《ƘADDARAR RAYUWA》K page 97
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 97
Tun acikin toilet din bayan ta taimaka masa ya tsarkake jikinsa ta fuskanci sauyin yanayi a tattare dashi,
Wani irin kallo yake mata wanda takasa gane na menene sai lumshe ido yakeyi kamar wanda yakejin bacci,
Numfashinsa yana fita da sauri da sauri ganin haka ya sanya ya janyoshi kawai suka fice daga bandakin,
Suna fitowa daga toilet din sai taga jikinsa gabaki daya ya mace kamar wanda ciwon yake shirin tashi gabaki daya ya canja yanayi ya isa gadon batareda yasake kallon yanda takeba ya kwanta a gefensa na dama, dasauri ta bude wadrope din taciro sabuwar jallabiya da sabon boxer kamar yanda tagani suke kowanne cikin ledarsa gabaki daya wadrope din abjnda yake cike kenan dam kuma dukansu sabi fill, taga dai wanda yana cirewa fita dasu akeyi, ahaka dai ta taimaka masa ya sanya amma a yanda ta sanshi a kwana biyunnan zata iya cewa yanzu kamar wanda aka sauyashi kamar wani daban bashiba,
Da sauri yakoma yasake kwanciya a gefensa na dama ta dauko ruwan addu'a tabashi ya sha ya sake komawa ya kwanta ha lumshe idanuwansa,
ganin haka ya sanya itama ta kwanta gefensa shikuwa yana kwanciya kamar wanda baccin yake jira ya daukeshi, ba ita tafarka ba sai asubahi a yanda ya kwanta ko kwakkwaran motsi baiyiba saida ta mirginashi ta canja masa wajan kwanciya sannan ta tashi tashiga toilet tafito daureda alwala taga yakoma kamar yanda ya kwanta a barin damarsa,
tabarshi a hakan ta gabatarda Sallah dake anrigada anshiga ta dade zaune akan Sallaya bayan addu'oi tayita karatun alqur'ani saida taji bacci na neman daukarta a zaune sannan tatashi ta dauko ruwan addu'an da mai martaba ya aiko ta tasheshi amma kamar baya jinta ko matsawa baiyiba nunfashinsa dai yana sauka a hankali ganin haka ya sanya kawai ya shafe masa jikinsa dashi sannan ta kwanta a gefen gadon,
yau kam bata kai kamar jiyaba dawuri tatashi tashiga tayi wanka sannan tafito ta canja kayanta tafita bataga kowa a falonsu Umma ba dan haka tawuce izuwa kitchen wanann matar ta jiya tagani wacce Umma tace mata itace wacce takeyin komai na kitchen din,
Da mamaki take kallon Sawwama domin batasan abunda yakawota kitchen dinba batama taba kallonta ba ko batasan bakowa ke shiga kitchen dinbane?
Sawwama ta kalli matar taga ita take kallo ta juyarda kanta gefe batareda ta kalletaba ta bude baki zata gaidata sai taji matar ita tafara gaisheta nauyin amsawa taji sai kawai ta maida mata da gaisuwar itama matar bata amsaba dan tasan cewa batada damar amsa wannan gaisuwa ko ba'a fada mataba tasan cewa itadin watace shigar jikinta zai nuna hakan,
Jin bata amsaba ya sanya Sawwama bata sake tankawaba tajuya tafara abunda ya kawota saboda taji Umma jiya tace ayimasa faten dankali da kifi sanna asaka alayyahu akai hakan ya tabbatar mata da yanaso ne,
Advertisement
Saida ta tanadi duk wani abunda takeda bukata sannan tafara aikin itadai matar kallonta kawai takeyi bataso ta hanata kuma taje tayi laifi tunda batasan ko wacece ba,
Sawwama bata matsa a wajanba saida tagama komai ya jure sannan tabar kitchen din,
Iya wanda zauyi amfani dashi ta deba da ajiye sauran akan dining dinsu Umma,
Har lokacin yana bacci hakan yasa ta debi nata taci sannan ta rufe masa nasa ta zauna takira mama Sun dade suna hira samnan ta kira haleema saida suka dauki tsawon awa suna waya bayan sun gama takira hajiya suka gaisa,
Baba kam tasan yana kasuwa hakan yasa batama kirashi ba,
Har wajan shabiyu bai tashiba tana zaune tana danna waya taji Sallamar Umma amsa Sallanar tayi sannan tace tashigo ta karaso ciki ta gaidata ta amsa tana tambayarta mai jiki tace "Alhamdulillhi
Umma ta zauna tana kallonsa da mamakin irin kwanciyar dayayi,
kwana biyu har wani dan cika yayi,
Saida tanemi waje ta zauna sannna ta maida hankalinta kan Sawwama wacce tayi kasada kanta tace "ya tashi kuwa? Ko har yanzu bai farkaba?
Sawwama tace "tun jiya dai daya kwanta da dare bai tashiba na tasheshi yasha wannan ruwan da aka aiko amma har yanzu bai tashiba,
Umma ta jijjiga kai tace toh kwanciyar fa tun jiya haka ya kwanta?
Sawwama ta dago ta dubeta dan bata gane yanayin tambayarba,
Umma data fahimci haka sai tace "ina nufin a hannun damansa ya kwanta?
Eh a hannun ta kwanta koda na mirginashi sake dawowa yayi,
Umma da nisa zuciya cikeda damuwa danma yanzu damuwartata ta ragu cikin karyayyiyar murya tace "kuma naga jiya baiyi baccinba Allah dai yasa bawani sabon abun bane kuma,
Sawwama ta amsa da amin,
Suna zaune ahaka Ummi tashigo ta samesu sa'i-sa'i suke taba hira amma ita bata sanya musu baki saboda akwai rashin sabo,
Saida akayi azahar sannan su Umma suka fita don gabatarda Sallah itakuma aciki tashige toilet tayi alwala ta gabatarda nata sallan ta zauna akan sallaya tanata addu'oi,
Umma ce tasake dawowa ta sanarda ita mai martaba zai shigo dama da hijabinta jikinta sauya wajan zama kawai tayi, Umma ce tayi masa iso yashigo da sallama Sawwama ta amsa murya kasa-kasa yashigo kai tsaye yayi kan Yareema saida yayi masa addu'oi yaduba jikinnsa sannan ya juyo ya zauna a sopa dake dakin Sawwama ta gaidashi kanta yana kasa ya amsa yana tambayarta jikin yareema tace "dasauki,
Sun dauki tsawon lokaci ahaka mai martaba yakara mata yan nasihu sannan yace "aduk lokacinda kuke zaune kada bakinki yagaji da tofa masa addu'oi kuna zaune kiyita fadin
"*HASBIYALLHU LA'ILAHA ILLAH HUWA ALAIHI TAWALKALTU AHUWA RABBUL ARSHIL AZEEM*
*A'UZU BIKALIMATILLAHI TAMMAH MIN KULLI SHAIDANIN WAHAMMA WANIN KULLI AININ LAMMA*
Ki lazimci karanta *A'UZU BIKALIMATILLAHI TAMMAT MIN SHARRIN MA KHALAQA*
*LA'ILAHA ILLAH ANTA SUBUHANAKA INNI KUNTU NIMAL THALIMIN*
In sha Allahu Allah zai dubemu sannan sai yaye mana damuwarmu,
Sawwama kanta yana kasa tace "in sha Allahu yacigaba da bata addu'oi na tsari dana kariya,
Ya dan dade a wajan Sannan yayi sallama yatafi,
Advertisement
Yana tafiya Sawwama tahau yin addu'oin tana shafa masa dama tunda can ita bakinta bamai zama shiru bane idan tana zaune toh akwai abunda takeyi acikin ranta kamarsu *Istigfari, Su Hasbunallhu wani'imal wakeel, La haula wala kuwwata illah billah*
Har akayi la'asar Yareema yana wannan baccin yanzu kuma abun yafara bata tsoro dan bata tana kallon baccin nasa hakaba,
Tayita kokari ko zai tashi amma ko motsi bayayi idan taga haka zai takoma ta zauna tacigaba dayi masa addu'a."
———————————-
Cikin week din Sadam ya shirya dawowa kasarsa akaro nafarko bayan wasu shekaru,
Hafsa ganin dagaske tafiya zasuyi su barta ya sanya itama tace binsu kawai zataje,
Abida kuwa cike takeda zumidi dan rabonta da gida itama tun tahowarsu da Sadam banda aurensa da Hafsa ma da wayartama kwacewa yayi,
Kowaccensu na ciki na ciken kawai amma ita Abida dake bata iya boye abunda yake cikinta sai ta fiddoshi haka yasa bata iya boye damuwarta dake ciki na dawoda Sawwama dayace zaiyiba tasan irin sonda yake yiwa Sawwama bata nanma bata isheshi kallona bare kuma ace yanzu tadawo,
Tanada yakini cewa idan yanzu Sawwama tadawo toh zaiyi mata soyayya ne fiyeda yanda yayi mata abaya zai riketa gam kuma ba mummy ba koma wacecce bazai yarda tasake rabashi da itaba,
Ita dai wannan lamari sam baiyi mata ba tafiso ace yakaro wasu matan da ya maido Sawwama,
Sun gama shiri tsaff lokaci suke jira suyi airport domin tashin yamma zasuyi,
Yana zaune adakin Abida amma hankalinsa yana can gida gani yakeyi kamar lokaci bazaizoba yakoma yaje aiwatarda abunda yakaishi, yasake duba agogo akaro na ba dadi mtsww yaja tsaki ya furzar da wata iska yana karkada kafa,
Abida da fitowarta daga wanka kenan ta tsaya tana kallonsa cikeda takaici,
Kasa karasawa gaban mirror tayi ta nufoshi saida tayi magana kafin yasan da isowarta, yana kallonta daureda towel yace "me kikeyi anan da bazakije ki shirya ba?karki bata mana lokaci, tabe baki tayi tace "saura awa biyu harda rabi kafin jirginmu yatashi idanma kayi hakuri lokaci zaizo amma cikin kwanakinnan duk wanda yaganka sai yaga wani zumudinda kake ciki ita kanta waccar uwar kwainanayen bata isheka kallo ba,
Zaunawa tayi gefensa ta canja murya tace "Sadam dan Allah kafasa zance dawoda Sawwaman gara ga auro wash matan daban,
Wai na mamajo kika maida nine abida? Kullum zancenki na auro wasu matan daban ance miki ra'ayin kainane tara mata kema sanin kan,,,, daga masa hannu tayi cikeda takaici tace kafada yafi sai arba'in dan haka banada bukatar ji, kai kanka kasan idanma yanzu kana kokarin kamanta adalci a tsakaninmu tana zuwa zaka daina ka canja gabaki daya saboda kasmau abunda kakeso dama abunda kake fada shine katara mata ata dalilin rashinta, kaga kuwa kdan tazo mundawo hoto,
Sadam yayi shiru yakasa bata amsa dan yasan a wannan karon kam dole saiya danni kansa ayanda yake jin daukin Sawwama idakuma ba hakaba toh za'ayi babu dadi tsakanin matansa,
Mikewa tayi ta isa mirror ta shafa mai sannan ta shirya ko kallonsa batayiba yaja trolley dinta tayi gaba,
Bude dakin hafsa tana zauna akan bed ta alamu tagama shiryawa jiransu kawai takeyi, yana kallonta itama ya fahimci tana cikin damuwa,
Sake murfin kofar yayi ya karasa ciki ya zauna gefe ta cikin sigar lallashi yace "amaryata ne yake damunki haka?
Hmmm nikam aina kusa sauka a wannan matsayin tunda ga wata amaryar zakayi, yayi murmushi dan yasan kishi ke dawainiya da ita yace "Au na manta ashefa yanzu itace zata kasnace amarya toh nacanja uwargida, tabe baki tayi tatashi cikeda damuwa zatayi waje hannunsa ya sanya yakamo hannuta ahankali ya jawota tadawo baya akan cinyarsa ya daurata, ya sanya bakinsa a dai-dai wuyanta ta lumshe idanuwa, a hankali yafara magana "Hafsa karkiyi kishi da Sawwamaty idan kikayinin haka bazanji dadi ba,
Sawwama tanada kwayun hali zakiji dadin zama da ita, nisawa tayi cikeda damuwa tace "amma fa sonda kake mata yayi yawa kaduba kaga kwanakinan kowa yaganka sai yasan kana cikin nishadi,
Kimin afuwa sannan kimin uzuri akan Sawwama nafara sanin menen so kaddara tazo ta rabani da iga bawai dan nadaina sonta ba na hakura da ita yanzu Allah yabani damarda zan maidata dole nayi farin ciki,
Sawwama nada kyawun hali sosai itace macenda nasan menene so akanta mun dauki tsawon lokaci muna tare da zancen aure amma haka Allah ya rubuta abida zan fara aura koda na sanarda ita bata kullaceniba bare ta kullaci abida,
Kinga batada hayaniya sam tanada halaye masu kyau zakiji dadin zamada ita har indai baki bata mastsalaba inada tabbacin bazaki samu matsala a wajanta ba,
Jikinta yayi sanyi sosai har kunya taji toh meyema abun kishi da Sawwama bayan wajan mijinta zata dawo?
Amma ai dole tayi kishi tunda tana sonsa kuma tanada masaniya akan sonda yake yiwa Sawwama,
Nisawa tayi ta turo baki tace "amma fa karka manya kayimin alakawarin zaka bani twins na rikesu,
Sadam yayi shiru kamar mai nazarin wani abun sannan yabude baki yace "eh toh nayi alkawari zan bakisu amma yanzu tunda mahaufiyarsu zata dawo saina shawarceta tukunna dukda nasan bazama tahana ba sai abaki hamdan saboda saboda zakubi jituwa dashi dan yana bawa mahaifiyarsa ciwon kai saboda ita batason hauaniya, Hakeeda kuma kamar yanda na fada miki batada maraba da mahaifiyarta hattada kamanninsu da halayensu,
Uhmm kawai tace sannan ta mike tana fadin "muje time, a falo sumu Abida tacika tayi famm danma yayi mata dokaciya akan kada takara shigo musu daki idan suna ciki komai zatayi tajira har sai sun fito, kuma ranta yana bace sam batajin yin laben shiyasa bata labe danjin abunda ya zaunarda suba, suna fitowa fuuu tafice tayi waje."
taxi suka kira ta daukesu har zuwa airport, suna isa bata sukabi duk wani matakin daya kamata bada dadewaba jirginsi ya daga."
Saukar cikin dare sukayi Amma dukda haka Sadam bai yarda sun sauka gidan Mummy ba gidansa suka sauka ahakan aka tattare abunda za'a tattare suka kwanta har Allah-Allah yakeyi hari ya waye yaje yaga Sawwama da yaransa."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial44 Chapters
Tempero King
Kade, a young man with a troubled past and abandonment issues, returns home after four years of service in the military with reservations about his future. However, Everything is upended when foreign races descend on earth, introducing humans to cultivation. Suddenly, the mythical abilities written about in stories are no longer works of fiction, but instead are the new reality. The foreign races-- Congregated into factions -- didn't come to Earth out of benevolence, however. They had a goal, which becomes apparent when Portals begin appearing across the globe. On the other side of these portals, sits a vast new world with resources galore. The faction's couldn't visit this new world themselves, so they requested that humans enter these portals to explore and conquer this new world in their sted as their champions, and in return, they offered these humans knowledge and resources for their cultivation. Just like that, a life changing opportunity presented itself to Kade and the rest of humanity. Is it truly as simple as it seems, or is there something dangerous under the surface? What makes this new world different from the countless others in the universe? If it sounds too good to be true, then it likely is. But those are questions for another day. For now, our protagonist will grasp this opportunity with both hands and claw his way to the top while facing the obstacles in his path as he goes! -Cover Art- The cover art is composed of two parts. 1: The hand was drawn by Robert Marzullo, a professional artist who has illustrated a few comic books and had some 3D animation on television. He is currently illustrating his own comic book 'Blackstone Eternal'. He has graciously allowed me the opportunity to use his artwork for the cover of my original webnovel. -Link to the art used: https://www.deviantart.com/robertmarzullo/art/Hand-Studies-By-RAM-605188489 -Robert Marzullo's Deviant Art page where you can find his other social media: https://www.deviantart.com/robertmarzullo/about 2: The magic circle used was created by ChocasaJulie on Deviant Art. She follows her passion for art despite those that would consider it a waste of time. She has even made some of her art Free Use in support of other artists. Her only ask is that she is credited, and that is more than fair!
8 185 - In Serial225 Chapters
To Midnight
*CURRENTLY ON A SHORT HIATUS* Without warning, a giant, black obelisk appears in the center of a local park in Maryland. No one knows where it came from, how it got there, or even what it’s made of. The great obelisk foretells that a great evil, known as “The One” is about to descend upon the world. In addition, it warns the world that superpowered people called Resonators are also going to appear around the world, and among them is “The Chosen” who must locate the other obelisks to learn the truth of the world. After finding a shard that claims that he is The Chosen, Vincent Huron sets off and travels around the globe in order to save the world. With the help of his friends, Zander Nenmos and Eliot Zanes, Vincent will discover his destiny, uncover the mystery behind these strange obelisks, and come face to face with the truth behind The One. New chapters every Monday and Friday!
8 166 - In Serial18 Chapters
Kanojo no Jin
Kurasawa shin a highschool student with few male friends and no girlfriend or friend of opposite sex. one day he found a website who provide a cute cat looking like Jin for one year free to overcome loneliness among youth. He ordered thinking it as a joke but after ordering one he really get a cat Jin and from that his life changes completely.
8 73 - In Serial37 Chapters
Living With My Bully
(Original Version, New Version in Progress that I suggest waiting for if you'd like) "I'm sorry for your loss." I hear and look over to see Oliver, "I've been in a similar situation, I may not have lost someone this way, but I definitely did lose someone. My family and I will be here for you and will help you get through this." He says biting his lip. I smile a bit. "Thank you Oliver, hearing you say that really means a lot to me." I tell him. I can barely see Oliver look back through my tear-filled eyes but then I feel two arms wrap around me. ~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~Meet Iris Mitchell, she's known as the nerd in school with her best friend, Kayla. Iris is also extremely stubborn and doesn't know when to shut her mouth. She also likes to watch Netflix 25/8 with Kayla. But in school, Iris is bullied by Addison Meyer and the one and only, Oliver Sullivan. Meet Oliver Sullivan, he's known as the bad boy in school but also the bully of many students in the school, and Iris is one of them. All the girls want him, except Iris and Kayla, they fantasize about famous actors and fictional characters. Oliver is mostly found hanging out with his friends Adam, Lucas, and Ross. But outside of school, Oliver is an extremely different person and no one knows. Well until Iris moves in with him, of course. Iris' father, Christopher Mitchell, dies in a fire, at his job, saving people on the top floors. With no mother or relatives to go live with, Iris needs to move in with a family, and her dad knew the Sullivan family pretty well. What's going to happen when Iris moves in with her bully? Read to find out!7-9-19//#18 in bully8-3-20//#4 in teenfiction
8 149 - In Serial7 Chapters
Pictures of You
Tiva One-Shots//Each update is a separate Tiva quick fic. They'll probably mostly be based on OTP story prompts.
8 175 - In Serial5 Chapters
New generation
In which it all starts when Zeus has a dream.Based off The Lightning thief movie.
8 110

