《ƘADDARAR RAYUWA》K page 92
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 92
Kwanansu hudu agarin amma gabaki daya garin ya isheta damuwarta kawai taganta agida Hajiya kanta ta fahimci hakan shiyasa ta yanke shawarar kwana biyar kawai zasuyi su koma hakan yana nufin saura kwana daya kenan,
Hajiya Sam batason ganinta cikin yananyin damuwa har irin haka,
Ta lura idan suna zaune ita shiru kawai takeyi tana tunani idan aka sakota cikin zance sai tayi murmushin yake kawai,
Yareema kuma gabaki daya ya hanata sakatt kuma baya taba yiwa kowa magana sai ita baya sakewa da kowa sai ita idan tabar wajan ya ringa musu tijara kenan bata samun lokacin kanta sai dai idan yayi bacci,
Har su umma hakuri kawai suke bata domin sun san ta takura dayawa amma babu yanda zasuyi,
Aranar Hajiya ta snaar musu cewa washe gari zasu koma nan kuma sai hankalinsu ya karkato kan lamarin toh idan suka tafi wani hali yareema zai kasance aciki?
Karfa akoka gidan jiya, su kansu shaidane baya taba yarda ya zauna waje idan bata a wajan kuma har lokacin bai saki jiki da kowa ba sai ita, yaya zasuyi kenen menen mafita?
Izuwa yanzu basu hango mafitar ba amma da ace zau kara koda wasu yan kwanakine tabbas za'a samu mafita,
Hajiya zaune gaban mai martaba kanta yana kasa bayan sun gama gaisawa sannan tace "Abba dama nazo na sanarda kai ne cewa gobe idan Allah yakaimu zamu koma gida,
Mai martaba saida yaji gabansa yafadi a tunaninsa zau dan kwana biyu,
Shiru yayi sai can yace "Bazaku dan kara wasu kwanaki ba? Tunda kinga yanda lamarin ya kasance kada kutafi kuma abu yazo ya baci azo akoka gidan jiya azuwa yanzu bamuda wata mafita amma nasan idan kuka kara kwanaki tabbaas zan nemo mafita,
Ajiyar zuciya Hajiya ta sauke sannan tace "Abba nima naaso nakara kwanakin tunda dama bada niyyar kwanakin danazoba kenan naso nafi haka amma Abba hafsatu tana takure matuka tana cikin damuwa ganinta a wannan yanayin baiyimin dadiba Abba kar garin son zuciyarmu ita kuma mu tauyeta tunda mijinta ya rasu na yi alkawarin bata farin ciki dai-dai gwargwado yana daya daga cikin dalilin dayasa nazo da ita nan,
Kar yazamnaa ni banbata farin cikiba kuma na sakata a damuwa batajin dadin zaman nan idan muka koma can duk wani abunda ake ciki sai a yanke, tayi magana yanda mai martaba ya fahinceta sosai,
Advertisement
Dan haka baija wani zance ba,
Mai martaba ya nisa sannan yace "hakane maganarki kinyi tunani mai kyau shikenan yanzu kuje in sha Allah zamusan abunyi,
Hajiya tayi masa godiya sukayi sallama da fadin gobe zatazo yimasa Sallama,
Sawwama jin zasu tafi washe gari taji dadi sosai sai take ganin kamar gobenma bazata yiba,
Washe gari jirgin 12:am suka biyo suka dawo gida sai asannan sawwama taji sanyi aranta,
A gidan Hajiya suka wuni zubur sai yamma likis kafinnan tasaka driver yakaita da muhamnad da tsarabarda suka zo da ita,
Babu wanda tabawa labarin abubda yafaru agidan tacigaba da rayuwarta kamar yanda tasaba, amma sai dai wani abu guda daya shine tausayin Yareema takeji aranta ko menene ya sameshi ya kwanta ciwo haka tsawon lokaci?
Menene alakarta dashi wacce ita bata saniba? A iya tunaninta tayi amma batasan wani abunda yataba hadata dashiba.
Nisawa tayi sannan afili tace "Allah yabaka lafiya dan har cikin ranta tana tausayinsa."
Yareema yasake shiga wani hali a hankali-hankali ciwon yake dawowa yanaso yakoma kamar na baya mai martaba Umma da sauran hankalinsu ya tashi ganin abunda yake shirin sake faruwa,
Mai martaba ya rigada yagama yanke hukunci cikin zuciyarshi dai dai har izuwa yanzu bai fadawa kowa Bayan yazo ya duba jikin yareema yafito falo yasamu su Umma suna zazzaune suna kallonsa gabaki daya suka mike shikuma ya zauna akan kujera sannan suka zauna a kasa,
Yadubesu zuciya cikeda Damuwa yace "Ga dukkan alamu abunda banaso shine yake shirun sake faruwa jikin yareema yanaso yasake dawowa kamar nabaya,
Bamuda tabbacin abunda yake faruwa gameda wancan yarinyar (Sawwama) amma inada yakinin cewa akwai wani abun dake kulle tasakanin wannan ciwon dakuma ita yarinyar bamu saniba ko Allah ya rubuta cewa warakarsa na tareda ita shiyasa tsawon lokaci mukayita neman magani Allah baiyiba amma gashi a mintuna kadan da haduwarsu sai Allah ya nuna mana ikonsa, yanzu gashi tatafi abu yanaso yadawo,
Shiru yayi sannan yacigaba da magana "narigada na yanke hukunci cikin raina amma yazama dole na shawarceku matsayinku na mahaifansa zan tafi dakaina har can garin na nema masa auran wannan yarinya domin hakan shine kawai mafita,
Umma wacce itama ayanzu tasan batada wata mafita data wuce wannan dari bisa dari tabawa mai martaba goyon baya,
Amma sai dai ita yarinyar basusan ko cewa zata aminceba, amma zasu fara tunkarar Hajiya da maganar kafin akaita gaba,
Mai martaba yace "idan Allah yakaimu gobe zan tashi natafi can kuma inaso har naje nadawo babu wanda zai san abunda yakaini,
Advertisement
Da mamaki suke kallonsa da sukaji abunda yafada wai gobe zaije can, mai martaba da kansa zaije akan wannan maganar shida bama mutumbe mai son tafiya ba, barinma da akace yareema ya kwanta rashin lafiya sam baya nisa da gida saboda tsoron abunda zaije yazo,
Umma cikin ladabi kanta yana kasa tace amma Mai martaba daka tura wani basai kaje da kanka ba koda wasu daga cikin amintattunka katura za'aje kuma zasuyi abunda yakamata,
Mai martaba cikeda damuwa yace "wannan lamari yanada muhimmanci sosai a wajena bai kamata ace nayi wasa dashiba bayan ku nan dana sanar daku babu wanda zai san abunda zai kaini, kuma na gargadeku karkowa yasani,
Umma tace "in sha Allahu babu wanda zai sani, mai martaba yace "Allah yayarda akowani lokaci yana fada musu su boye samun lafiya da ciwon Yareema bawai dan yana tunanin zasu fada ba sai dan kawai yanaso yasake jaddadawa."
Da dare Hajiya na zaune wayarta tafara ruri tana dubawa taga mahaifinta da sauri takai hannunta taja ta amsa kiran cikin ladabi ta gaidashi ya amsa cikin hikima mai martaba ya zayyana mata abunda yake shirin faruwa da kuma wanda yafaru m bayan tafiyarsu,
Hajiya tayi shiru sai can tace "Abba ni aganina hukuncin daka yanke bayida laifi hakan yayi yareema danane ni kaina mai bashi aurene ya aura ko aysha akace a aura masa a yanzu banida jaa zan bashi zuciyata daya kuma hankalina kwance amma dubada condition dinsa a yanzu bana tunanin Hafsa zata amincewa auren kokuma zatayi farin ciki da auran Abba rokon danakeso nayi maka guda dayane in sha Allahu gobe zan kirata muyi magana kafin kazo amma har indai bata amince ba inaso kayimin wannan alfarmar kada a tilastatta ko abi ta wajan mahaifanta yanda zasu sanyata ta amince, inaso tayi farin ciki tayi aurenta zai sanyata farin ciki tasamu nutsuwa fiyeda yanda tasamu wajan Abubakar lokacin yana raye,
Shiru mai martaba yayi jim kadan sai kuma yace "toh shikenan Allah yakaimu goben nayi miki wannan alkawarin babu wanda zai tilastata, amma kifara magana da ita tukunna kafin na iso jirgin rana zamubi bayan azahar in sha Allahu zamu iso,
Hajiya tace Allah ya kawoku lafiya sannan sukayi Sallama."
Wa she gari ta sassafe Hajiya tafara aikan abubuwan da za'ayi na bukatar wanda za'a tarbi baki dasu,
Wanda zatayi ordernsu kuma tun adaren jiya tarigada tayi karfe tara takira Sawwama tace tanason ganinta batareda wani tunani ba Sawwama tadauki muhammad dake su Hamdan suna makaranta tataho,
Ganin ayyukan da akeyi ya sanya tmdaga zuwanta itama tashiga aikin cikin kankanin lokaci suka gama tangamrmen falon Alhaji na tarban baki aka sake gyarawa dukda koda yaushe acikin gyara yake aka jere abubuwan acan lemu kuma da na kanti da wanda suka hada da kawunansu aka sanyasu a cikin firiji,
Sai bayan angama aikin Sawwama tasamu zama Hajiya kam bata samu zamaba domin tasa anata gyaggyara ko'ina dan mai martaba wannan karonne zuwansa na biyu gidanta da rasuwar Abubakar sai wannan ko auran yaranta yazo daga zaran an gama daurin aure daga can yake wucewa,
Shi kansa alhaji ya kansile duk wasu schedules dinsa na ranar ya gayyaci wasu daga cikin abokanansa kawai suna jiran zuwan mai martaba."
Hajiya babba tana zaune rohoto ya isota cewa mai martaba zaiyi tafiya da garinda zaije amma sai dai basusan abunda zai kaishi ba Hajiya Babba tashiga taraddadi sosai domin mai martaba baya tafiye-tafiye shi sam idan yabar gari kuwa toh zaije Kasar saudia ce, sai kuma wani Babban lamari dan haka gabaki daya hankalinta baikawo mata cewa wai zaije nemawa Yareema aure bane amma duk da hakan ta sanya ayi mata binciken abunda zai kaishi garin."
Saida sukayi sallar azahar sannan Hajiya tasake wanke ya shirya cikin Lace tazauna a dakinta sannan ta nemi ganin Sawwama,
Sawwama tamikr tabar muhammad wajan Aysha dan tasan maganace mai muhimmanci tunda a uwar daki za'ayita,
A zaune tasamu hajiya akan Sofa dake cikin dakinnata saida gabanta yafadi dan wata iriyar kama da Hajiya tayi mata da Abubakar, gabaki daya shima kamanninta ya dauko,
Dakyar ta iya saita kanta dan hawaye ke son gangarowa a idonta ta maidasu sannan ta isa da Sallama Hajiya ta amsa tana sakar mata da murmushi zama tayi kasa nan kan carfet kanta yana kasa tace "Hajiya gani,
Hajiya tadade tana kallonta ahaka takasa furta komai jin shiru yasa Sawwama tadago taga ita Hajiyan ke kallo saita maida kanta ta sunkuyar Hafsatu! Hajiya ta kira sunanta a hankali ta amsa da fadin "Na'am,
Iska Hajiya ta furzar Sannan tace."
Nayi test jiya shiyasa jiya da shekaran jiya kuka jini shiru na tsaya na dan taba karatu, Allah ya taimakemu baki daya ya biya mana bukatunmu na Alkahiri nagode sosai da Hakurin da kukeyi da yanayin typing dina in sha Allahu komai yakusa zuwa karshe nahuta kuma ku huta. Sai dai comment dinku yayi kasa sosai😩😩 dan Allah kudaure kuna comment dayawa ko zan samu naji karfi nagama tashi daya."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial227 Chapters
The First Corridor of Old Works
But what is it, really? Old Works. They say, some do anyway, or would, if they still had tongues - it's a dream. That it's a million year old mystery connecting three planets. Some, yet other, anonymous entities, charge that it's a structure, more accurately, an architecture - a quest, even, made from, and through - corridors. Pretty inarguably, for one thing, it's a maze. Even some pronounce, if you can understand those currently vomiting blood, that it's a corporation, and yet others - the brave ones – and dead - say it's... near death. Or that it is. Death. - Death itself. But that dark thing on the horizon, that thing emerging to replace the only system we... know. - Whatever it is it couldn't be the end, of everything, could it? Eminently possible, but - it couldn't be worse? 3 civilisations/3 planets... and Old Works. 4 heroes: The Cyclops seeing out his Eye the reality of that place - and by means of that vision - greasing the many-toothed gears of that great old churning nightmare. The Writer sweating to keep the story alive that supports the great old lying structure. The Fake King who abides among all those tunnels of dreams and lies and dreams and... slaves. And the Hero Dreamt, all those slaves - to maintain that structure's even functioning, have to - at all... they dream him. They literally dream him. But that thing, from whence, who knows, arriving? What kind of sick demonic mind could even - But it can only be psychosis - Or possession. Reducing all of reality to some kind of – what would you call it? A Game? A video... joke? And that half-Cyclops, that beauty – what does she have growing – beneath her supernatural genitals? A game for him? A game/a dream; a – world? Or just Old Works. And this Wound in reality – that our writer near-died putting inside her. What is it anyway? And what reality does it bring with it. This demon or God. Through the corridors; lattices of smoke and shadows and colours; dungeons; and supernatural organs; the labyrinths made from dreams... and flesh. - What happens when they face that Wound – staring the absolute. right. in. them? - Through - What happens to all us... slaves... then? But at the end of the hallway, you see it there, I say you do, that turning - It's only the First Corridor of Old Works. This finished 104,000 word kind of LITRPGy fantasy novel, the First Corridor of Old Works will be released in daily 2000 word chapters, or equivalent [unfailingly at 20:47 GMT] Immediately followed by the Second Corridor of Old Works [161,000 words, edited, ongoing, as of 24/09/21] At first lite on stats these LITRPGy elements will become increasingly - built meticulously upon what precedes - ubiquitous, as we proceed into a world painstakingly built to support these mechanisms. After - minimum - 6 months, this manic daily release schedule will be somewhat relaxed: 5 days a week. - But don't lie to yourself it's not there. That thing watching at the end of the hallway... and where it leads. It's - Of countless, it could only be - The First Corridor of Old Works.
8 192 - In Serial8 Chapters
The immortal and the personification of mana
Aurum the once immortal have travel back into the past and is now ready to stir the path this time in a better direction than the previous timeline. Will he be able to guide it back into a happy ending or will it be just the same as the previous one? This world is set in a medieval-like setting. Technology is advancing but it's still isn't the best thing yet.
8 172 - In Serial6 Chapters
CHAOS: The Youth and The World of Wonders.
What had been forgotten, wasn't worth the memory. The youth woke up with no memories of his past. He didn't know his own name or his own origin, but he knew he wasn't alone, at least in this body. There was another one, and both of them didn't know much about each other. They had a conversation, but their conversation ended with a darkening world. The youth woke again, inside a chamber made of rocks. Two kids around- a twin of girl and a boy- told him that he fell from the upper world into the deepest place, where the sun could never reach and a single-season took all of the year. The youth didn't wait long until he voiced his desire of returning to the upper world, but for some reason, the humans here would prevent him and chase him away... and the little girl who only glared at him eventually told him that someone inside her was saying that youth was the worst being he had ever seen. Not to cause trouble to anyone, the youth decided to go away... but he didn't know that wherever he went trouble would always await.
8 217 - In Serial24 Chapters
rich man's world; charlie dalton
(𝙳𝙴𝙰𝙳 𝙿𝙾𝙴𝚃𝚂 𝚂𝙾𝙲𝙸𝙴𝚃𝚈)Sigrid Taylor Hall is a sixteen-year-old girl with a big dream and an even bigger disagreement with her father. Fall of 59, she bakes her brother a batch of baked goods for the fourth year in a row and breaks into his room to surprise him but when the door opens she's shocked to see that his dorm did not belong to him anymore. Instead she's met with a snarky, witty seventeen-year-old boy named Charlie Dalton. It all started with a tray of blueberry coffee cake and the words, "I don't remember being named Peter but hello to you too." - - - - - - - dead poets society. started: may. second, twenty twenty-oneended: to be determined
8 239 - In Serial62 Chapters
Forget Me - [ j.jk ] ✔️
[ Book 1 ]"Pictures I'm living through for now, trying to remember all the good times. Our life was cutting through so loud, memories are playing in my dull mind, I hate this part, paper hearts."-Every year on January 1st at midnight, the human mind resets itself anyone in love. Zero memories of your partner. Everyone believes it as a curse so people get scared of falling in love. Out of the two, only one of you can love while the other one doesn't cause if both of you love each other, you both will forget each other by the end of the year. You never cared about love, relationships, the curse, only caring and paying attention to only your grandma and brother. But that changed with him. but was it okay to? - Jeon Jungkook.{ started } - august 16, 2020.{ ended } - december 14, 2020.
8 101 - In Serial9 Chapters
Hualian (READ THE DAMN DESCRIPTION PLS)
This is before they met. So I'm doing the whole story. Hehehe There WILL be smut in this. Smut is Hualian and maybe a little NanYao
8 134

