《ƘADDARAR RAYUWA》K page 91
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 91
kwance yake yana bacci ahaka baza'a taba cewa yanada matsala ba da bataji ana zancen bayida lafiya ba toh da sai tace baccin jin dadi kawai yakeyi fatar jikinsa sheki kawai takeyi irin wacce hutu ya amsheta,
Da dukkan alamu wannan fata tadauki lokaci bataga ranaba Ta tsura masa idanuwa tana kallonsa,
Bazata taba cewa majinyaci bane ahaka domin bbu alamun jinya ajikinsa, kallonsa takeyi tun daga sama har kasa ta tsaida idanuwanta a yattsun kafarsa sai kuma tasake dago kwayar idanuwanta har izuwa zara zaran gashin idanuwansa, sai take ganin kamar tasan fuskarsa awani waje,
A'ina kenan toh? Mutumin da akace yayi tsawon shekaru yana jinya kwance baimasan yanda yakeba,
Sai dai idan yayi mata kamada wani wanda tataba kallo,
Zama sukayi gefen gadon da yake dukansu ita kuma tazauna a side drawer dake jikin gadon kamshin turare taji mai masifar dadi tun shigowarsu takejin wannan kamshin gabaki daya rayuwarta sau daya ta taba jin turare mai dadinsa,
Umma tadubi Hajiya tace kinga dannaki koh? Gashinan yana baccinsa yanzu haka zancen danake miki yakai 1week yana wannan baccn
Sai jiya da jikin yataba shi hakanma bai bude idanuwa ba yanzu baifi yafarka sau daya a sati ba,
Kuma abun mamaki ba wata na'ura aka sanya masa da zata taimakeshi ba iko kawai na ubangiji ne,
Koda ya tashi sai dai ihu kawai yakeyi banda ihunsa shekara da dama banji muryarsa ba,
Hajiya tace "Allah ka dubi lamarin wannan bawa naka kabashi lafiya su duka suka amsa da amin,
A hankali Sawwama ta furta Allah ya yaye masa yabashi lafiya Umma tadubeta tadanyi murmushi sannan tace Amin,
Sun dade a zaune sunayi masa addu'oi sannan suka mike da niyyar fita itama Sawwama ta mike tafara tafiya a hankali,
Caraf taji an cafke hannunta atsorace ta juyo tadubeshi idanuwansa suna kulle kamar yanda tabarsu amma hannunsa yana rike danata gam,
Jan hannun tayi a hankali amma taji shi gam danba rikon wasa yayi mata ba,
Dayan hannunta ta sanya tayi amfani dashi dan raba hannusa da nata amma ko gizau hannun baiyiba, ganin bata tahowa ya sanya Hajiya juyawa tayi mata magana sai taga abunda yake faruwa ta kalli hannun sannan ta dubi Sawwama ta sauri ta karaso wajan ganin tajuya yasa hankalin Umma itama yakai wajan hardasu Ummi da aysha suka juyo,
A hankali umma tace "kiyi hakuri sannan ta sanya hannu zata raba hannu Gam taji hannun arike,
A fili ta furat "Yareema! Yareema! Yareema ka farka ne? Tayi magana ne duk da tasan cewa bazai san metake yi ko cewa ba,
Sake mata hannunta Yareema kaji?
Shiru dai bai motsa ba, a hankali ta sake kama hannun zata cire ta karfi ya jawota ta fado kansa da sauri tafara komarin mikewa sukam mutanen dakin tsayawa kawai sukayi kallon ikon Allah,
Umma tsoronta karya shaketa kamar yanda yataba shaketa shekarun baya dasuka wuce dan haka ta isa ta rikota tana shirin kwacota daga hannunsa kamar wanda aka tsikareshi ya bude ido, akan Sawwama ya saukesu,
Advertisement
Itama shi din take kallo idanuwansu ya hadu waje daya murmushi ya sakar mata Sannan cikin mamaki da al'ajabi ya furta kinzo? babu abunda sukayi miki?
Umma dake tsaye akansu saida ta zauna dabass akasa dan tsakanin mamaki rabonda taji muryar danta yayi magana an doshi kusan shekara tara,
Hajiya ta karaso dasauri tana fadin yareema! Yareema Alhamdulillahi kana jina? Kana cikin hankalinka kallonta yayi da alamun rashin sani a fuskarsa bai kulataba ya juya ga Sawwama yace "babu abunda sukayi miki
Sawwama sai tayi amfani da wannan damar tace "eh babu sakeni na tashi na zauna dasauri yakai kallonsa wajan hannunta daya rike sannan gata kuma kwance a ajikinsa, saketa yayi dasauri a fili ya furta kiyi hakuri,
babu komai tace sannan ta mike,
zata zaune can gefe yayi saurin rike hannunta yace "ki zauna anan tsoro nakeji karsu sake zuwa sutafi dake babu musu ta zauna dan har ita cike takeda al'ajabi yanzu mahaifiyarsa tagama fadin rabonda taji muryarsa yafi shekara takwas yanzu kuma gashi nan yana mata magana garau zatt mai hankali kai hakan yake nufi kenan?
Dakyar Umma ta iya mikewa daga yanda take tazo jikinsa ta rumgumeshi sosai tana kuka tana yiwa Allah hamdala saida tagama kukanta bai kulataba tayi masa magana yaki amsawa hankalinsa yana kan Sawwama gabaki daya,
Daga karshema hannunta yasake kamaw yarike gam kamar wacce za'a kwaceta,
Kowa yayi masa magana adakin yaki kulawa ko dagowa bayayi ya dubesu, itadai Sawwama ita kanta bazatace ga halinda take ciki ba a yanzu tarasa abunda yake faruwa gabaki daya takasa gane komai kanta ya kulle,
Umma tacewa ruma takira mai martaba da sauri tafice tashiga mota lokaci kalilan ta isa shashinsa batareda an tsayarda itaba aka barta tashige saida tazo shiga falonda yake a zaune sannan akayi mata iso a falon tasamu Hajiya Babba shiyasa batayi gigin sanar da mai martaba abunda yake faruwa ba, ganinta a birkice ya sanya mai martaba yadauka jikin yatashi dan haka yabiya suka wue can kai tsaye,
Hajiya Babba kuwa taji dadin wannan lamari domin itama a zatonta jikinne yatashi shiyasa akazo neman mai martaba, yan wahala tafadi bayan fitan mai martaba ta rigada tasan wahalarda kansu kawai sukeyi amma Yareema bazai tana samun lafiya ba,
Sashinta takoma saboda tasan idan jikin yatashi mai martaba yatafi to acan yake raba dare,
Abunda yaje ya samu yasha bambam da abunda yayi tsammani mai martaba yayi murnar wannan canji da aka samu daga wajan Yareema haaliafa kuma ya gargadi,
Amma sai dai abunda yakasa sani shine menene akalarsa da Sawwama? Menene Alakarta da ciwon Yareema da yana kallonta kaso Hamsin daga cikin ciwon da sukayi shekara tara suna magani bai kauba sai yanzu?
Mai martaba yaje ta dayan gefen ya zaune yace "Yareeema yaya jikin kana jina?
Ance kayi magana nima kayimin magana naji,
Yareema ya kalleshi sanna ya juyaga Sawwama yace "karki kulasu mugayrn mutanen ne zasu cutar dake,
Sawwama ta girgiza masa kai tace ba muggaye bane kuma bazaku cutarda kowa ba yan uwanka ne idan sunyi maka magana kana amsa musu,
Dagowa kansa yayi ya dubi Umma dasauri tazo tazauna kusa dashi tace "Eh eh yareema mu yan uwankane ba zamu cutarda kaiba, ni mahaifiyarka ce nima haifeki ka kalleni kayimin magana ko zanji dadi,
Advertisement
Kallon Sawwama yayi yanaso ta gaskanta masa zancen kai ta daga masa alamun eh dagaskene abunda Umma tafada,
Murmushi kawai yayiwa umma Mai martaba yace "yareema kallo ni nan ka gane ni waye?
Ya juya wajan Sawwama yace" wannan fa shima ba mugu bane?
Sawwama tace eh ba mugu bane, waye shi? Ya tambaya shiru tayi dan batasan menene alakarsa da mai martaba ba,
Mai martaba yace "ni kakanka ne nine mahaifin babanka, ina baban nawa yake? ya tambaya,
Allah yayi masa rasuwa, jijjiga kai kawai yayi hannunsa yana cikin nata firr yaki sakinta tagumi kawai tayi da dayan hannun tana kallon ikon Allah,
Ajiyar zuciya ya sauke yace "ashe bamasu cutarwa bane toh amma mutanneda suka kamaki ina suke?
Sawwama da batasan amsar tambayarsa ba tayi shiru kawai tana kallonsa duk cikinsu ma babu wanda yasan abunda yake nufi,
Mai martaba yace kuzo muje waje nagano wani abun dangane da abunda yake faruwa yanzu,
Yacewa Sawwama kiyi hakuri ki zauna anan yanzu zamu shigo kai kawai ta gyada musu Umma tace "kana ganin babu matsala idan anbarsu su kadai?
Yace "babu komai, fita dukansu sukayi yana kallon sun fice ya sake rike hannunta da karfi yace kiyi hakuri kinji bazan sake bari wani abun ya sameki ba bazan sake hannunki ba,
Sawwama kallonsa kawai takeyi tarasa abun cewa,
Suna fita Mai martaba ya dubesu yace su sallami duk yan aikin da suke ciki babu bata lokaci duk wasu masu hidima na sashin Umma aka sallamesu yarage saura Umma, ummi, Hajiya Aisha, ruma dashi kansa mai martaba,
Yadubi Umma yace "toh Alhamdulillhi inaga ciwon Yareema yakusa zuwa karshe dan yanzu zamu iya cewa hamsin cikin dari na matsalar takau tunda har yayi magana kuma alamu ya nuna yasan me yakeyi amma saidai wannan yarinyar ita kadaice acikin tunaninsa da rayuwarsa dole akwai wata alaka data taba hadasu akwai alaka kai karfin gaske a tsakanin wannan lamari,
Mun dade muna magani Allah bai kawo sauki ba ashe saukinsa yanaga gareta sai yanzu Allah ya turo manada ita,
Ba shakka sun san juna kafin wannan abun ya sameshi,
Hajiya tace Abba bana tunanin haka saboda har yanzu ko shekara ashrin da daya ina tunanin bata ida rufawa ba kaga lokacin da wannan abun yafaru kenan tana karamar yarinya kuma bata taba zuwa nan garinba koda sau daya zanyi mamaki idan akace sunsan juna,
Mai martaba Yace " yanzu kishiga kiji ta bakinta mikewa tayi dan cika umarnin mahaifinta,
Bayan tashiga kamar yanda tabarsu haka ta taddasu yana makale da ita,
Zama tayi gefen Sawwama ta dafata cikin kulawa tace Hafsatu kiyi hakuri da abunda yake faruwa,
Murmushi karfin Hali kawai Sawwama tayi Sannan tace "bbu komai,
Hajiya tace "Hafsa ko kin sanshi ne?
Sawwama tayi shiru sai kuma ta girgiza kai tace "bansanshiba Hajiya,
Amma kiyi tunani baki taba kallonsa wani wajeba?
Sawwama tace bantaba kallonsa ba nima saida nayi tunanin haka amma bantaba kallonsa ba,
Hajiya tace "ikon Allah kenan shi kadai yasan abunda yake kulle a acikin wannan lamari,
Zuww tayi ya sanarda mai martaba yanda sukayi,
Mai martaba yace "toh itama batada amsar wannan lamari yanzu haka amsar da zata warware wannan abu tana wajansa dan shikam tabbas yasanta ayanayinda yake yanzu bazamu samu amsaba,
Amma muci gaba da addu'a sannan ayita zamuci gabada magani bazamu tsayaba har muga yanda Allah zaiyi damu sannan basaina fada mukuba bayan mu da muke nan banaso wannan zance yafita ko'ina,
Yanzu kukoma ciki saboda zamanta ahaka zataji babu dadi har muyanke abunyi,
Mai martaba yatafi ransa cikeda jin dadin wannan hali dayaga jikannasa aciki,
Ahaka suka koma suka samesu yana nan rikeda ita ya dubi Sawwama a hankali ya rada mata yunwa nakeji,
Umma dake gefensa taji abunda yace "dasauri ta mike dakanta tayi dining ta debo masa abincin da aka jere musu danyin dinner ta daukoshi a plate jikjnta har rawa yakeyi ta zauna gefenaa tadauki spoon ta debi abincin sannan takai bakinsa,
Batareda gardama ba ya bude bakin ta zuba masa a hankali yake ci tana bashi harya koshi,
Bayan yagama yadubi Sawwama yace "bakyajin yunwa ne?
Murmushi kawai tayi bata bashi amsaba,
Hajiya tadubi Aysha da ruma tace "ku kawo mana abincin gabaki dayanmu nan sai muci, suka mike suka debo abincin Sawwama kasa ci tayi saida Hajuya tayi magana tadan tsakura kadan tabari muhammad dama shikam yana jikin hajiya ita ta bashi harya koshi,
Yasaba da ita sosai hakan yasa bai nemi zuwa wajan mamarsa ba,
Anan suka raba dare murna da farin ciki bai barsu sun iya rintsawa ba barinma umma datake ganin kamar idan tatafo zai sake komawa bacci,
Saida bacci ya daukeshi Sannan sawwama tasamu da zare hannunta, wani daki dake cikin sashin suka ta kwanta amma bata iya bacci ba,
Tunanin abunda yafaru dakuma wanda yake shirin faruwa kawai takeyi amma takasa gane komai domin kwakwalwarta ta tsaya cak tadaina wani kissafi,
Tashi tayi tadauro alwala tacigaba da Sallah akunnenta aka kira a sallatu har aka kira sallah tayi raka'atanil fijr sannan ta gabatarda sallar asubahi sai asannan bacci ya dauketa,
7:am Yareema ya tashesu yana neman yanda take aysha tazo ta tasheta, taje tasamu halinda suke ciki yana ganinta kuma sai ya lafa, breaskfast kanma ki yayi kowa yabashi sai ita zallah,
Haka suka wuni a zaune tagaji tazama ji takeyi kamar tafashe da kuka da ita dayace adakin tasan kuka zata saka tayi mai isarta,
Yanzuma taki magana domin tana kallon idan tafara kukane zai kwace mata,
Wai meyake shirin faruwa da itane? Menene hadinta da wannan yareeman da baya samun nutsuwa sai idan tana wajan?
Zuciyarta azalzalarta kawai takeyi ji take kamar tayi tsuntsu takoma gida dan bazata iya zama irin wannan zama maras makama da alkibila wanda sun kansu basusan me suke ciki ko wane hukunci zasu yanke ba."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial38 Chapters
Indistinct Instinct
They say Kaiser is more beast than man.They say he fought two armies at once by himself and forced them to retreat.They say he cavorts with witches and demons.They say he has a thousand lovers, each more beautiful and deadly than the last.They say the Night Goddess adores him, shrouding her beloved in her dark embrace.They say that blood still stains the Wyrm King's throne.They say, They say, They say... They say a lot of things. Rumors and myth surrounding Kaiser float through Gods' Nature like the wind through the trees, but sometimes, the truth is stranger than fiction. *Chapters will be released on Mondays to Patrons and here Saturday.* *Warning, this story has a slow start as I build up characters and the world. If you are looking for something that dives right into action then this is probably not the fiction for you. If you want a believable plot, good development, and character growth, then I welcome you.* *This work is under constant improvement. Volume 1 now finished.*
8 206 - In Serial31 Chapters
Zero Fate against the world (An Isekai Story)
This is a repost done by me the author. The original site where I post this is on Webnovel.I just wanted to see how my novel would go on another site if you liked it be sure to go to Webnovel since I am very active there. Although I can try to be just as active here.Now for the synopsis: Philip lived his life like any university student, he went to the campus, heard his teachers, made his notes, went home, studied, and played some games with the boys at night.Until one fateful day. It was the final class of the year, and he together with all of the people present in the room, were transported to another world.In a strange and unfamiliar world, everyone received powers and abilities including him, but with a twist, he didn't receive a class. Only a skill.They weren't there to kill a demon king, nor they were there to prevent a war. Although you could say they were there to cause one...How will he do with his strange skill? And how will his "friends" act?Let's find out because I am also curious!...Hey!No release schedule yet. I will post the chaps as I see fit since I am currently focusing on my other works. Go check them out!They are on the other side, although I can try to repost them here as well.I am here to say that I don't own the cover image, nor do I own the special abilities of the MC, you will see why.If you own any of these things and want me to take it down I will, but remember that currently, I am not receiving any money from this.
8 209 - In Serial7 Chapters
Journey of Infinite Steps
Science Fiction/ Low fantasy Iliad. Oliver just wanted a job that could keep his family fed, and himself sane. Was that so much to ask for? Apparently. As he instead ends up facing monsters and dodging his way to another world instead. Competent as he views himself figuring out how to reopen a portal back home by himself is defiantly above his knowledge base. Of coarse it would be vastly simpler if he could keep 'getting back home' as his primary goal. 'Staying alive' is unfortunately a far more immediate and relevant goal. I will post any content warnings on a Per Chapter basis. Divisive content will be as skip-able as I can reasonably manage Discord Link will be available for those interested in assisting editing/ coauthoring. Especially character writers/those willing to work out the math/ economies and world building even if only as a wall to bounce ideas off of.-----Full Synapsis contains serious spoilers----- Looking to take care of his family, Oliver finds himself flung into a faraway place. Try as he might, his Iliad will not be simple or peaceful as he'd like. Alas the slow and unending war of Chaos and Order has long memories and longer reach. If Oliver is to make his way back home it looks like He'll have to solve the universe one fight and mystery at a time. Especially as the Laws of Physics shift, often on a per world basis. Hopefully there is still a home to come back to.
8 148 - In Serial17 Chapters
Doctor in Immortal World
Han Cang, who used to follow the path of Daoism, and once belonged with the most remarkable warriors in upper class, an elite among his Daoist fellows, has now fallen into mortal world, namely, Earth. Since then, he enjoys his “retired life” quite a lot as being an alcohol retailer who owns a shop on the street, and gets used to live like a mortal, until a mysterious teen walks in his shop in another boring afternoon. The young girl who gets a pair of pink eyes comes for a little help that Han Cang should never respond, a transmigration to immortal world. Regardless of her inscrutable purposes, soon Han Cang finds his shop being under attack by people who possess the power from the other world to which he once belonged, and that leaves his perfectly peaceful ordinary life in ruin. To find out the truth and solve some pending issues left alone long ago, Han Cang returns to immortal world with the mysterious girl. This time, he will be known as a Doctor, to face the enemies whom he used to call brother and master, and even worse, the woman who once brought him peace and now hunts him to death. The great rebellion of one man against the entire universe of Dao has just begun…
8 75 - In Serial43 Chapters
Unchained
When a young witch is thrust beyond the veil and into an active revolution, she must fight both for her own survival against a secretive government agency bent on eradicating magic, and with her own morality as the lines between revolution and terrorism start to blur. After all, what wouldn't you do to save yourself? Unchained is a story about loyalty, revolution, and the sacrifices we make for both.
8 135 - In Serial11 Chapters
// Girls // The 1975
❝ 'cause they're just girls, breaking hearts. ❞ - The 1975, girlsfinished: may 1, 2014©girlwiththeredshoes 2014
8 96

