《ƘADDARAR RAYUWA》K page 98
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 98
Ana shirin kiran magrib taji motsinsa kamar kotsinsa amma kuma data matsa kusa dashi sai taga kamar bashine yayi motsinba,
toilet tanufa danta dauro alwala sai tajira akira Sallah,
ta dauro alwala tafito Ganin mutum a zaune yayi mugun razanarda ita dasuari taja da baya ta dafe kirjinta,
Ajiyar zuciya ta sauke bayan takarewa yareema dake zaune kallo ta isa wajan fuskarta dauke da fara'a ta zauna ta sanya hannu ta tallafi kumatunsa ido ya tsura mata kamar maison gano wani abun takasa gane wane irin kallo yake mata, kamar wanda yakeyi mata kallon rashin sani, kallo mai cikeda tuhuma,
Cire hannunta tayi daga fuskarsa ganin yanda yake dubanta,
Ina Umma? Taji ya tambaya
Ba irin wannan muryar tasanshi dashiba dan haka jikinta har rawa yakeyi tamike tafice bata samesu a palour ba domin dukansu sun shiga sallar magriba sai juyawa tayi tanufi ciki yanda yake mata nune dashin dakin Umma a kofa ta tsaya tayi Sallama Umma wacce fitowarta daga alwala kenan ta amsa jin muyar Sawwama ya sanya tafito dasauri cikin sanyin murya tace Umma yafarka yana nemanki,
Umma tace "yana nemana? Yaya akayi harya nemeni?
Sawwama tace "haka naji yace ina kike, Umma tace "toh muje tashige gaba Sawwama na biyeda ita abaya,
Tana shiga dakin ta ganshi zaune tadan karawa tafiyarya sauri harta isa bakin gadon ta zauna, shi take kallo kamar yanda shima ita yake kallo, murmushi ya samar mata irin murmushin data dade bata ganiba murmushin yake yinsa a duk lokacinda suka zauna tare da ita suna hira kota sanya masa albarka a wannan lokacin sai yayi Irin wannan murmushi dayayi yanzu,
Umma ta shafo fuskarsa da tafin hannunta tace "Yareema? Kana jina? Kana fahimtar me nake cewa?
Ka ganeni kuwa? nice Ummanka,
Murmushin yayi yace "Ummana cikin wadannan tambayoyin wanne daya kikeso na amsa,
Sunkuyarda kai tayi ta sanya hannunta tana buga saitin zuciyarta a hankali a hankali yayiyin shikuma ya rike daya hannun da matse hannun da karfi sannan tadago ta kalleshi tana kokarin danne kukan dayakesp yaci karfinta iska ya furzar sannan ya jata jikinsa yana buga bayanta a hankali a hakandai saida taci karfin kukan dan bata barshi ya fitowa sakeshi tayi sannan ta mamaye fuskarta da murmushi mai kayatarwa wanda ta dauki lokaci batayi irinsa ba,
A fili take furta Alhamdulillhi, Alhamdulillhi Alhamdulillhi, dukkan yabo da godiya ya tabbata agareka y Allah, ya Allah kaine maji rokon bayinsa yau Allah yasa ma dawomin da Yareema, yareeman dana sami Allah na gode maka tafada hawaye na gangarowa akan kumatunta,
Yareema yasa hannu ya share mata hawayenta dake kwaranya akan kumatunta,
Iska ya sake furzarwa kamar wanda bayaso yayi magana sai kuma ya daure yace "Ummana koda bansan abunda yafaru ba kuma banida tabbacin ko wani abun yafaru amma nasan komai ba lafiya ba akwai wani abun daya yafaru dani naji canjawar yanayi sosai ajikina,
jikina yabani hakan, ganin wannan yarinyar adakina dakuma yanayinki ya sake tabbatarmun da abunda nake tunani."
Umma tace "Yareema yanzu ba lokacin wannan zancen bane amma ita wannan yarinyar daka ganta itadin matarka ce,
Sawwama tun datsu ta zuba musu ido kawai tana kallonsu ganin yadago ya dubeta sai tayi kasada kanta,
Yadade yana nazari akanta kafinnan ya juyarda kansa wajan Umma yace "ki sanar dani abunda yafaru wanda har nayi aure banida masaniya akan hakan,
Batareda tabashi amsa ta mike tace "ina zuwa ficewa tayi mintuna kadan suna zaune itadashi sai kallonta yakeyi yanataso tadago su hada idanuwa sanin yana kallonta ya sanya bata dago ta dubeshi ba ahaka Umma tadawo ta samesu ta zauna yanda tatashi tace jira mai martaba yana hanya na tura a isar masada sako zaka ganshi nan bada dadewa ba,
Advertisement
Jijjiga kai kawai yayi yanaso yasan abunda yafaru dashi amma yasan Umma koda zata bashi amsa toh bayanzu ba tunda har ya tanbaya sau biyu bata bayarba sai dai yajira da kanta taji zata bada din saita amsashi,
Lokuta kalilan Su Ummi suka shigo itada Ruma, Ruma tana shigowa yakira sunanta tanajin haka ta daka tsalle ya sake ihu,
Ummi tace "ke shasha meye hakan kuma,
Jijjiga Umma takeyi tana ihu tana fadin Umma yaya yareema yakira sunana, dariya Umma tayi tace Yayanki yasamu lafiya Ruma,
30minute Sawwama tamike ta dauki sallaya tabar wajanda suke taje van gefe tana Sallah sai lokacin Unma ta tuna itama batayi sallar ba fitowarta daga alwala kenan taji sallamar Sawwama,
Mikewa itama tayi tace barinayi Sallah yanzu zan dawo,
Yareema yace "Wace Sallah akayi?
Umma tace har ina kiran isha'i amma ko magrin dinma mu bamuyiba,
Jikinsa yayi sanyi tabbas yasan wani gagarunin al'amarine yafaru dashi, mikewa yayi yace shina zaiyi Sallahn yashiga ya dauro alwala ya fito bashi waje Sawwama tayo yayi magrib ya mike zai fita Ummi tace "Yareema ina zakaje?
Masallaci yabata takaicacciyar amsa,
Ummi ta mike tana fadin kayi hakuri ka rufa mana asiri dawo kayi Sallarka agida idan aka samo bakin zaren ka fita ka jira nasan mai martaba ma yanzu zai karaso,
Zama yayi ransa yana masa daci wai yau shine da Sallah a cikin gida kamar wata mace,
Komawa kan sallayar yayi ya gabatarda sallar isha'i,
Bayan idarda Sallar isha'i mai martaba ya iso su duka suka saika kasa mai martaba yazauna akan kujera idanuwansa yana kan yareema dake zaune akan Sallaya, bai nemi karin bayani ba sukuma babu wacce ta sanar dashi domin sunsan shirunsa akwai abunda yakeso yagano ne,
bayan ya Sallame ya juyo ya dubi mai martaba dake kallonsa ya sakar masa murmushi,
Sawwama dake kallonsa aranta tana tunanin shikuma dabi'arsa kenan?
Kafin yayi magana sai yafara tura aiken murmushi,
Khaalifaah mai martaba yafadi,
Na'am yareema ya amsa,
Alhamdulillhi mai martaba yafadi sannan ya kalleshi yace "sauki yasamu khaliifa toh Allah ya kara maka lafiya ya kareka su duka suka amsa da amin bai dade a wajanba ya mike yana fadin bari naje zuwa gobe saina dawo ka kula sosai da ibada yau da dare kar ayi bacci a zauna ayita fadawa Allah bukatu ayita kiyamul laili ha matarka nan saita taimaka maka nima nawa wajan ba baccin zanyiba mahaifyarka ma nasan haka zuwa Safiyya sai musan abunyi, Yareema ya mike ya rakashi suna zuwa falonsa ya tsaidashi daga nan shikuma yacigaba da tafiya,
Su Umma ma dare suka raba anan sannan suka tafi suka barshi dagashi sai Sawwama,
Daganan aka hau zaman kurame sai da dare yayi nisa sannan ya mike ya shiga ya dauro alwala yafara Sallah kamar yanda mai martaba ya umarceshi ganin haka ya saya itama tatashi ta yi alwala tazo ta jonashi
Akan sallayar bacci ya dauketa saida rana tafara fitowa sannan tafarajin wani sautin kira'an alqur'ani mai dadin gaske a hankali ta bude idanuwanta ta saukesu akanta ganin gari yayi haske ya sanya ta mike dasauri tashige bandakinta dauro alwala yana zaune akan Sallaya yana karatu jin motsinta ya sanya ya sauka gefen carfet itakuma tahau kan Sallayar tayi sallah,
Tana zaune a wajan cikin sanyayyar muryarta tace "ina kwana?
Saida yakai karshen ayarda yake karantawa sannan ya rufe kur'anin ya dago ya dubeta."
*Continuation*
Fuskarsa daukeda murmushi cikeda kulawa ya amsa gaisuwarta sai kuma suka zauna shiru babu wnada yasake cewa komai lokaci-lokaci yake dagowa yana kallonta iyakuma tunda tayi kasada kanta bata sake dagowa ba,
Bani ruwa taji yafadi kamar wacce take jira tamike dasauri tafita ta dauko ruwan hadeda cup ta zuba ruwan sannan ta mika masa ya amsa yayi bismillah hadeda kafa kansa saida ya shanye sannan ya sauke yaja nunfashi sannan yace "nagode,
Advertisement
Murmushi kawai tayi sukaci gaba da zaman kurame har Umma tayi sallama tashigo ta samesu a haka,
Fiskarta cikeda walwala rabonta da tayi walwala irin haka tun kafin ya kwanta rashin lafiya,
Murmushi ya sakar mata yana fadin Ummana Barka da safiya ina kwana?
Ta zauna can gefensu sannan ta amsa da fadin lafiya kalau yaya kwanan jikinnaka?
Alhamdulillhi yabata amsa,
Sawwama ma ta gaidata ta amsa cikeda fara'a tana tambayarta mai jiki saida tadan saci kallonsa wanda shidinma ita yake kallo sannan tace "jiki Alhamdulillhi,
Umma tace " toh Ma sha Allahu mungodewa Allah gabaki dayanmu Allah ya biyaki da gidan Aljanna wannan sadaukarwa da kikayi ubangiji kadai zaiyi miki sakayya, mu kam anamau wajan sai dai mu biyaki da kyautatawa amma ba kwatankwacin yanda kikayi mana ba,
Shi bai fahimci zancen ba sai dai ya dauki hint,
Suna zaune ta mike tadubi Umma tace barina hada breakfast,
Umma tace "toh tafice tayi kitchen kamar dai yau haka taga matar jiya ta gaidata itama bata amsaba kuma bata maida mata gaisuwarba kuma koda ta gaisheta ba amsawa zatayi ba,
sawwama zata fara aiki tajiyo muryar matar tana fadin" Rabki shi dade ki fadamin abubda kikeso saina dafa na aiko miki,
Batareda ta kalletaba tacigaba da aikinta sannan kuma tabata takaicecciyar amsa,
"Babu komai
Saida tagama sannan ta kauce daga wajan,
Ta deba kai tsaye tayi shahshinsu,
Ayanda tabarsu haka ta samesu suna taba yar hira sai Ummi da Ruma da suka karu adakin,
A gefensa ta ajiye da plate din sannan ta zuba ta mika masa ya karba hadeda yimata godiya,
Zata sake zubawa Umma tace har indai mune mun rigada munyi karin kumallo ki zauna kawai ku karya,
Plate din ya tura mata gabanta sai takasa gane abunda yake nufi agabansu Umman zasuci abinci tare?
Daukan wani spoon din yayi ya sanya a cikin abincin ta zaune ta dauki spoon din jujjuyawa takeyi kawai amma takasa kaiwa bakinta shikam ko ajikinsa cin abincinsa kawai yakeyi, ganin abunda takeyi yasanya ya tsaida nasa cin abincin cikeda kulawa yace "meyafru? Naga bakyacin abincin, sai lokacin hankalin Umma yakai kansu murmushi kawai tayi danta gane Sawwama nauyi takeji,
Umma tace "nauyi takeji shiyasa bataci kizuba naki daban karki zauna da yunwa,
Hannunsa ya daga cikin abincin yace "no taci wannan zan zuba wani,
Dasauri ta girgiza kanta tace "No zanci basaika zuba wani ba,
A hankali tafara tsakuran abincin takai bakinta kadan taci sannan tace "ta koshi,
Shikam dai bai koshi ba dan zama yayi yaci abincin sosai kuma yayi masa dadi,
Dama ta lura tun bayida lafiya baya wasada cikinsa yana farkawa abunda yake fara tambaya shine abinci,
Sai wajan Sha daya kafin mai martaba yashigo bayan sun gaidashi duka yadubi Yareema yace Khaliifa yaya karfin jikinnaka?
Murmushi yayi saannan yace "Alhamdulillhi,
Toh ma sha Allah haka akeso Allah yasake warware mana al'amura, su duka suka amsa da Amin,
Saida yayi gyaran murya gabaki dayansu suka dawoda hankalinsu gareshi sannan yace "Nasan bakada masaniya akan abunda ya sameka da halinda ka kasance aciki,
Wata jarabawace ta sauka maka tsawon lokaci wanda muka kasa gane kan lamarin domin lamarine mai wuyar sha'ani, tsawon lokaci ana abu daya bazamuce dai babu cigaba ba angodewa Allah domin wani lokaci al'amuran saimu gansu da sauki wani lokacin kuma abubuwa sukici suki cinyewa,
Kwanakin baya Allah yakawo mana Wannan baiwar Allah matarka Hafsatu ya nuna Sawwama tundaga zuwanta sai Allah yafara buda mana al'amura muka fara ganin canji sai sauki yazo,
Mungodewa Allah daya kawo mana ita cikin rayuwarka, bansaniba amma dole akwai wata alaka mai karfi a tsakaninku ko ince tsakanin abunda ya sameka dakuma ita domin itace makarin Al'amarin,
Mai martaba dalla-dalla yafi abubuwanda sukayita faruwa ya sanarwa Yareema, har zuwan Sawwama,
Yareema saida yayi kwallah jin tsawon shekaru yana wannan, jikinsa yabashi kam yana cijin bacewar hankali na wani lokavi amma hai dauka abun yayi misa hakaba,
Kuma gashi wai matar dan uwansa itace tadawo matarsa ta dalilinta Allah yakawo masa saukin jinyarda yayi shekara da shekaru yana fama da ita,
Muryar mai martaba ta katseshi da fadin ko akwai wani abunda kasani gameda wannan lamari?
Nisawa yayi sannan yace "Abba haka yareema yake cewa mai martaba Abba kamar yanda yayansa suke fada masa,
Munyi waya da Hajiya na shaida mata zanje can dama kamar lokacin danake zuwa ne,
Nadauki hanyar garin kafinna isa nafara rasa hankalina zuwa isana garin narasa hankalina gabaki daya amma zan iya fadan abunda na aikata tabbas a wannan lokacin bana cikin hayyacina amma nasan abubuwanda yafaru,
Bansaniba nasamu kaina cikin matsananciyar sha'awa dana kasa iya controlling kaina kamar mahaukaci haka na kasance yayibda tukinma ya gagareni, tsayawa yayi kamar wanda bayason cigaba da magana har saida mai martaba ya tanka yace "akwai wani abunda yafaru bayan haka kokuma ka mance bazaka iya tunawa ba?
Girgiza kai yayi yace "koda nace bana cikin hankalina amma zan iya tuna abunda na aikata,
Na fito daga mota domin nakasa tukun narasa abunda yake damuna wani irin nunfashi kawai nakeyi, yayinda hadari ya hado sosai a lokacin walkiya da tsawa kawai akeyi,
Gabban jikina gabaki daya sun mutu, jinakeyi idan ban sauke sha'awata ba alokacin mutuwa zanyi amma dukda hakan na gwammaci na mutu,
Ana haka saiga wata yarinya kamar wacce aka jefota,
Izuwa yanzu Sawwama gabanta faduwa kawai yakeyi domin tafara fahimtar yanda zancenaa ya dosa,
Abba nayiwa wannan yarinya fyade ya karashe maganar murya na rawa, sannan yacigaba da fadin koda bana hayyacina amma bazan iya mantawa da mummunan aikin danayi ba,
Yakasa karasa maganar yayinda zuciyarsa take zafi nunfashi kawai yake fitarwa,
Dakin ya dauki shiru na wani lokaci sautin numfashinsa kawai ake iya jiyowa,
Ya dauki mintuna kafin yace "a wajan nabarta nakamo hanyar gida domin bazan iya zuwa wajan Hajiyaba, naji kawai nadawo gida bayan nadawo kuma daga nan bazan iya sake tuna abunda yafaru ba,
Mai martaba jiki a sanyaye yace "kafin kafita kaci wani abunne?
Batareda bata lokaci ba yace naci abinci, agida ko awaje? Ya gida yabada amsa, jijjiga kai yayi yace aje ajira masa matarda take daga abinci a shashin Umma,
Rumace tafita domin kirannata,
Umma hawaye kawai takeyi idanuwanta har kala suka canja, tarasa me yareema yake fada, tarasa me zuciyarta takejina gabaki daya har wani daci takeyi mata,
Yareema yacigaba da fadin,
Abba na aikata laifi domin banida dalili ko uzurinda zai wanke abunda na aikata bansan wani hali nabar yarinyar ba tamutu tana raye, Abba zanje na nemeta duk yanda take kuma zan karbi kowanne irin hukunci ne,
Sawwama takasa rike kukanta domin yaci karfinta kuka kawai tasake mai karfi su duka suka juya suna kallonta babu wanda ya iya rarrashinta amma mai martaba ya zuba mata idanuwa yanaso ya karanci wani abu,
Umma tayi karfin hali ta dafata tace "kiyi hakuri da abunda mijinki ya aikata nasan zakiji zafi amma inada yakinin bahaka Yareema yakeba dole akwai wani abun akasa,
Mai martaba ya fitarda numfashi mai nauyi ya gyra zama sannan yace idanna kintata dai-dai ba abunda ya sakata kuka ba kenan tana kukane saboda itace yarinyar da yareema yayiwa fyade sai yanzu nagano alakarta dashi wanda su kansu basusanda hakanba,
Saurin daga hannuwa daga cikinta Umma tayi danta razana sosai,
Itakuma Sawwama kukannata ya karu su dukansu kallonta sukeyi ko zata musanta abunda mai martaba yafada amma a'a kukanne kawai takeyinsa,
Mai martaba yace "ki tabbatarmun Hafsatu kece wannan yarinya ko bake bace?
Har yanzu bata bada amsaba kuka kawai takeyi wanda hakan ya tabbatar musuda zarginsu,
Tsugunnawa Yareema yayi akan kafafunsa ya riko hannunta yakasa furta komai yayinda itakuma kukan kawai takeyi ko kokarin kwace hannun batayiba,
Ana haka ruma tashigo tace mai abincin tazo mai martaba yabada Umarni ashigo da ita sanna yace Ruma tafita,
ganinsu ahaka yayi matukar tsoratata dama ita tunda taga wata tafara shugowa tana dafa abinci jikinta yabata akwai matsala,
Da zube guiwowinta akasa tana kwasar gaisuwa babu wanda ya iya amsa mata,
Mai martaba kai tsaye yace "Abincinda Yareema yaci ranarda ya kwanta rashin lafiya me kika zuba aciki?
Jikinta yadauki rawa alamun rashin gaskiya ya bayyana a tattare da ita tafara kame-kame,
Amma gwarjinin mai martaba ya sanya takasa canko karyarda zatayi ma,
Shekara nawa kikayi kina zuba abu a abincinsa? Amsa daya kuma gaskiya nakeso idan baki bani yanda ya kamata ba hukuncinki zaiyi tsanani domin babu azzalumi kamar mutumin daka yarda daci ya zalinceka,
Shekara tara tafada sannan ta saka kuka tana fadin ayi mata rai, bazata sakeba,
Murmushi kawai mai martaba yayi sannan yayi umarni atafi da ita,
Bayan sun fice yace "ayanda na fahimci lamarin asirine abune mai yiwuwa sunyi tsawon shekaru sunayi bai kamashi ba shine suka yanke shawarar farawa da abincinsa, ta iya yiwuwa abun sha'awa suka bata dafarko tazuba masa hadeda asirinsu domin sai alokacin bayida tsarki zasu samu cin gabaka akansa, saboda sunga baida mata bare su kintaci lokacin zai tara da ita kuma yareema kamilalle ne bare asamu hanyarda zata sanya yasamu najasa ajikinsa,
Dole wannan hanyar zasubi kafin su samu su aikata abunda sukeso shine sukabi hanyarda zasu sanyashi yayi mummunan aiki,
Ina kintatar abunda yafarune bance lallai hakan bane yafaru amma babu yanda za'ayi wannan lamari ya kaucewa haka, kuma koda bamu saniba alamu ya nuna mana ita yarinyar daya tarada ita itace suka hada makarin ciwon da ita, atunaninsu baza'a taba samunta ba,
Wani abunda basu saniba shine da Allah yaga dama toh da zai bashi lafiya koda bada makarin ciwonba,
Amma sai Allah yagwada musu iyakarsu ya gwada cewa duk nisan wannan makari zaizo ya sameshi har yanda yake, yabarsune sunyi ikonsu an wani lokaci Ahalin yanzu kuma zai gwada musu nasa ikon wanda ya zarce duk wani ikon mai iko,
Babu wani mai iko sai wanda Allah yabashi damar yayi hakan."
Yadubi Sawwama yace "Hafsatu ba ina fadin wannan abun bane dan yazama dalilin da zaisa na wanke yareema a wajanki kona kareshi ba,
Tabbas Yayi miki laifi mummuna ya aikata miki ba dai-dai ba ya kuntatawa rayuwarki,
Amma a matsayina na mahaifi gareshi domin ayanzu nine mahaifisna ina baki hakuri kiyi hakuri bawai ina baki hakuri bane dan ki yafe masa ba A'a wannan shi zai nema, ina baki hakurine saboda abunda aka miki mu dukanmu mun cancanci mubaki muneni gafararki, nasan a wannan lokaci rayuwarki ta kasance cikin kunci ta dalilin abunda ya aikata miki amma shi bawa ako'ina yake baya wuce kaddararsa ke dashi haka KADDARAR RAYUWAR ku tazo."
Ba editing fa dan ina school ma na karasa wannan shafin dan na jiya baiyi yawa ba kuma banaso pages din su haura yanda nake tunani."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial1363 Chapters
VRMMO: The Unrivaled
Lu Chen used to be a ranker of the most popular VRMMO game, Spirit of Grief. After a car accident turned his dreams into dust, his disability left him incapable of escaping the pit of mediocrity he was thrown into. Helpless and defeated, his story ended.Two years later, the Eternal Moon Corporation launched a new VRMMO called "Heavenblessed", and Lu Chen stumbled into another terrible accident that left him in a complicated situation far beyond his ability to handle. That won't stop him from rising to the top, however. Not again.Come witness the rise of the sword-wielding zombie and the relationships he makes during his journey to the apex! For riches and bi- ahem, for career and love!He wields a demonic sword from Hell, he dons armor shining with Heaven's light. His boots stride across the sky as his helmet devours the souls of his enemies. On his left side sits the Goddess of Death. On the other, the Angel of Beauty.From the land of ice and death, a generation of Asura Kings rises, their roars reverberating throughout the world.Tremble in fear, noobs!
8 8156 - In Serial1353 Chapters
Refining the Mountains and Rivers
A young man's life changes when he stumbles upon a mysterious item. Qin Yu had never been a lucky person. Weak of body, bullied by his peers, and with only his friend as his family, he struggles day-by-day to live. But everything changes when he stumbles upon a little blue lamp. An immortal and demonic cultivating adventure.
8 3345 - In Serial2455 Chapters
Mortal Cultivation Biography
A poor and ordinary boy from a village joins a minor sect in Jiang Hu and becomes an Unofficial Disciple by chance. How will Han Li, a commoner by birth, establish a foothold for himself in in his sect? With his mediocre aptitude, he must successfully traverse the treacherous path of cultivation and avoid the notice of those who may do him harm. This is a story of an ordinary mortal who, against all odds, clashes with devilish demons and ancient celestials in order to find his own path towards immortality.
8 1051 - In Serial1503 Chapters
Dragon Prince Yuan
Destiny stolen at birth, the prince of the once mighty Great Zhou Empire, Zhou Yuan, has been plagued all his life by a fatal poison, forced to suffer powerlessly until one day when fate draws him into a mysterious domain where he meets a beautiful girl in green, a bizarre dog-like creature and an unfathomable old man in black.Join Zhou Yuan as he is thrust into the whirlpool of destiny while he seeks the pinnacle of cultivation.
8 1058 - In Serial677 Chapters
Ranker's Return
In the early days of the virtual reality game, Arena, meleegod was the strongest ranked player! He deleted his character and suddenly left. In order to restore his bankrupt family, he returned to Arena!"Do you want to create a character?"
8 1715 - In Serial1525 Chapters
Monarch of Evernight
Qianye rose from hardship but was felled by betrayal. From then, one man, one gun; he tread the path between Evernight and Daybreak and became a legend. Even if Evernight was destined to be his fate, he still intends to become the ruler who dictates.
8 22865

