《ƘADDARAR RAYUWA》K Page 93
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 93
"Kamar yanda kika gani ni yar gidan sarauta ce mahaifina shine Babban sarkin da yafi kowanne sarki matsayi a kasarnan bama kasarnan kadaiba hattada Kasashen waje sunaji dashi saboda kasancewarsa mutum mai ilimi,
Matansa guda hudune wacce muka fara zuwa wajanta bayan saukarmu cikin masarauta itace babba sai mahaifiyarmu nida mahaifin wannan maras lafiya wanda kika ganshi,
wanda kikaji ana kiransa da Yareema,
amma ita mahaifiyarmu ba yar kasarnan bace,
alokacinda akayi gasar karatu acan kasar saudia itace wacce tazo na daya, ba mazauna cikin saudiya bane aslinsu yan kasar ne amma ba mazauna cikinta ba kasar bane suna zaune awani kauye dake yankin kasar,
Alokacin mahaifina yaganta ya nemi auranta toh cikin yardar ubangiji da rabon hauhuwarmu suka bashi auranta dake a wannan lokaci suna masu shirya wannan gasar karatu ta kasa gabaki daya,
Kuma dama shi babban Malami ne wanda yayi suna a duniya baki daya,
Mahaifiyarmu bata kasance yar gidan masu kudi ba amma iyayenta sunada arziki abunda nake nufi da arziki shine sunada Karamci da sanin darajar mutane ba lallai sai kudi bane yake zama arziki akwai abubuwanda Allah yake azurta su dasu, Mahaifiyarmu tanada Hakuri nutsuwa da hankali sannan ga biyayya duk wani abunda mahaifinmu zai sanyata har indai bawai yasabawa addini ba bazata taba bijirewa ba sanin kanki ne ayanda mahaifinmu ya kasance mai cikeda addini bazaima taba kokarin sakata abunda zai sabawa ubangijinta ba tunda shima bazai iya saba masa ba,
Mahaifiyarmu ta fuskanci kalubale dadama a gidan sarauta amma dake ta kasance mace mai hakuri bata taba sanya hakan aranta harya dameta ba halinda na kirki ya sanya tashiga ran mahaifinmu yana matukar kaunarta wanda saida kowa dake cikin wannan masarauta yasanda hakan,
Ana haka mahaifinmu ya karo mata har guda biyu bayan wani lokaci amma dukda haka yacigaba da nuna mata soyayya,
Sauram matan babanmu a yanda suka nuna mana basuda matsala suna nunawa kowa soyayya sai dai bamusan abunda yake a cikiba dan masarauta ba wajene wanda zaka saki jiki da kowa ba dan kawai ya nuna yana sonka a ido,
Yanada yara sai dai dukansu matane sai guda biyu Yareema wanda Hajiya babba ta haifa m sai kanina mahaifin yareema kenan,
Mahaifiyarmu batareda shekarunta sun wani jaa ba Allah ya daura mata ciwo yan kwanaki tarasu munyi kukan rashinta daga baya muka Fawwalawa Allah komai,
Mahaifinmu yacigaba da kewar mahaifiyarmu nan ya dauki son duniya ya daura mana komai mu, komai mu toh anan ne kuma sai Al'amura suka fara cakudewa domin Hajiya babba tafito mana da halinta kiri-kiri ta nunawa duniya ba sonmu takeyi ba,
Bayan wasu shekaru Danta wanda shine magajin mahaifinmu yayi aure matarsa itace Hajiya suwaiba wacce muka gaisa da ita bayan mun gama gaida matan Abbana,
Nima ban dadeba na auri Alhaji nabar kanina a gidan yana ganin kalubalen rayuwa,
Akwana atashi shima ya giram yakai mallakar nasa gidan abbanmu yayi masa aure, a kankanin lokaci Allah yabashi haihuwa shine yareema toh yareema yafara girma baifi shekara goma sha aduniya ba Mahaifinsa kanina kenan da babban yayanmu yareema sukayi hatsari dukansu suka rasu,
Advertisement
Anshiga babban tashin hankali a wannan lamari sosai dafarko munyi tunanin Da makarkashiya a hatsarin toh amma wa zamu zarga?(Abunda yafaru shine Hajiya Suwaiba itace wacce ta shirya wannan hatsarin Alhali batasan cewa harda mijinda za'ayi tafiyar ba dan shi bayama kasa, shikuma ya rigada yayiwa kaninsa waya akan yazo ya daukoshi a airport saisu wuce wajan taronda zaije gabaki daya,
Hajiya suwaiba ta aikata hakanne saboda taga yanda Mai martaba yake nuna soyayyarsa ga mahaifin yareema, shine ta shirya kasheshi abun kuma ya auku harda mijinta, dake itada yayarta Hadiza kawai sikasan zancen sai suka boyeshi luff amma tabbas tayi dana sanin faruwar wannan lamarin, taji dama bata kwatanta aikata hakanba domin itama tayi rashin jigo a rayuwarta gabaki daya, bata sakeyin dana saniba sai da taga yareema Haleefa yazoma shinr wanda zai gaji gari da sahalaewar mai martaba instead of yaronta wanda a ganinta shi yakamata abashi kujerar mahaifinsa sai taga ba hakaba
Shikuma mai martaba yayi amfanine da wanda yafi kowanne ilimi hankali nutsuwa uwa uba iya zamada mutane da tausayinsu sannan kuma yabi zuciyarsa na soyayyarda yake yiwa yaron ya nadashi akan wanda zai gajeshi,
Masu karatu yanzu dai ni daku kadai mukasan wannan abun banda sauran mutane)
Hajiya taci gaba da fadin wanda lamari bamusan wanda ya shiryashi ba babu wanda za'ayi zargi fiyeda Hajiya Babba domin itace ta nuna tsanarta a garemu karara,
Amma Idan hajiya Babba ce itama harda nata yaron sonda Mahaifinmu yakeyiwa kanina shiya koma kan dansa yayinda Ya nadashi magajinsa domin shine wanda ya cika zati da sura sannan da kalamar zama sarki shine wanda ya cancanki ya mulki mutanen kasar gabaki daya,
Rashin mahaifin Yareema ya sanya yake kallona kamar mahaifinnasa nima ina sonsa cikin raina ina jinsa wani lokaci har fiyeda yaranda na haifa domin kuwa dan uwana nake kallo a tattare dashi,
Yasaba da yarana sosai barinma Abubakar bazaki taba cewa ba ciki daya suka fito ba bayan kamanni ga shakuwar jini da Allah ya hada musu,
Kullum suna tare zamansa yadawo nan dan shima yafijin dadin nan din domin yana soyuwa agaremu gabaki daya,
Dake mahaifina yana bukatarsa kusa dashi yasa zaman nan yayi masa wahala sai dai duk weekend yana hanya,
Ko ranarda wannan lamari zai auku masa sai da yakirani ya sanardani cewa yana hanya nagama shirin tarbansa najishi shiru naduba lokacin da yakamata ace ya iso bai isoba,
So saina kirashi wayarsa bata shiga hankalina bai kwantaba nayita kiransa nakira yayansa Abubakar naji ko suna tare ya shaidamin sunyi waya yace masa yakusa isowa dan mota yabi ba jirgi ba sai kuma nakira mahaifiyarsa ta shaidamin aiya dawo yashiga daki yana bacci toh kinji daga yanda al'amarin yafara."
Ciwonanm Allah yabarwa kansa sanin abunda yake fili dana badini,
Tunda wannan lalaura tasamu yareema banu taba kallon canji irinna lokacin da kuka haduba bamusan abunda Allah ya kunshe gameda wannan lamari ba,
Amma Hafsatu inaji ajikina wannan lamari alkahirine zai biyo bayansa,
Bazan tilasta kiba bakuma zan rokeki kona nemi alfarma ba dannasan zakiyimin idanna rokeki koda kuwa ace ranki baisoba,
Advertisement
Abunda yake fariwa shine yanzu haka abbana yataso zuwa nan ganin domin nemawa Yareema auranki, dam-dam dam gaban Sawwama yafadi takasa dagowa tadubi Hajiya nan danan idanuwanta suka cike fa hawaye tunani take cikin ranta tana fadin Wannan karon kuma irin Kaddarar da Allah ya jefo mata kenan?
Hajiya tacigaba da fadin alfarmar da zannema wajanki guda dayace itace idan baki aminceba karki zalinci kanki ko kiji nauyina ko kunyata kice kin amince kifito kai tsaye ki nuna abunda yake cikin zuciyarki hakanne zaisa hankalina ya kwanta,
Suna cikin haka Aysha tashigo da Sallama tacewa Hajiya mai martaba ya iso yanzu haka Alhaji sun tafi rakoshi daga Airport,
Hajiya tace "toh Alhamdulillhi tunda ya iso lafiya ke aina kikasan isowar tasa?
Anfara uploading a yanar gitso shiyasa nagani tayi maganar tana juyawa hankalinta nakan wayarta,
Hajiya ta dafa kafadan Sawwama tace anty hafsa bari naje mugama shirya komai, kafin su karaso
Idan kikaji zuwansu zuwa jimawa sai kishigo ku gaisa, dakyar Sawwama ta iya gyada kanta hajiya tafice,
Tsawon 1hour da isowarsa amma bata tashi daga yanda takeba tarasa abunda yake mata dadi a duniya komai yataru ya cunkushewa kwakwalwarta,
Tambayan kanta takeyi
Shin ta amincewa wannan auren? Idanta amince hakan yana nufin zata zauna da wanda baisamma waye kansa ba bare iyayensa itama kawai tasan yanayin rashin lafiyarsa ne yake nuna mata kamar ya santa,
Idan ta aureshi tasan rayuwarta ta dakushe gabaki daya kenan dan babu wani jin dadi ko farin ciki da zata samu a auren wanda baisan menene kansa ba ganaki daya tay-tayi ko hawayene ya digo daga idanuwanta amma yaki zuba,
Gaskiya bazata iya amincewa wannan aurenba ita batama tunanin sake wani auren a rayuwarta tun rasuwar Abubakar takeji bazata sake wani aurenba saboda farin cikin daya bata iya rayuwarta yananan zaune a kwakwalwarta bataso wani yanayi na daban yazo ya dakushe wannan farin cikin da yabarta dashi,
Idan zata sake aure kuwa toh tanaji iya gidan Sadam zata sake iya komawa Masoyin Asali ko wani hali yake? Yana tunaninta koya manta da ita?
Zata koma gidansa su rungumi yaransu Muhammad kam tasam Hajiya zata rikeshi tayi masa tarbiya fiyeda yanda ita zatayi masa amma su hameed da hamdan kam koda idanuwanta ya nuna mata cewa mummy tana kaunarsu bataji zuciyarta zata yarda da wannan kaunar tana zaune ahaka Hajiya ta aiko ayi kiranta jiki a sanyaye tatashi ta fita har falon Alhaji Da sallama tashiga jiki a sanyaye."
—————-
Yau Sadam yafita a dakin Hafsa yakoma dakin Abida har ila yau bai taba yarda wani abun yashiga tskaninsu ba kullum yakance mata bazai iyaba ko yana gajiye ko wani abun kuma tana labe idan suka kebe adaki da hafsa tanajin abubuwanda suke faruwa wani lokacin idan tajiyo ya hanata nutsuwa wani lokacin kuma ya hanata bacci amma kamar aikin Allah sai taje tayi,
Kwanciya yayi abunda yabarta kamr kullum tayi masifa tayi masifa amma yaki kulata daga karshe saita fashe da kuka yana kwance yana jiyo kukanta a hankali zuciyarsa tafara karaya,
Yana daga kwance yafara fadin meye kuma na kukan? Kiyi shiru kibarn nayi bacci,
Kuka ta kara volume hakan yasa ya mirgina barinda take kwance badan ransa yasoba yafara jijjiga bayanta yana lallashinta da wannan damar tayi amfani harta samu abunda take nema a wajansa."
Washe gari ta safe duk wata hanya da zatabi dan sanya Hafsa tagane abunda yafaru a tsaknainsu saida tabi Hafsa taji haushi kam sosai aranta amma kuma afili saita nuna ko inkula,
Dan taga abidar ba kaine da itaba idan tabiyeta zasu samu babbar matsala itakuma bata wannan hanyar takeso ta bullo mata ba,
Ta lura ita macecec mai masifar kishi toh da wannan hanyar zatayi amfani wajan cusguna mata,
Zaune suke a falon kowacce danne-danne kawoa takeyi da wayarta babu mai kula wata a cikinsu,
Sadam yashigo daowarsa daga aiki kenan, Hafsa tatashi da sauri tana masa sannu da daowa tana isa wajansa ta rumgumeshi batareda ya lurada Abida dake falonba ashariyarta kawai yaji hakan yasa yasaki Hafsa cikin bacin rai yadubi Abida yace "amma dai kinsan nanba gidan arna bane koh?
Abida cikin takaici tace "au haba? Sadam yaja tsaki kawai yashige ciki zabar bacin raima ya manta dakin abida yake yawuce dakin Hafsa Hafsa kuwa tana kallo bata hanashi ba tabi bayansa, suna shiga takarbi jakar hannunsa ta taimaka masa yafara rage kayan jikinsa,
Tana kokarin zugr zip na wandonsa dan tayashi cirowa Abida tashigo domin tana gama zagin datsu ta juyarda kanta gefe batada yanda yashiga ba saida tabishi daki ta kare masa bala'i bata ganshi ba shine ya biyoshi nan,
Tana kallonsu haka tayi kan Hafsa tana zaginta Sadam yayi saurin shiga tsakani domin kokarin kai mata duka take, rai bace yace "wannan wani irin haukane Abida? Zaki shigo mana daki kai tsaye haka harma kina neman kaiwa matata duka ,
Abida cikin bacin rai tace Au ni bakuga abunda kukamin ba dake nice uwar bakin jini laifina kawai kake kallo?
Sadam yace "dakata me akayi miki? Yanzu bazan taba daukan wannan haukar ba kisani idanma rabuwa dakene kikeso nayi zan rabuda ke kije dannagaji da wannan haukar yakamata ace yanzu nima nawa hankalin ya kwanta,
Jin zancen rabuwa ya sanya jkkin Abida yayi sanyi tasaka kuka tace "kai baka kallon laifinta yanzu fa kwananne kazo dakinta tana cire maka kaya kuma kunsanda hakan sai acuceni nayi shiru,
Dafe goshi yayi dominshi ya manta ma da hakan, da sigar lallashi yace "kiyi hakuri na shafa'a bata kulashiba taifice yabi bayanta Hafsa tatabe baki."
Ayita Hakuri dani har Allab yakawo na kammala gabaki daya school ne sai daukan zafi take nagode sosai da muna kaunarku da wannan littafi, in sha Allahu komai yazo karshe saura kiris."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial25 Chapters
Blut und Eisen: Blood and Iron
An old man haunted by a past filled with regret is thrust into Royal Road as his family tries to save his mind from the effects that comes with age. A grandson's search for his own identity and that of his family. What does it mean to be associated to an unspeakable era and can you truly escape from it in the virtual world…. Or in Gerhard's case, is there even any reason to? Now given a chance, will his soul once again awaken to a second life of Blut und Eisen: Blood and Iron
8 150 - In Serial202 Chapters
Contractbound
A man with two souls inhabiting one body found himself tangled in the supernatural world involving dark rituals, human sacrifices, and unbelievable creatures. Graham and Valentine Hymes, in their journey of finding the true nature of their origin, were sucked into an even bigger plot that they had never imagined before.
8 204 - In Serial9 Chapters
Demiurge: The Creator
Formerly known as Demiurge. Everything from Chapter six is new! Cryptic Synopsis: Eternity is not a dream.Death does not reign supreme. Death, I continue to be.Breath, stay away from me. As the silence becomes ever greater.I become Demiurge, the creator. Normal Synopsis: Adam hates the world, yet he loves life. So he does what every reasonable person would do and decides to leave this world, literally, as he becomes a test pilot for an interdimensional travel experiment. Hoping to find another, better, world. A world he found, but is it better?
8 102 - In Serial9 Chapters
Dennica/Daystar
Inspired by Slavic and Eastern European folklore, this story will take you to the tsarstvo of Suntolia, where we will follow the life of the four Petrosinovi siblings - Vulchan, Albena, Bozhana and Kalina. With Vulchan being crowded at a young age due to unfortunate events, each has to carry out the weigh of their new position, yet they are unable to let the desires of the heart.Will they be stronger than the family curse and see the daystar in the sky..."In this family, you either die young or live to suffer..."
8 134 - In Serial22 Chapters
✿ Khuda Ka Shukr Kaise Karun ✿ || HOW TO THANK GOD ||
||sPoiLeR||You will love the chemistry between the following characters. →_→Hakan, Aliana, Adeel, Hoorain, Idris, and Gulnoor are the main characters. Villian roles were performed by Dilara, Zoya, Junaid, Aslan, Hamza, and Altan. As the story progresses, new characters will be introduced.←_←♡♡ HAPPY READING ♡♡❥ A writer only begins a book. ❥ A reader finishes it. _ Samuel JohnsonName of the book: Khuda Ka Shukr Kaise Karon [How to Thank God]Author: Tasneem ✿ Language: English and Urdu (Anglo-Urdu)Translation: Available✓Genre: General Fiction/ Romantic ( Halal Romance)Total no of chapter: 10 [On-going]Total number of characters: 25■ This is my first ever book about spirituality, iman, tawakkul, and taqwa. ■ It's a tale of true love, twists, mystery, cute romance, fun, social, adventure, suspense, and thrillers. ☞The story gets better by reading further, and the more you read, I hope so:)✿ I would appreciate it if you would read, share, comment, vote, and follow me.◕ᴗ◕✿ Stay tuned!!! Also, please show your support for the #KKSKK [How to Thank God].✿ And thank you so much, my true readers, for your love and support.Started: 10.08.2022 (On-going)#KKSKK ||How To Thank God||_Tasneem ❥All rights reserved.Copyright © TasneemWrites9Ranking August 2022# 1 spiritual out of 30.4 K # 2 urdu out of 1.06K# 5 urdu out of 10.9K# 2 novel out of 391
8 96 - In Serial69 Chapters
The Boy Who Read Minds ✔️
Highest rank: #1 in Teen-Fiction and sci-fi romance, #1 mindreader, #2 humorAaron's special power might just be the coolest- or scariest- thing ever! It's always helped with his bad-boy reputation, his rightfully arrogant all-knowing intimidation seemed to go a long way with his love life and somehow also his education.Until he met Violet, one of the smartest girls in school; a girl he's been using for years, zoning in on her mind to ultimately cheat on exams and steal the title of valedictorian. Until one day, Violet failed him. Her mind wandered all over the place- her parent's divorce, her breakup, and he couldn't help but sympathize. But Violet's a smart girl, who knows how long it'll take before she finds out.Aaron depends so much on his mind-reading capabilities that when they suddenly disappear- so does everything he hasn't worked for. His secret was like Samson and his hair, once it's told, the magic's all gone.Word count: [85,000 - 92,000]***Copyright © 2021#1 TEEN FICTION#1 mindreader#1 sci-fi romance#8 romance#2 humor#1 puberty#1 superpowers#1 sweet#35 comedyFor business inquiries, please contact: [email protected]BOOK 1 of the Mind Reader Series
8 136

