《ƘADDARAR RAYUWA》K page 94
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 94
Kanta yana kasa tashiga wajan Can gefe tazauna ta gaida mutanen ciki cikin girmamawa mai martaba yace abasu waje dama tun kafin yafada wasu daga ciki sun fara barin falon,
Bayan kowa yabar Falon yadubi Sawwama yace "Hafsa Sawwama ta sake nutsarda kanta a kasa kwarjini da cika idon wannan Dattijon ya hanata dagowa ta kalleshi saida yasake kiran sunanta ta amsa cikin nutsuwa, mai martaba yace "dago ki kalleni magana zamuyi har lokacinma takasa kallon nasa hakan yasa yayi murmushi irinna manya sannan yafara magana,
Nasan ta iya yiwuwa kunyi magana da Yata ta sanar dake batunda nazo matadashi jiya amma inaso na sake jajjada zancena nazo na nemawa jikana aurenki,
Nasan zakiyi mana kallon masu son zuciya mutanennda zakafi son kansu fiyeda kowa abun bahaka yakeba,
Dalilin faruwar wannan lamari bayan zuwanki bayan tafiyarki kuma ciwo yasake dawowa muna saka rai in Allah yayarda za'a samu waraka daga gareki,
Zakiga kamar munason aura miki wani mutum daban, Mai martaba yayi dariya Na manyan mutane sannan yace "Abun bahaka yakeba a zahirin gaskiya bantaba cin karo da wani mutum irin yareema ba A hali da komai ana cewa mutum tara yake bai cika gomaba amma fa inada tabbacin Idan Allah yabawa yareema lafiya kika zauna dashi zakice shi yacika goma,
Idan kika amince da wannan auren Allah yabawa yareema lafiya zaki kasance kullum kina min addu'a saboda hada wannan al'amari danayi,
Yareema mutum ne wanda cikin dubu samunsa ba lallai ba zaki iya tara miliyoyin mutane baki samu daya kamarsa ba, bani kadai na shaida hakanba duniya ya shaida mutanenda suke taredashi sun shaida,
Yareema mutum ne Yareema mutum ne kwarai dagaske Allah ya hadashi da jarabawa daciwo wanda bamusan menene ba,
Amma zuwanki munga canjin Al'amari harmun fara gano bakin zaren Yareema yayi magana radau yanda kowa zai fahimceshi,
Tsawon Awa biyu suka dauka Mai martaba yana bata labarin Yareema da yanda yake tafiyarda rayuwarsa yanda yake mu'amala da mutane tanata mamaki shin dama za'a samu mutum irin haka?
Advertisement
Mai martaba yayi murmushi ganin yanda jikinta yayi sanyi yace "kadan daga cikin halayansa kenan na fada miki saikin zauna dashi zaki tabbatar abunda na fada miki yafi haka, dan inaji ajikina yakusa samun lafiya,
Nisawa kawai tayi batace komaiba amma cikin ranta tana mamaki dama Sarakuna suna sakewa haka suyi magana?
Kodai dan ita yana neman wani abun wajanta ne?
Mai martaba ya daura da fadin ina neman alfarma a wajanki da ki amince da wannan auren in sha Allahu zai zame mana alkahiri gabaki dayanmu, amma yanzu zan baki lokaci kiyi tunani tunda anzo abun a kurarren lokaci kiyi shawara da mahaifanki naso nagansu amma Mahaifin Abubakar (Alhaji) yace "abari sai kin amince tukunna samau mahaifanki nima na yarda da hakan domin abi komai a ka'ida yafi kinada dama da ikon da zakice baki amincewa wannan aurenba amma ina neman alfarmarki akan ki amince in sha Allahu duniya gabaki dayanta sai tayi alfahari da wannan auren,
Sawwama ita dai batace komaiba amma jikinta yayi sanyi,
Bayan yagama ya bukaci Alhaji da Hajiya su shigo ciki suka zauna kasa kamar yanda Sawwama take a kasa, mai martaba yace "mungama magana amma nabata lokaci tayi tunani duk abunda ta yanke saita sameki ya nuna Hajiya ta fada mikk idan yaso maji Allah yasa muji Alkahiri su duka suka amsa da amin banda Sawwama,
Alhaji yace " Mai martaba koni danaji wannan zance nayi farin ciki Allah yasa hakan shine hanyar samun lafiyar Yareema,
Ko Abubakar yana raye Yareema yaga Hafsa yace yanaso Abubakar mai barmasa ne bare yanzu da baya raye da yana raye zaiyi farin ciki da wannan lamari domin yadamu da halinda dan uwansa yake ciki,
Hajiya ita dai batace komaiba har suga gama amasallacin dake cikin gidan sukayi la'asar daga nan Mai martaba kai tsaye aiport kawai yawuce har yaje yadawo basusan abunda yakaishi ba, Hajiya tasake jaddada mata cewa idan bata amince ba tafito kanta tsaye tace bata amince ba dan bataso tayi abunda zuciyarta bata aminta dashiba,
Hajiya tafita a dakin dake dama sun koma dakinta Aysha tashigo ta zauna kan sopa dake cikin dakin jikinta duk yayi sanyi itama Sawwama anata wajan hakanne jikinta yayi sanyi duk tarasa abunyi, ta dubi Sawwama tace "Anty Hafsa kekam yar Sa'a ce dafarko Yaya Abubakar gashi yanzu Ya Yareema,
Advertisement
Gabaki daya salihan mazan kike kwashewa, iska ta furzar tace bazan boye mikiba Anty Hafsa naso Yaya yareema kamar hauka, tun bansan sonsa nakeyiba har nadawo nasan sonsa nakeyi soma mahaukaci wanda hana iya controlling dinsa idan akace zaizo gidannan kamar anyi mini gagarunar kyauta nakeji koda yake zan iya cewa garama ace anyimun kyauta wannan mai saukice ko muryarsa naji zan iya wuni cikin farin ciki,
Na dade inata kissima yanda zan fada masa ina sonsa inataso na tsara yanda zai amince dani domin naga shi nasa wajan bai daukeni da komaiba,
Alokacinda wannna abun yafaru dashi hauka naso nayi,
Har nadebi shekaru bankuala wani saurayiba smamma yanzu gashi nan kamar ba'ayiba sai dai har yanzu ina sonsa,
Sawwama tasamu kanta da tambayar ko meyasa kike sonsa?
Aysha tayi wani murmushi wanda Sawwama bata gane ma'anarsa ba tace kinga halin Yaya Abubakar?
Toh wallhy Yaya Yareema harya fishi kirki dole mace idanta zauna dashi taji sonsa aranta, kamar kwai haka yake treating na mata shi yanayjn hakan domin kyautatawa amma keda yakeyi miki hakan dole zuciyarki ta tsinke har indai bata kashi bace,
Sawwama tace "kina masa irin wannan son meya hanaki auransa?
Aysha tayi murmushi tace Allah baiyiba amma kam naso Ya Yareema,
Kekam yanzu Allah yabaki, sai nakeji damana nine ke,
Sawwama taso tace kizama ni din mana ki aureshi sai dai kawai taki fadi dan kawai tana ganin suna zuga halinsa ne danta aureshi,
Koma ta aureshi yanzu ina halinma yake idanma da akwaishin kenan dan samun mutum mai irin halinda suke zayyano mata da kamar wuya,
Mikewa tayi tace "Anty Hafsa kiyi tunani mai kayu kiyiwa kanki zabinda gaba bazkaizo kina dana saniba,
Tana gama fadin haka tayi waje,
Sawwama bata bar gidanba sai magrib Hajiya ya sanya aka kaita,
Aranar ta yi bacci cikeda damuwa cikin dare tafarka saka makon wani mummunan mafarki
Sak shigen mafarkin datayi alokacinda akayi maganar aurenta da Sadam wannan mutumin nan dai wanda yake neman taimako wajanta cikin mafarkinya yau fuskarsa tafito mata tass ba kowa bane sai yareema tarasa abunda wannan mafarki nufi,
Washe gari haka tatashi mama saida yakasa hakuri ta tambayeta abunda yake damunta,
Ta shaidawa mama Abunda yake faruwa sannan tace "ni ban dauka dawani abuba shiyasa ban fada mukuba koda muka dawo ma ni namanta da yafaru sai gashi naj yazo kamar yanda nafada miki wai ciwo yasake tashi Mama kasa cewa komai tayi dan dai ita ranta bai amince da wannan aurenba tayyaa za'ace yarta taje ta auri wanda baimasan kansa ba gabaki daya, sai dai har cikin zuciyarta takejin tausayinsa amma tausayinsa bazaisa tayi tsautsayin barin yarta ta aureshi ba,
Bayan Baba yadawo a kasuwa dayake yanzu karfe hudu ya dawo yabar yaron shago Mama ta jere masa abinci akan dining ya zauna yaci bayan yagama tashiga masa bayanin abunda yake faruwa, sannan ta daura da fadin amma ni ban amincewa wannan aure ba tayaya za'ace ta auri wanda shima baisan kansa ba sucire son zuciya a wannan lamarin,
Amma Baba baice komaiba har washe gari Baba baice komai gameda lamarinba,
Bayan ancika kwana biyu Baba yana zaune ya kishingida jikin kujera Mama tace "Baban Hafsa nayi maka bayanin abunda yake faruwa amma bakace komai ba,
Nanma dai kamar bazaiyi maganaba sai kuma can yace "kiramin Mamana,
Mama tatashi tayi wajan Sawwama tashiga falon da Sallama sannan ta karasa ciki ta sameta kwance su muhammad kuma na wasa tsakar dakin Hameeda na gefenta tana bacci, itama idanuwanta a lumshe amma ba bacci takeyiba tsabar tunanine kawai mama tadan dade akanta amma bata saniba saida tayi mata magana sannan tace" Hafsa Babanki yana nemanki Ahankali ta bude idanuwanta ta mike dan amsa kiran mahaifinnata."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial19 Chapters
A God's Pub
A god's pub is place of mystery, full of wonder and adventure. Those who wander inside shall find another world, both familiar and unknown. Enter through the door and find out, just what awaits you on the other side. Gods, spirits and demons live together in the one city that houses them all. A city with as many names as there are beings inhibiting it- the city of a billion names! Located inside this extraordinary city which few mortals ever sat a step into is a certain pub in a certain city with a certain god serving as both it's owner and bartender. What happens if this god decideds to keep a young woman that mistakenly entered his pub? The cover image is not owned by me, the artist is: https://www.artstation.com/waynechan If the artist want's me to take it down I will immediately do so. Sadly I could not contact her to ask for permission. If anyone can do so in my stead I would really appreciate it!
8 84 - In Serial8 Chapters
Roma
I stood at the top of the game, but was forced to abandon my true dream.Now that I have another shot, I won't let it slip away again~ Renata Cassius was the teen prodigy of the game 'Ambush', holding the title of best player in the world. But her real dream was beyond that - it was to stand at the top of a pro scene, to lead a team to victory. And with the release of 'Legend', an unknown quantity in the world of Full Dive VR games, she might just have the chance she's been looking for.
8 149 - In Serial9 Chapters
The Usual VRRPG
2068 The earth has changed. Global warming Already passes the 50% stage. United Nation (UN) makes a statement that they will release the virtual reality game that already been developed. The UN hopes the second earth inside the game will slowly reduce the earth destruction by reducing the activity in the real world. ---- Jonny Darker is an average university student that studying Psychology. When then UN release the news, his best friend Aska asks him to play the game. But on the contrary, he refuses because he is doesn't know much about game expect a classic game like Tetris. Until Aska bring all of Jonny Circle of best friend to persuade him. At last Jonny agree to play the game with one condition they can't leave him alone. This is the story of a newbie player to become a famous virtual gamer. ****** This story is new, not like my other novel that already done in another language except translating into English. Warning !!! English is not my Native Need a lot of data and idea so if you have an interesting data and idea message me I will gladly put them to the story. A lot of error especially grammar. Try to be patient with me. Slow release and maybe slow pace story. P.S : My Art Hand Is Still At Kindergarten Level So Please Don't Laugh ^^ Thank you
8 111 - In Serial12 Chapters
The Forgotten Shield and The World Heroes (Remake).
When 10 students find themselves being transported into another world, 1 of them will find a home and new adventures in this new place while the other 9 gets themselves involved in a war. The world Heroes have been summoned, a lost "title" has come back, and a world of fantasies and adventures is waiting to be explored. This story is a remake in English of "El escudo Olvidado", you can also find this story on WattPad.https://www.wattpad.com/story/126788458-the-forgotten-shield-and-the-world-heroes-remake
8 152 - In Serial103 Chapters
7 Dragons and Princess
A world where power is everything,a story about half breed and princess .not a journey to see the vast world but also a journey to change the world.
8 189 - In Serial8 Chapters
IGCSE BIOLOGY
- Chapter by chapter of IGCSE Biology syllabus - Disclaimer: I AM A STUDENT. I cannot guarantee that everything written is accurate.
8 142

