《ƘADDARAR RAYUWA》K page 90
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 90
Har Sawwama tagama takaba tana cikin damuwa sai dai damuwarta ta ragu bakaman kwanakin baya ba,
Mama tana zaunawa tayita mata nasiha harta kwantar matada hankali hakama Baba shima nasa wajan,
Hajiya kuwa akai-akai take zuwa dubata kowacce juma'a saitaje kamar yanda alokacin baya itama Sawwama ke zuwa mata duk jumu'a,
Yaranta suna debe mata kewa wasu lokutan kawai takan zaunene suyita suntiri tana kallonsu."
Duk wannan halinda Sawwama take ciki zamu iya cewa gara ita akan Dr domin Dr ta lalace gabaki daya ta fita kamanninta har takaiga rokon Allah ake mata yanzu ko zata cire abun aranta ta sake cikin hukuncin ubangiji aka fara kallon canji daga gareta saboda koda bazatayi maganaba zata zauna yanda mutane suke amma da kuwa sam batasan zama wajan koma waye."
Lokaci sai kara tafiya yakeyi har an yaye muhammad izuwa yanzu Sawwwama tagama warwarewa kawai sai da dan abunda baza'a rasaba wanda yake cikin zuciyarta wannan kuma dama sai ahankali wani tabon a zuciya baya taba gogewa,
Yanzu dakanta take zuwa gaida Hajiya duk jumu'a idan kuma bazata samu zuwaba saita aika mata yaran, yawuni zuwa yanma adawo dashi."
Yauma kamar kowacce jumu'a ta shirya ta nufi gidan Hajiya bayan tayi mata abubuwanda takeso a nau'in abinci Hajiya kullum takan tsinci kanta cikin farin ciki idan taga Sawwama da muhammad hardasu Hamdan da Hameeda ake zuwa yanda ta dauki muhammad haka tadauki Su hamdan ko abune bata taba siya ita kadai sai dai tasiya ta aika mus gabaki daya."
Bayan sun gaisa Hajiya tace "inataso nakira mahaifinki ko naje da kaina yabarki wannan karon mutafi wajan dangina tare sai mukai musu muhammad su ganshi, ko lokacin ta sukazo lokacin rasuwane hankalinmu gabaki daya baya kan hakan,
Naso muje amma Allah baiyiba sai ya aiko mana da wannan rashin amma yanzu tunda naga kin dan warware sai muje ki gansu wani satin in sha Allahu zamu tafi zanzo dakaina na roki mahaifinki,
Sawwama taji dadi sosai dan itama kanta zataso tadan warware ta bude idonta,
Sau daya tataba tafiya itace tafiyarsu da Abubakar taji dadin tafiyar sosai."
Sai dare kafin Hajiya ta sanya aka kaita gida itada kanta ta fara fadawa Baba zancen tafiya kamar yanda tayi tsammani kai tsaye ya amince,
Bayan nan Hajiya tazo dakanta tasake tambayar Baba yace mata ai bama saita zoba ta takirashi kawai itama Sawwwama yarta ce."
Ranar Lahadi suka shirya tafiya da cewar zasuyi sati daya can kafin sudawo,
Hajiya da Sawwama sai kuma Aysha da mai aikin hajiya guda daya suka tafi, jirgi sukabi a wasu yan tsirarrun mintuna suka isa garin motocine sukazo taransu daga airport kai tsaye cikin masarautar suka mufa duk yanda Sawwama taso kawarda kanta daga kallon masarautar saida takasa wata irin masarautace kayatacciya wacce zata dauki hankalin kowane irin mutumi dayake cikinta, mamamki Al'ajabine ya cikata dama akwai irin wannan gini a duniya? Ko tafiyar dasukayi honey moon bataga tsararrren waje irin haka ba ko'ina sai yalli yakeyi yanda kasan da gold aka ginata,
Advertisement
Amma sai dai wani abu guda daya yanayin mutanen cikin masarautar ya bambamta da ita kanta masarautar abunda hakan yake nufi shine,
Mutanen cikinta sam babu annuri ko walwala a tattare dasu ba waje daya ba saboda duk yanda suka wuce haka take kallon mutanen toh me yake faruwa?
Bata da amsar wannan tambayar har suka isa wani sashi mai kyawun gaske dan karamin flat ne ginin ya tsaru,
Dama ansanda zuwan Hajiya toh angayra wajan suna fitowa daga mota gabaki daya ma'aikatan wajan suka zube kasa suna kwasar gaisuwa Hajiya ta amsasu cikin fara'a sannan tayi musu umarni dasu mike sanin halinta ya sanya babu ja suka mike aka bude mata kofa suka shige ciki,
Komai na falon kamar sabo haka yake ya tsrau sosai dake bawani gajiya sukayiba tafiyar jirgi sai kawai suka zauna a cikin kankanin lokaci aka tanadar musu da abunuwanci dana sha kadan suka taba sannan Hajiya tace su tashi dukansu su shiga cikin gida gaisuwa, tana dauke da muhammad dake yasaba da ita sosai itakuma Sawwama suna tafe a Aisha suka fice Sawwama tadauka akafa zasu tafi tunda taji ance cikin gidan amma sai taga akasin haka mota suka shiga tasu daban ta Hajiya danan suka saida suka danyi tafiya kai yar nisa sannan suka isa Motar Hajiya na gaba suna biyeda ita abaya,
A sashin Hajiya Babba motar ta tsaya Aisha itakam dama tasan yanda zasu nufa domin duk zuwansu wajan Hajiya Babba suke fara nufa daga nan saisu wuce wajan sauran matan,
Har falon akayi musu iso itadai Sawwama ganin ikon Allah da al'ajabi kawai takeyi wai ace yan adam ne suke rayuwa a irin wannan gida wanda akayi zubinsa kamad da zinare komai na ciki gold ne hadda da adon sarauta da akayi toh da Gold colour akayi,
Sun dade zaune a falo kafin Hajiya Babba tafito cikeda kasaita ta zauna tana shan kamshi, Hajiya ta dubeta cikin girmamawa ta gaisheta ta amsa fuska babu annuri Aisha ta gaisheta ta amsa da lafiya,
Sawwama cikin sanyin jiki ta gaisheta Saboda taga yanayin yanda ta amsawa su Hajiya gaisuwa, batareda ta amsa ba ta kai kallonta ga Sawwama haka kawai gabanta yayi wata mummunan faduwa tsawon lokaci takasa dauke idanuwanta daga wajan Sawwama ita kanta batasan mai take tunani ko kallo gameda itaba balle kuma su Hajiya, jin shirun yasaka Hajiya ta dago kanta ta dubi Hajiya Babba sai taga Sawwama take kallo da wani irin yanayi wanda bazata iya kintatar ko wani iri bane juyawa tayi ga Sawwama taga kanta yana kasa tana Wasa da yattsun hannunta Saboda ta fahimci cewa uta Hajiyan take kallo gabaki daya jikinta yayi sanyi wani irin kunya da mutuwar jiki ya sauka mata jin yanda Hajiya Babba ta basarda gaisuwarta jikinta har rawa yakeyy kadan,
Hajiya ce ta katsa shirun da fadin matar Abubakar ce dayake bata taba zuwa ba kuma lokacin da kukaje ta'aziyya baku hadu da itaba shiyasa nazo da ita, Hajiya babba ta sauke ajiyar zuciyarda batasan na menene ba ta kauda kanta gefe batareda ta amsa ba,
Advertisement
Haka suka zauna tsawon lokaci sanann Hajiya tace "Hajiya Babba idan kin amince mana zamu shiga sauran wajajan mu mika gaisuwarmu, da hannu kawai tayi mata alamu Hajiya ta mike suma duka suka mike a sukwane suka fice,
Saida suka fita Aisha taja tsakai zatayi magana mahaifiyarta tayi mata ido sai tayi shiru
Saida taga ficewarsu Sannan tadawo daga idanuwanta daga kofan datake kallo,
Wacece wannan yarinya?
Matar Abubakar?
Toh menene atattare da ita da zaisa ganinta ya sanyata shiga wani yanayi da faduwar gaba?
Kai ina bama dalilinta bane faduwar gaban kawai dai yazo akan gaba ne amma wannan yarinyar batakai ta fadar matada gaba ba,
Saida suka shiga mota Hajiya itama ta jaa dan guntun tsaki wato matarnan batada kirki, kiri-kiri Sawwama ta gaidata haka taki amsawa ko dan muhammad dina batayiwa magana ba,
Nisawa tayi alokacinda suka iso dayan shashin, na daya matar mai martaba,
shiga sukayi suka gaidata ta amsa cikeda fara'a har tadan jasu da hira sai wasa take yiwa Muhammad,
Sun dan dauki lokaci ba kamar wajan Hajiya Babba ba sannan suka fito,
Shashin Hajiya suwaiba suka nufa itama tasaki fuska sun gaisa tanajan Muhammad da wasan kaka shi dake yanada kuiwa ma firr yaki zuwa wajanta,
bayan sun gama suka fita suna fita Hajiya suwaiba tabisu da Harara taja tsaki a fili tace nagode Allab da baiyiki a namiji ba da babu makawa sarautar kasarnan kece zakiyi Allah ya raka taki gona aje can akare agidan miji makira,
Sashin Umma suka nufa sai kuma Hajiya tadubi time tace "yanzu Abba (mai martaba) yadawo sashinsa mujuya can dannassn hirarmu anan bamai karewa bace idanna gama dashi saimu dawo nan,
Can shashin mai martaba suka nufa yayi farin ciki sosai na ganinsu yarike Muhammad yanata yimasa addu'a yana fadin Allah yasa kazama kamar mahaifinka Allah yajikan mahaifinka addu'a sosai yakeyi wanda saida ya sanya Sawwama ta zubarda hawaye,
Itama yayita sanya mata albarka sun dauki lokaci a wajan har aka kira Sallah mai martaba yafita zuwa masallaci sukuma suka wuce masaukinsu,
Suna shiga ciki aysha kamar wacce take jira tace Allah wannan Hajiya babbar tacika wulakanci Hajiya kiga yanda ta share gaisuwa anty hafsa, Hajiya tace "bata kyautaba nima banji dadin yanda tayi dinba,
amma kema kullum saina kwabeki nan fa ba kamar ko'ina bane ita masarauta daban take ba'a sakin baki sakkaka ayita magana kowa da kika ganshi anan naciki na ciki,
saida sukayi Sallah suka kara sanyawa cikinsu abinci Sannan suka fito zuwa wajan Ummaa,
A falo suka samesu su duka Umma da ummi sai ruma,
Bayan sun gaisa Hajiya ke tambayar jikin Yareema Umma tace "toh dasauki za'ace amma jiki yana nan jiya ayau,
Hajiya cikin damuwa ta daga tace "Allah ya Allah muna rokonka ka dawo mana da farij cikinmu kabawa wannan Bawa naka lafiya ya Allah muna rokonka ka waware wannna kulallen zare dake tattare da ciwon wannan bawa naka.
Su duka suka amsa da Amin,
Hajiya ta nisa sannan tace "tabbas Yareema shine farin ciki da walwalar wannan masarauta gabaki daya bamu dada tabbatarda hakaba saida jinya ta sameshi tsawon shekaru kenan amma har yanzu waji farin ciki yakasa ziyartar wannan masarauta gabaki daya zuciyoyi suna cikin kunci, Duhu ya sauko ya sauka a wannan masarauta Babu wanda yakejin dadinta Allah ka dubemu kabashi lafiya,
Hajiya ta matse kwalla sannan tacigaba da fadin lokacin yarima yanada lafiya kowani karshen wata sai nazo gida saboda babu yanda yakemin dadi kamar nan amma tunda wannan rashin lafiya ta sameshi bbu yanda yake bani kunci kamar nan sam banason zuwa,
Umma tayi murmushin yake tace "yareema naki ne ai banga wani abunda yareema yakeso da girmamawa fiyeda keba,
Yakan cemin mahaifinsa yake kallo idan yana ganinki,
Hajiya tace ko lokacinda wannan abun zai faru saida ya kirani cewa yana hanya zaizo inata shirij tarbansa jin shiru bai isoba ya sanya na kira wayarsa akashe kema na kiraki kika shaidamin kema yayi miki Sallama akan zai taho wajena,
Umma tace "haka wannan zancen yake amma kawai kuma sai gashi yadawo baijeba yafasa zuwa tun daga lokacin nagane baya cikin hayyacinsa yace zai kwanta yanajin bacci tunda yayi wannan baccin har yanzu bai sake samun hankalinsa ba yanzu haka sai yayi kwanaki yana bacci toh mu harma munfi ganin masa saukin yayi baccin akan yafarka ta karashe hawaye yana zubo mata a kumatunta,
Hajiya tace "wannan lamari akwai kulalliya a cikinta mudai Allah muke roko ya warware mana,
Suduka suka amsa da amin,
Umma tajawo hannun Muhammad tana fadin yaronnan sak mahaifinsa bbu abunda yabaro nasa,
Hajiya tace " eh kamar anyi kaki an tofa Abubakar ne sak Umma tace "Allah yajikansa yayi masa rahma suka amsa da amin tadubi Sawwama tace "wannan ce matarsa ko? Naganta lokacin rasuwa dake a tsattsaye ne bazan iya ganetaba, Hajiya tace "eh itace, Allah sarki sannu mijin yatafi yabarki da yarinta, mutuwar miji babu dadi na taba naji sai hakuri, kasa Sawwama tayi da kanta, tanaji suna kara famo mata ciwon dake cikin zuciyarta,
Sun dauki tsawon lokaci suna hira sannna aka kira magrib anan sukayi Sallah har zuwa isha'i
Saida dare yaraba sannan suka koma masaukinsu washe gari Sawwama badan ranta yasoba suka sake komawa gaida Hajiya babba kamar yanda sukayi jiya haka yauma sukayi saidai yau basubi wajan mai martaba ba saboda yanada ganawa da mutanensa sai yamma saje wajansa,
Wajan Umma suka nufa kamar jiya suka yada zango a wajan akai-akai umma ke shiga taduba yarima saboda jiya da dare jikinnasa yatashi,
Suna zaune Aysha ta mike tace "umma zan iya shiga naduba yaya Yareema?
Hajiya tace "bari maje tare banason ganin yareema cikin wannan yanayin yana dagamin hankalina,
Umma tace muje harsun fara tafiya Hajiya tajuyo tadubi Sawwama tace "Anty Hafsa taho mudubashi kyayi masa addu'a ba'asan addu'arda zatayi tasiri aciki ba, mikewa Sawwama tayi cineda faduwar gabanda batasan dalilinta ba a hankali take tafiya harta riskesu suka nufi dakinda yake kwance."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial401 Chapters
Class: Mash
In a world full of magic and power, where strength is defined by classes and levels. Follow Mash, a young boy who gets to experience the wonders of the world, from receiving his first class to realizing his dreams, and all the little progress in-between. Although things don’t go as he predicted. His first class defined him as something he was not, yet it offered him a new opportunity. Only through gaining experience and levels can he even begin to reach his dreams, whatever they may be. After having his first real fight, Mash catches a glimpse into the profound wrongness in his world. In this moment of revelation, Mash’s life takes a new path, one he will have to carve for himself. A path that was not for knights, heroes, or kings, instead one for gods, of power beyond even his own understanding. Participant in the Royal Road Writathon challenge. I upload everyday at 12:00pm cst. P.S I am working on rewriting the first couple of chapters, expect those to release slowly over the next week or so. I will keep the above schedule for the normal chapters. Thanks for reading. I will mark them with edited, when done. The story itself won't change much, i will just be adding clarification and editing it so it matches the form of the later chapters.
8 792 - In Serial22 Chapters
The Big Yoink: A Smol Detective Story
This is another fanfic set in the universe of They Are Smol, a delightful series of stories which you should totally go read right now if you haven’t. It’s a sequel to my own The Smol Detective. In this story, Oscar Williams and his adopted alien family have to determine the guilt or innocence of another human and her two alien friends. The trio stands accused of stealing a sacred relic, and if it isn’t found soon an ancient religious cold war could turn very hot indeed… Formal Disclaimer Type Thing: I do not take credit for the original setting, this story is set in an alternate version of the 'They are Smol' universe, written by the one, the only u/tinyprancinghorse. TPH takes many forms and is known by many names. He is like Nyarlathotep, only smaller and cuter and more prancey. TPH also has a Website should you require more Smol Shenanigans in your life. Which you do, so get over there and read it. The cover art for this sequel again comes courtesy of the mighty Akella, and they deserve lots of headpats from giant aliens because they are awesome.
8 109 - In Serial26 Chapters
Existara
Desperate times call for desperate measures. The Rebirth is only months away and a victory is a must. At all cost. To stop the reoccurring nightmare that has tormented the land of Existara for centuries… For the first time in the History of the Concord – there is a chance for the impossible to happen. The question is – can they make it in time? Or will one man’s ambition be the executor that condemns the world into eternal chaos…
8 153 - In Serial7 Chapters
The Whispering Blade
In the blink of an eye, Ezra Nyx’s life changes forever. As an ordinary college student that only wants to get by, he he doesn't have high expectations of his future, but one night, he experiences something life-changing. He now knows something that no one else does, humanity is not alone. Unknown forces are finding their way to Earth, making it their little playground. Follow Ezra’s journey as he navigates through all the chaos and becomes more than he ever thought he could be.
8 203 - In Serial54 Chapters
Anna's Dream
This web novel is about Anna the only child of the enigmatic being known as The Dreamer. Join her as she travels a world filled with magic and wonders. She's not the chosen one, she has no destiny and there's no telling what she's going to do next, other than look for some cupcakes that is. This is the first thing I've written I hope you all enjoy reading about Anna as much as I enjoy writing about her. I plan on releasing this once a week on Fridays at 10 am EST
8 96 - In Serial50 Chapters
Sinbad: High King of the Seas
{Completed}Annalise was an infant when she was stolen from her parents at the age of three she managed to escape from a man who couldn't catch her. She winds up in a village where she meets a young boy around her age. He was kind and gentle to her and as they grew older, he became her best friend. She watched by as he became a strong willed man who captured seven dungeons. Though he became important, he always had time for Annalise, who remained by his side because he always found time to protect her.
8 201

