《ƘADDARAR RAYUWA》K page 96
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 96
Da zallan wayo da dabara Hafsa tayita gasa abida bata futo fili ta nuna mata cewa tana takun saka da itaba rashin wayonta tayita amfani dashi wajan ganin ta gasata dai-dai gwargwado,
A lokacinda Hafsa ta fahimci cewa Abida tanayi musu labe aduk lokacinda suka kebe saida canja salonta da zaran sun shiga daki idan wani abun yana faruwa takan saka kunne taji takun isowar Abida daga wannan lokacin saita canja sauti taringa fitarda Sauti mai kara wanda duk mai sauraronta zai dauka tsabar tana cikin yanayine na jindadi yakw sanyata haka Harsho Alhaji hotiho (Sadam)😅 a tunaninsa saboda yanda yake bida itane ya sanya take wannan abubuwaam baisan zallan makirci bane,
Itakma Abida duk lokacinda ta jiyo kwana bakin ciki takeyi amma kamar wawiya takasa daina zuwa kullum tana hanyar zuwa labewa a bakin kofarsu."
Zaune suke su dukansu a falo babu mai kula wata kamar wanda aka sanyasu zaman dole Sadam yashigo ya samesu dawowarsa daga aiki kenan Hafsa tayi masa sannu da zuwa itakuwa Abida ta tabe baki ta kauda kanta gefe yarigada yasaba hakan yasa baibi takantaba,
Ita duk lokacinda yake dakin Hafsa ko kallo cikekke baya samu wajanta kuma itama haka takeso idan yana dakinta daga ko kallo ya hadasu da Hafsan yayinda itakuma Hafsa idanma a dakin Abidan yake sai tayita jansa da hira kala-kala,
Abida kuwa ba iya hakuro zatayi ba haka zatayita bala'i saita manna mata hauka tashige daki kokuma tazaune ta kunna TV kota dauki wayarta,
Zama yayi a kujerarda Hafsa take zaune Abida taja dogon tsaki su duka suka juya suka kalleta sai kuma suka maida Hankalinsu ga junansu murmushi Hafsa tayi masa tace "Barina dauko maka ruwa dannasan ka gaji idanka huta saimu shiga kayi wanka,
Ba ishin ruwan yakejiba amma ya amsa da godiya saboda yasan tayine danta kyautata masa,
Mikewa tayo tashiga kitchen ta dauko robar ruwa tareda glass cup sai Taceccen ginger da lemon tsami ansanya masa sugar da tamarine yar kadan ta fito dashi hannunta a tray da ruwan dakuma lemon data hada tazuba a jug ta iso gabansa ta dire tray din a hankali ta zuba lemon tabashi ta kafa kansa saida ya shanye tass kafin ya daga kai "inkaro maka ta tambaya girgiza kai yayi zata zuba ruwanma ya dakatarda ita yace nagode Allah yayi miki akbarka zuwa jimawa zansha ruwan,
Ta maida ta ajiye sannan ta zaune Aboda datake jinsu tasake jaan tsaki tace kibibin banza ayide mungani idan tusa zata hura wuta,
Sadam yayi murmushi sannan ta amshe yace "aita rigada ta hura wuta ta ruru kece kika kasa gane hakan tunda ke kin rigada kin kwarawa taki wutar ruwan sanyi banaji zata kama a halin yanzu,
Abida da maganarsa taci mata rai danta gane yanda ya dosa ta kauda kanta bata sake cewa komaiba,
Sadam ya sha mur sannan yace "matso kusa inaso muyi magana daku Kamar bazata matsoba sai kuma tatashi ta canja kujera tadawo takusa da wacce suke zaune,
Saida yayi shri na wani lokaci kafin yayi gyaran murya yace "inaso kubani hankalinku anan ku saurari abunda nakeso na fada muku danna rigada na yanke shawara abunda nakeso kuyi shine kubi umarnina sannan ku zauna lafiya,
Watannin baya da suka wuce mijin Sawwama wanda ta aura bayan rabuwarmu Allah yayi masa rasuwa,
Ba Abida zallah ba har Hafsa saida gabanta yafadi dan kobai karasa ba sunsan yanda maganarsa tadosa,
Yacigaba da fadin "Allah yayi masa rasuwa tun alokacinda aka sanar dani rasuwarsa naketa tunani amma izuwa yanzu nagama yanke shawarij abunda zanyi,
Advertisement
Zan maida Sawwama asake daura mana aure tadawo dakinta mu rumgumi yaronmu,
Tunda dukanku kun sani Kaddara ce kawai tarabani da ita kuma nasan tajirani ko zan sake maidata amma hakan baiyuwuba saboda halinda nake aciki koda nazo nasamu lafiya naji cewa bazan sake maidata rayuwarda tabari abaya ba,
Ahalin yanzu nagane cewa wannan ba shwarar gaske bace, shawarar gaskiya itace na maidata dakinta mu rungimi yaranmu,
Abida wacce takejin zuciyarta kamar wuta tace "wallhy gara ka kara auro mata biyu kacike hudu daka dauko wannan bala'in,
Sadam yace "ni nagama magana shiyasa tun farkon maganata nace ba shawara nazo nema ba kawai zan sanardakune dan kunada hakki Hafsa kanma tarasa nacewa saida shida kansa yace "Hafsa kinji abunda nace ko kinada abun cewa a wannan?
Shiru tayi kamar bazatayi maganaba sai kuma tace "ni tsorona shine kowa yasan irin sonda kake mata ba lallai bane idan zaka iya adalci a tsakaninmu, kar itakuma tazo tayo amfani da sonda kake mata tayita kuntata mana,
Murmushi Sadam yayi yace "kidaina jin tsoron wannan in sha Allahu zanyi adalci dai-dai gwargwado atsakaninku,
Sannan ita Sawwama bahaka takeba ita wannan data zauna da ita tasan halinta sai dai idan bazata fadi gaskiya ba amma koda sau daya bata taba yin wani abun danta kuntata mataba,
Abida tace "sonda kake matane ya sanya bazata fadi gaskiya ba ai amma zamanmu da ita wani irin rashin adalcine banganiba wani irin cin zarafine baka minba,
Kallonta kawai yayi ya girgza kai danya tabbata abida bata tsoron Allah,
Ganin lokacin Sallah yayi ya sanya ya mike yana fadin "zuwa next week in sha Allahu zan tafi can kasar idanda wacce take bukatar zuwa a cikinku zata iya shiryawa saita bini atake Abida tace zanbika,
Hafsa itadai batace komaiba ya shige ciki jiki babu kwari ta dauke tray dinda ta ajiye takai kitchen Sannan tabi bayansa."
Sadam yajira dady bayan sun gaisa yace "dady na rigada na yanke shawara zan maida Sawwama wani week din zanzo in sha Allahu, zancen mummy kuma zanzo da ita nan kasar Mummy batana gantaba bare harta samu damar kuntata mata,
Dady yace "hakanma yayi Allah ya tsabarda abunda yafi alkhairi idan kazo sau muje tare daga nan idanma aurenne sai adaurashi a wajan tunda abu bana farko kona biyu bane basai antsaya taron jama'a ba a daura tatare dakinta baki alekum,
Da haka suka karkare hirar sukayi Sallama."
—————-
Dake tasan Yanda idan suna tare yake makalkaleta bata kawo komai aranta ba ta juya tacigaba da baccinta,
Baccinta yayi nisa kamar mafarki-mafarki taji yanayi mata wasu irin abubuwa,
Bata farka ba tacigaba da baccinta jin abun ya yi yawa ya sanya ta tabbatar cewa ba bacci takeyi ba razane tafarka taga yareemane yake mata wannan abubuwan mutumin da ake claiming maras hankali shine ya juye ya rikide yadawo mutum mai cikeda hankali wanda yasan hanyarda zaibi ya sarrafa mace, ganin abunda yakeyi yana nema yayi yawa ne ya sanyata saurin tureshi taraba jikinta da nasa dan atunaninta iyakacin abunda zai tsaya kenan amma sai taga babban abun yake nema gabaki daya,
Kasa bude idanuwansa yayi saboda yanda yakeji gashi ta turesho ta hanashi turenshi datayi yagane cewa batason abunda yake matane, shikuma dukda kasnacewa baimasan abunda yakeyiba baisan dai-dai da rashin hakanba yanda yakeji bazai iya bata mataba bazai tana iya aikata abunda bataso ba,
Komawa gefe yayi ya kudundune a bargo itama ta koma ta kwanta ganin kamar wanda yakoma bacci,
A kankanin lokaci cikeda mamakin yareema Bacci ya dauketa cikin baccinta take jiyo sauti kanar nishe cikeda bacci ta bude idanuwanta taganshi dafeda mararsa daga alamu yana cikin mawuyacin hali dasuari ta matsa ta tallafeshi cikin tausaywa halinda yake ciki tagane dalilin fadawarasa wannan yanayin nan tausayinsa da haushin kanta suka cikata,
Advertisement
Saima takasa gano menen dalilinta na tureshi datsun ko gani takeyi dan bayida cikekken hankali bazata iya hada shimfida dashiba kenan?
Iya tunaninta tagano batada wani dalili daya wuce wannan runtse idanuwanta tayi kawai gashi gabaki daya yadawo wani abun tausayi yashiga wani mawuyacin hali batada wata mafita face ta mika kanta gareshi danya samu ya fice a cikin wannan halinda yake ciki,
Itada kanta tashige jikinsa tadauki hannuwansa ta daurashi a yanda taga datsu hankalinsa yafi karkarata wajan,
Janye hannun yayi cikin wahalalliyar murya yace "nabari tunda bakyaso,
Wani tausayinsa yasake shiga zuciyarta tace inaso kayi ya girgiza kai tace "ni nace kayi inaso saida yatsaya ya dubi fuskarta yaga tabbas tana nufin abunda tafada da saurinsa ya koma yacigaba da abunda yakeyi da zafi-zafi kamar wanda yakejin tsoro tasake hanashi."
Jin sautin saukar numfashinsa ya sanya ta juyo ta tsura masa idanuwa yana baccinsa cikin kwanciyar hankali batasan sadda murmushi ya subuce mataba da sanya hannu ta shafa gashin girarsa daya kwanta luff ya hade gabaki daya,
A'iya tsawon rayuwarta zata iya cewa tunda take bata taba Samun gamsuwa irinta yauba a rayuwar auratayya, gabaki daya yanayin yau na dabanne da samu nutsuwarda bata taba tunanin zata samu makamanciyarta ba, zuciyarta tayi fari tass babu abunda takeji sai dadi da sanyi yana shigarta,
Kallonsa kawai takeyi tana mamakin mutuminda baisan kansaaba ya iya aikata wannan lamari mai girma, mutumin da ake yiwa kallon maras hankali ya iyabi sako da lunki yana sarrafa mace kai kace mai cikekken hankali mai cikekken hankalinma wanda ya karanci wannan fannin kadai zai iya aikata wannan lamari."
Ahaka bacci ya dauketa bata farkaba saida taji kiran asslatu ta mike tashiga bayi tayi wanka ta fito da gabatarda nafilfili ta dade tana addu'a sannan aka shiga sallah tayi raka'antanil fijr tayiwa Yareema addu'a sosai bayan taji anshiga sallah tatashi tayi tata sallar tayi karatun Alqur'ani mai girma sannan tayita azkhar saida gari yafara haske sannan ta koma ta kwanta har bacci yafara daukanta tayi saurin farkawa dan tasan zuwa jimawa Umma zataso tashigo idan tazo taga dakin ahaka kuwa tabbas tasan abunda yafaru bare yareema dake bacci hankalinsa kwance ko kayanma babu jikinsa sai dai kawai yana rufeda bargo,
Idan akazo aka ganshi ahaka kuwa babu wanda zaiyi tunanin ba itace ta nemeshi ba kowa cewa zaiyi itace da nemeshi ko tausayi babu baida cikekken lafiya amma ita bukatarta kawai,
Ita kanta tayi mamakinsa wacce taga abunda idanuwanta kasa yarda tayi cewa yanada wata matsala dam ya rikide ya dawo mata cikekken mutum bare wanda basu ganiba,
Saida ta kimtsa dakin sannan ta tasheshi itada kanta ya taimaka masa yayi wanka sannan tabashi wasu kayan acikin wadrope ta taimaka yasaka sannan suka koma bacci ga mamakinta harda tashi karfe goma amma Umma batamayi da layinba,
Koda tafita falo ma bata samu kowa a nanba sai dai taga abinci akan dining kuma tanada tabbacin nasune dan kulolin sabbine jiya da yareema yace yanajin yun aka budesu aka zubo abincin aciki daukwa tayi takoma ciki ta tasheshi ta zuba masa abincin ta ciyarda shi sannan ta dawo dasu ta ajiye bai dadeba yasake komawa bacci,
Kusan azahar sannan taji shigowar Umma,
Ganin Yareema ya canja kaya ita bata canjaba ya sanya Umma tabada umarni aka kawo mata akwatinanta nan sashin aka juyesu a dakinda suke,
Yareema Bai sake tashiba sai karfe uku na yamma hakanma yunwace ta tasheshi,
Suna zaune afalo Umma da Ummi da runa Sawwama tafito ta sanarwa Umma abunda yareema yakeso Umma tace banyi zaton tashinsa yanzuba gashi ba abunda yakesoba aka dafa dan dama shi yawanci abinci daban ake masa rana dai-dai kune yakecin abinda mukaci,
sai dai bansan ko zaiciba tunda yanajin yunwa amma lafiyarsa kalau baya taba yarda yaci couscous, Sawwama tace "inane kitchen din saina shiga ma dafa masa wani abun?
Umma tayi murmushin najin dadin yanda Sawwamar take nuna kulawa akan yareema tace "ki huta abun zaiyi miki yawa barina saka yanzu adafa masa, wayarda ke kan side table ta dauka wayace ya tafi ta gidanka ta danna lamba kirrr ringi biyu aka dauka a cikin wayar tabada umarni akan ayiwa Yareema faten dankali da kifi sannan asaka alayyahu sosai daga cikin wayar aka amsa da sauri cikin girmamawa sannan ta katse wayar,
40minute yawuce Sawwama taji shiru gashi gabat Yareema shi kadai mikewa tayi tace Umma inane kitchen dinnan na dubata?
Umma tace "laa da kin jirata zatazo yanzu aikin kitchen dinne gabaki daya a wuyanta ya rataya shiyasa wani lokacin ake samun tsaiko amma tunda hankalinki yayi kan yareeman gara ki dubata daga nan saiki wuce shashin naku sanyawa tayi aka nuna mata kitchen din Sawwmaa ma'aikaciyar shashin tana tafiya tana binta abaya saida sukazo dai-fai shiga kitchen din Sawwama tace "zaki iya juyawa ni zan karbo yarinyar ta tsaya da mamaki ganin babu wanda yake taba zuwa kitchen itake karbo abinci da jeresu a dining amma ganin unarnik da aka bata kenan ya sanya taja ta tsaya da baya-baya take tafiya harta fice Sawwama ta sanya kanta kitchen din bata kaiga yin Sallama ba idanuwanta ya hango mata mai girka abincin ta gama girkawa amma tana tsaye tana barbade abincin da magani da sauri taja baya ta koma gabanta yana mummunan faduwa bata taba kallon yanda ake zuba magani a abinci ba sai anan,
Toh ko dama duk abincinsa ana saka masa magani acikene? Idankuwa hakane ai sai dai Umma tasaka da kanta da sam basaso wani yaje wajanda yakema balle maganinsa,
Komawa tayi jiki a sanyeya tanaso takarbi couscous din takai masa amma itama tsoronta takeji kardai itama anzuba wani abun aciki,
Kamar zata wuce kai tsaye shashinsu saita juya tanufi palournsu Umma suna zaune yanda tabarsu tashigo da Sallama su duka suka amsa,
Kanta yana kasa tace "Umma ina neman wata alfarma ce, Umma da fara'a sosai tace "saki jikinki ki fadamin koma menene kijini kamar mahaifiyarki in sha Allahu zan yi miki abunda kike neme dan inada tabbacin kinsan inada iko dashi shiyasa kika nema a wajena,
Sawwama tadanyi twisting lips dinta kamar batason fadin abinda yakawota sai kuma tadaure tace "dama inaso daga yau naringa dagawa yareema abinci da kaina,
Umma tace "toh amma bakya ganin aikin zaiyi miki yawa? Ga kulada yareema gakuma dafa abinci a yanda tsarin nanma yake mai kulada kitchrn dabanne ita waccar matar itace take kukada kitchen din nan sashin samada shekara ashirin iyakacinta kitchen bata shigowa nan muma iyakacinmu nan bamu cikayi da wajanta ba sai mu shekara bamu lekata ba,
Sawwama ta sanyayar da murayarta dama kuma muryartata mai sanyice tace "Umma nafiso na girka masa dakaina hankalina zaifi kwanciya,
Ummine ta amshe maganar da fadin daga yau kiringa dafawa mijinki abinci da kanki babu wanda zai saka hannu tunda hankalinki yafi kwanciya da hakan muma kanmu abunda hankalinki ya kwanta dashi nami zaifi kwanciya dashi,
Sawwama tace "nagode zata juya daya daga cikin ma'aikatan ta shigo hannunta dauketa tray da kwano na tangaram mai kyau sosai adaure akai Umma tace "gashi ma ya iso saiki karba ki kai masa,
Sawwama ta girgiza kai tace "A'a Umma abarshi kawai zan nema masa wani abunda zaici,
Umma dai mamaki ya cikata mai yasa sawwama take acting haka?
Ta kalli matashiyar ma'aikaciyar tace jeki kikai muku kuyi amfani dashi godiya tayi ta juya itama Sawwaman ta juya tayi shashinsu ta sameshi harya koma ya kwanta bacci ta shafe kansa cikeda tausayinsa yau tafara samun hint akan wannan ciwon nasa ganin wannan mata datayi tana barbarda magani a abincinsa,
Tausayinsa mai tsanani ya shiga ranta wai meya tsare musu haka da suke masa wannan mugun abun? Tasan dole bazai wuce akan sarauta bane ake masa wannan abun tsawon lokaci afili ta furta Allah zai saka maka,
Tana juyawa Ummi tadubi Umma tace "tabbas akwai wani abun tattare yarinyar nan,
Kina kallo yanayinta ya canja alokacin taje kitchen din ta dawo ta iya yiwuwa wani abun tagani, bai kamata idan tace miki abu ki zauna kina jayayya ba ke kanki yakamata ki dauki darasi akan fara zuwanta masarautarnan izuwa tafiyarta dakuma dawowarta a matsayin matarsa ki dauki duk wasu lammuransa ki mika mata sannan ki cire shakku aranki yarinyarnan in sha Allahu tazo mana da alkhairai dayawa ke shaidace akan yanzu tabbas nasan wani abun tagano a kitchen din amma mu kyaleta a hankali zamu gane komai tunda kikaji tace zata fara girka abincinsa da kanta hakan yana nufin ta dauko hanyar gyara lamura kenan idan Allah yayi cikin kwannanan sai kiga Yareema Haalifa yasamu lafiya abunda mukayi shekara da shekaru muna bukata sai kiga Allah ya amshi addu'armu, Umma sai taji hankalinta ya kwanta tunda Yareema yafara jinya bata taba tsintar kanta acikin kwanciyar hankali irinna wannan lokacin ba,
Da magrib Mai martaba ya aiko magani da ruwan addu'a abawa Yareema da kanta tayi masa amfani da maganin,
Da dare yayi ko baccinma yau batayiba da dai Yareema yaga sun kwanta sia yafara shafata,
Saita tabarshi ya gama lularda ita wata dubiyar daban sannan wani abun ya fado cikin ranta ta manta shaff yau ba wankan tsarki tayi masa ba kawai wanka tayi masa suka fito mikewa tayi ya tsaya yana kallonta da wata irin fuska a tunaninsa zatayi masa irinna jiyane ta hanashi abunda yafara,
Hannu ta mika masa alamun yataso,
zata taimaka masa yayi wankan tsarki kafin tabarshi ya kusanceta dan yanayinta suka kasance jiya ita kanta tanaso tasake kasancewa a irin wannan yanayin domin yakasa gogewa a kwakwalwarta gabaki daya."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- End192 Chapters
Emperor of Solo Play
Year 2035. The virtual reality game, Warlord, changed the world. An Jaehyun was one of the many who wished to change his life through the game. After dedicating his life to the game, he was met with a betrayal. A betrayal by his comrades. As a result, he lost everything. But a chance was given to him. A chance to redo everything again! “I won’t play with others ever again. Whatever the outcome, I’ll show that I can do it alone.” Others rolled a die to split the spoils of victory. An Jaehyun ate it all by himself. It was the start of An Jaehyun’s solo game life.
8 490 - In Serial221 Chapters
Consuming Earths, Devouring Skies
In the myriad realms, legends rise and fall in the countless eras. Yan Zaizen, a frail youth with an unfortunate history, meets one of these legends. Will this change his common destiny to something greater? The story of a boy that just wants a peacefully lavish life with money, amazing food, and a beautiful woman to love. The story of the heavens that laughs at this.
8 63 - In Serial37 Chapters
The Paths of Power
One start, but many paths to power. To save a people from war, three destinies are created on the path of conflict and death. For adventure, knowledge or chaos, who knows where events and their own nature will take them... Towards new or old forgotten paths? Two similar paths do not necessarily mean the same destination...An unoriginal story.Illustration : Yuri_BEven in my own language I sometimes make grammatical mistakes, for those who have the courage to read what I write in spite of that, sorry. You are warned.
8 106 - In Serial10 Chapters
NoS: The Crypts in the Shadow (Hiatus)
"What does one expect from caves? Normally, that would entail something like bats, guano and insects in narrow passages, ones that needs to be squeeze through? But... That is not what we found on our expedition deeper into the mysterious cave system, the one under that island, which has stumped scientists for decades... No, there is something else in these dark passages. Something not to be trifled with." -Yandré Skai ~ This is a parallel story that connects to the bigger world I created. One that I'm readying to reveal. ;) It is about two groups of modern humans discovering a great secret, but upon discovery is left without a way to get away from the perils that lurk within the giant network of dark caves. They will need to learn to survive the dangerous new world that they have tread into, all with the hope of finding a way above ground, maybe even a way back. But if they could by force of will find a way to reach the top; would what they find, give them peace, or change something vital in them... ~ Main Genre: Fantasy Epic, Contemporary twist Genres of the series: Adventure, Mystery, Survival, Discovery, thriller. The bigger story is Nights of Sambria and the Wish of light
8 198 - In Serial34 Chapters
Kiss of Tragedy
Juliet is the innocent freshman at university. Seth is the mysterious stranger. Too handsome to be real, he barely looks human. Most telling of all, he has three sets of bite marks down his throat. He denies being a vampire, though he openly admits he's nothing but trouble... until that fateful day when he kisses Juliet and her vision opens to show violence, death, a reality she can no longer run from, and a version of herself she didn't know existed.
8 140 - In Serial50 Chapters
Spirit Realm
https://www.wuxiaworld.com/novel/spirit-realmThis novel is not mine nor translated by me. For offline reading purposes only. All credits and acknowledgements goes to the author and the translator(s).Official Synopsis: Thirty thousand years ago, the Heaven Fighting Race who called themselves "Gods" invaded Spirit Realm. Hundreds of races rose up in resistance, but ultimately suffered a crushing defeat. The human race was the first to concede, and the rest of the Hundred Races soon followed in succession.During the subsequent ten thousand years, all of the races were enslaved by the Heaven Fighting Race. They were cruelly treated, and lived beneath the shadow of terror.The Heaven Fighting Race's march of conquest did not stop there. With Spirit Realm as the starting point, they invaded other secret dimensions, and spread war to all corners of existence. After greatly exhausting their combat strength, they were finally defeated by the Hundred Races who took advantage of this opportunity. With no other choice, they fled to the starry skies outside the realm.Thirty thousand years later, in an era where the Heaven Fighting Race has already faded to become ancient legend, an amnesiac youth possessing the Heaven Fighting Race's bloodline is being fostered in an insignificant household. Whilst struggling to live on, he silently awaits the day of the bloodline's awakening.SR Team: alyschu, Craxuan, wyhcwe, Nabuch
8 180

