yacigaba da magana Haihuwa awajan Sadam sai wani ikon Allah domin bazamu cire rai da rahamar ubangiji ba,
Dady ya zauna ya fayyacewa Baba yanda lamarin yafaru har yanda akayi rabuwarsu izuwa abunda likita ya fadi,
Sai yanzu baba yasan ainihin dalilin rabuwar dakuma dalilin dayasa Sadam bai dawo maida Sawwama ba ya tausayawa masa kwarai da gaske,
Baba ya jajanta lamarin sosai sannan yabashi hakuri yace masa in sha Allahu zai dawo masa dasu dakansa kafin yakoma amma yanzu yakara masa sati guda akai,
Jiki a sanyaye suka tafi Baba ma suka barshi da sanyin jiki,
Bai iya fita kasuwa ba bayan fitarsu Mama tashigo ya sanarda ita jijjiga kai tayi tace "kaga muguwar mata abunda ta jawowa danta koh?
Tana ganin muta kuntatawa ashe a kanta ta kuntatawa,
Allah ya kyauta Baba ya amsa da amin tafiya kasuwarda baiyiba kenan."
—————
Mummy duk yanda taki jinin Sawwama saida ta tausayawa Sadam,
Abida kam har tsalle tayi da labarin ya risketa, Hafsa itama taji dadi amma sadam yabata tausayi, jin cewa Sadam zai kwaso mata yaran tayi murna sosai dan dama abunda takeso kenan,
Tunda sukazo kasar Cikin matan Sadam babu wanda ta taka zuwa gaida mummy ita Hafsa tsoro takeji jin labarin mummy shiyasa ta yanke shawara bazata jeba, Abida kuma fushi takeyi da ita, danko mahaifin Abida ya yanke alaka da mummy,
Sai itace tataka taje gidan tasamu Abida a falo tana kallo tunda tace mata sannu ko kallon yanda take bata sake yiba daga baya kuma tatashi tabarta zaune,
Mummy bakin ciki ya na cita aciki, ga Hafsa kanma ko idonta bata ganiba, itakanma batasan wainarda ake toyawaba dan bacci takeyi,
Har mummy tagaji tatafi,
Takira Sadam ta shaida masa tabbas baiji dadin abunda yafaru ba amma sanin halin mummy ya sanya bai tankaba saboda yasan zata iya fada masa abunda ba shine ba ya tambayi matan su fada masa wani abin daban,
Yanaso yagyara alakarsa tsakaninsa da mahaifiyarsa bayason wani abunda zata sake yi da zai sake nuna rashin kirkinta kiri-kiri shiyasa ko abu tafada bayabin diddigi,
Gashi cikin matan babu wacce tayi masa complain shiyasa shima bai tankasu ba,
Yana sane babu wacce taje ta gaidata yasann tsakaninsu da Abida a halin yanzu Hafsa kuma baisan yanda Mummy zata karbeta ba, shiyasa bai kaitaba."
Toh Alhamdulillah mungama exam in sha Allahu bazamu tsayaba sai mun gamashi gabaki daya,
Ina matukar jin dadin yanda baku gajiya dabin labarinann dukda yanayin yanda yake zuwa baku daina nuna masa kauna da Bibiyarsa ba jzkllhu khairan nagode matuka🥰🥰
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alab
Advertisement
- In Serial45 Chapters
This Strange New Life
Seems like I got a new chance. Better not fuck it up then, since I really want to see what it feels to have a family. Power is pretty lame alone. Best used to build things and protect people. Did a lot of building 'till now, lots of research stuff and all. Now, let's protect the people that I love and that loves me back. An enjoyable life with my loved ones. Whatever the cost. Mufufu~~ What can I do, my siblings are so cute~~ maybe I'll try having children at some point~? --- PLEASE READ THE DESCRIPTION ^p^ ---- This is an extremely slow reincarnation story, with heavy usage of dialogues and diminutive descriptions. Chapter are posted whenever I feel like it, because I won't burn myself down like I did before. Chapters will often be around 2k words. The first arc, Life in Valince, will be at least 50 chapters deep, and the main character won't get to her 1 year anniversary over the span of this arc. As I said, it's a slow, character interaction, dialogue-heavy story. Lots of feeling, slice-of-life etc, with some dramatic events that shape the rest of the story ^^ AND PLEASE, STOP PESTERING ME ABOUT JAPANESE. this story contain a very limited amount of japanese words, used in context for a reason and that are part of the mystery of the worldAnd the bad guys use german (not because nazi buit because german is badass)And there’s also french. Please be open-minded. I’m not a delusional weeb and this kind of thing, and it would be very appreciated if people could be more polite.If you don't like it, I don't force you to read it, but a lot of people seems to like this novel nonetheless, so maybe you should give it a shot. ---- Lux's here! Yeah I know I should work on ToL and ToF but I had another idea, then another one. So here it is. Story talk about a war vet that reincarnate and can finally know what it is to have a family. I like engineering, creating things and all, so I'll try putting production scene in this. Like all my stories, it's about love, be it with family, friends or lovers. I like my coffee with so much love sugar that half the planet would get diabetes. You're warned. Also, the MC is quite OP, but I keep a progression curb and she still has things to learn, which she will eagerly do. After all, curiosity is one of her main drives, with a thirst for love and utter hate of loss, be it losing a battle or losing someone she loves. Ha, nearly forgot. CONTENT WARNINGS AREN'T FOR SHOW. Sex, of course. I'll try to explore sexuality as a male, a female, and some other PoV that can't be categorised like that, not exactly. Also, beware the yuri/yaoi. I don't limit myself to straight couples. Gore. A lot. Blood everywhere, guts spilling and all. I don't do censure. The Mc cut a wolf in half? you get the details of what is inside it. Traumatising content. I dunno. No NTR, no heartbreaking drama. However, some of you may dislike the way I handle bodies and flesh. Got some feedback about body horror on my previous works, but everyone as a different border separating transhumanism and body horror. Mine is pretty high. How high? Go read The Other Labyrthin to have an example. To put it in simple term, I've no problem at all to describe alien bodies, change in human bodies, interactions between differents strange species etc. Expect a lot of tentacle, bio-incubator, spawning pool à la zerg. Profanity. Well, I think you fucking got it in the very first sentence of this synopsis, ain't right? ---- THIS IS A WIP (work in progress)! Earlier chapters may get retconned or completely changed, structure of the story isn't set in stone, all the usual stuff. ANY HELP IS WELCOMED. Want to throw me your idea? Shoot! Spotted an error in the text? Comment! Seen a plothole bigger than the impact zone of a nuke? I'll gladly hear you out and try to fix the problem (somehow ;-;) --- Cover: John Martin - The Plains of Heaven (c. 1851) ---- Official Editor: TheZouave (starting from ch25 onward) ---- List of thanks: Necrotyr (English) Asviloka (English) Damokles (Review) David Talon (Review) JHA (English) Helbom (English) Slee202 (Common Coherence) NEEDS_MORE_DAKA (First First) Srayan (English) Koooomakimi (Dialogue Flow) Emagstar (English) Apocryphal (Review) ToasterForker (Review) Ellen Taylor (Review) Zak (English) PrimalShadow (English) Elliot Flanders (HUGE THANKS for the re-write of the poem "Tale of Ashen Night" Go check their work, it's good ^^) Lance Wheeler (Huge thanks for the English edit on each chapter ^^) (If you think you should be here because you helped me, feel free to ask, pointing the reason, like the comment you gave that could have helped me ^^)
8 198 - In Serial7 Chapters
Age of Blackstone - The Spawn of Apophis
When an elven princess is kidnapped, Blackstone finds himself aligning a mission of rescue with a bloody pursuit of vengeance. Can the stoic armored adventurer save the young royal from a horrid fate at the scaled clutches of the Spawn of Apophis?
8 237 - In Serial15 Chapters
Her and His unlucky adventure
A Short Storyby Ransuko Eliah Reins finds herself in yet another trouble. What scares her so much exactly? Who or what is that figure in the distance? Find out for yourself.
8 170 - In Serial75 Chapters
LACUNA ✰ BNHA
❝I'M ALWAYS TIRED, BUT NEVER OF YOU.❞ [various x reader] a lazy girl with a few missing brain cells is on the path to becoming a hero, but not without snatching some wigs and snatching some hearts. -former/current ranks-#1 IN #BNHA#1 IN #MYHEROACADEMIA#1 IN #BOKUNOHEROACADEMIA#1 IN BAKUGOXREADER#1 IN #BNHAVARIOUSXREADER#1 IN #BNHAXREADER✰PLAGIARISM IS PUNISHABLE✰COVER ART: @nemupan [tumblr]✰LOWERCASE INTENDED
8 137 - In Serial26 Chapters
Nothing Is The Same (6th book in Winchester Girl)
It's been half a year since Mary went to hell with Lucifer, Michael, and Adam. Now she's back and doesn't remember anything from Hell, but things are different. From Kara hiding ice powers, to Sam not having a soul. Mary sees nothing is the same.
8 127 - In Serial6 Chapters
Lore Olympus OCs
Lore Olympus belongs to Rachel Smythe.I own no one in this other than my OCs.
8 122

