《ƘADDARAR RAYUWA》K page 83
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 83
Sawwama sai kashe wayarta tayi saboda yanda Dr take kiranta tana fada mata maganganu harda wasu ikirari takeyi na lahantata,
Bata fadawa kowaba kuma kos sau daya bata taba ramawa ba,
Saukinta daya ba'agidanta takeba da batasan abunda zatayi mata ba anan kuma ko hauka takeyi bata isa ta ce zataje ta yimata wani abunba,
Daga karshe ta kunna wayanta ta kulle duk wasu lambobin Dr daga shigowar kira izuwa sako, har akakfafen sada zumunta saida ta rufeta kafun tasamu lafiya."
A gidan ake yiwa Sawwama jego tasamu gyara yanda ya kamata Hajiya tace "sai tayi arba'in zata koma gidanta yaronta sai girma yakeyi gwanin sha'awa babansa kullum yana kan hanyar zuwa dubasu,
Dr tayi rikicinta harta gaji shidai Abubakar hakuri kawai yake bata damuwarsa kawai ta kwantarda hankalinta dan bayaso zafin ya hade mata biyu koda yaushe yana tare da ita idan tana asibiti kuma kira akai-akai yanzu bawani birgeta yakeyi ba dan saudayawa abunuwan dayakeyi haushi suke bata shikuma iya kokarin kyautatawa yanayi mata.
Bayan Sawwama tayi arba'in Hajiya dakanta tafara yimata shirun komawa aka saka ranar komawa,
Ana saura 1week takoma gidan mijinta Abubakar yazo bayan ta agisheshi ya dauki yaron yana masa wasa sannan yadubeta yace" inaso ki shirya zaki rakani anguwa ki tambayi Hajiya duk daida narigada nafada mata,
Sawwama batayi tace toh taje ta tambayi hajiya bata hanata ba tana dawowa Hijab kawai tasaka yadauki babyn duka fice,
Waani guda taga sun shiga mai masifar kyau flat ne ginin ya tsari sosai Sawwama a zatonta gidan wasu yan uwansa sukazo amma saitaga babu kowa cikin gidan,
Saida yashiga da ita ko'ina acikin gidan ya nuna mata komai ya tsaru yayi kyau bayan sun fito ya zauna afalo itama tabishi ta zauna yace "gidan yayi kyau?
Yayi kyau sosai iska yafurzar yace "naji dadi da yayi miki kyau dama ance wanda kayi dominsa ya yaba cikin rashin fahimta Sawwama tace "banganeba,
Wannan gidan zamu dawo da zama in sha Allahu,
Wanda muke zaune fa?
Kkn manta yazama naki? Alhaji yabaki takardunsu nakine halak, nikuam bazan zauna agidan mataba yafadi cikeda zolaya,
Murmushi tayi tace "Allah ni da ba'a canja ba mu zauna a wancan ya ishemu rayuwa, Abubakar yace anrigada angama amma ga wata shawara, ehem inajinka, mai zai hana kibawa su Baba wancan gidan sudawo cikinsa dazama? Inaga kaman hakan yayi,
Advertisement
Sawwama tace shawararka tayi amma baba bansan ko zai amince ba,
In sha Allahu zai amince ai kece kikayi masa kyautar zai karbeta hannu bibbiyu, taji dadi sosai tace toh sai muyi musu magana tare,
Duk lokacin da kika shirya kawai kiyimin magana zamuje in sha Allahu zasu amince, Allah yayarda tafadi yace "amin basu dadeba suka koma,
Bayan sun koma take fadawa hajiya yanda sukayi, Hajiya tace "toh Alhamdulillahi abu yayi kyau abubakar yayi tunani nima na dade da kissima hakan araina ko alhaji yacemin dana gidan yanason yabawa mahaifanki ne baisan yanda zasu dauki lamarinba kasancewar yaga su bamasusan abun hannun wani bane shine yayi amfani da damar yabaki dan yasan dole wata rana zai dawo hannunki,
Godiya sosai Sawwama tayiwa Hajiya gana mamakin hali na karamci irinnasu."
Ana gobe zasu koma Hajiya take cewa Sawwama Naso ace kafin ki koma munje wajan yan uwana amma Allah baiyiba in sha Allahu idan zantafi zanje dake ki gansu, dayawansu basuzo sunaba saboda wata jarabawa da Allah ya saukar mana ya kasance kusan kowannemu yana cikin damuwa muda muke nesa-nesa nema abun yake zuwa mana da sauki amma sukda suke can kowane lokaci hankalinsu atashe yake wata rana in sha Allahu zan tafi dake cikin ahlina,
Sawwama acikin ranta tana tunanin yanzu haka Hajiya har akwai wani abunda yake damunta?
Wato ita matsala idanba mutum ba fito yafada ba ba lallai asan yana ciki ba, afili tace Allah ya yaye gabaki daya matslaar da take cikin ahlinku yadawo muku da farin cikinku,
Hajiya ta amsa da amin."
Sunyi araba'in da 10days Sawwama takoma gidanta dakyar Abubakar ya fadawa Dr zai je gidan Sawwama saboda tausayi take bashi yasan wasu abubuwan kawai tana daurewa ne shiyasa ta zabi janye jikinta daga nasa,
Ko kulashi batayiba yace Dr kina jina? Tace najika saime? Idan zaka tafin saika fadamin auren cin amanane babu yanda zaije,
Abubakar da jiki a sanyaye yatafi can amma ganin Sawwama sai ya mantar masa da damuwar daya debo,
Wanka yayi sannan yafito falo wajanta ya samu tagama shirya yaron har yayi bacci, zama yayi kujerarda Sawwama take yana fadin yau dai Allah yayi Hajiya tabani matata,
Dama Hajiya bata rike maka mataba, uhmm kekam ai komai hajiya tayi baki taba kallo, tayaya za'ayi na kalla? Bayan ita uwace, jawota jikinsa yayi ya sunbaci hanci ta yace kema ai uwace,
Bakinsa ta sumbata tace kaikuma ubane, zaro ido yayi yace "Hafsa kin daina jin kunayata ne?
Advertisement
Mikewa tayi da yaronta tana dariya tashige daki binta yayi abaya ta kwantar da yaron a gadonsa tayi masa addu'a, zaunawa yayi bakin gado yace "idan angama da baby azo ajida baban yaro yana jira,
Nufowa gadon tayi ta kwanta taja bargo tana fadin "bacci nakeji janye bargon yayi yace wane mutum,
Dariya Sawwama tayi tace "mutum kuwa shi ya isa, karasa hawa gadon yayi ya jawota jikinsa ya mirgina gabaki daya ya zamana shine asama ya sakar mata nauyi wata yar kara tayi ya saka dariya yana fadij zaki mai-maita abunda kika fada yanzu, turo baki tayi tace ni mai nace?
Lips dinta ya ciza a hankali yasake yace ina jinki maimaita,
girgiza kai tafara yi tana fadin Allah ban isaba kayi hakuri
No bazanyiba naga alamu kwana biyu da kikayi baki shiga hannuna bane bakinki ya bude,
Ta bude baki zatayi magana ya hade bakinsu waje daya yana kissing dinta,
Kamar yanda yafada hakanne tafaru tabbas tayi bayani."
Zamane mai cikeda dadi kulawa soyayya da hakuri da jina sukeyi kowannesu yana kokarin farantawa dan uwansa."
Dr har gida tazo tayiwa Sawwama tass kafin tahuce tace kuma har abada ko yanda take idan Sawwama tataka saita yimata illah,
Itadai Sawwama kala batace ba har tagama abunda zatayi tafice koda Abubakar yasan da zuwannata ma hakuri kawai ya bata,m."
Dafarko da takaiwa su Baba takardun gidan kin karba sukayi saida tayita rokonsu kafin suka karba amma har yanzu basu dawoba tukunna suna kan shawari,
Yau Sawwama agida zata wuni shida kansa yakaita dama sunyida Halima akan dukansu zauje gida sun samu baba yatafi kasuwa amma da rana yadawo cin abinci da Sawwama da halima sukayita rokonsa kafin yayarda da cewa zasu koma amma sai bayan sati biyu."
Wasu canje-canje Dr takeji ajikinta amma bata kawo komai aranta ba tabar hakan akan staress dinda take ciki dan har yanzu bawai tagama hucewa da Abubakar da Sawwama bane da aminta dasu subci amanarta."
Sawwama idan ta zauna saida yawa takanyi tunani bata taba tunanin farin cikin da Sadam yabata abaya idan tabarshi zata samu kwatankwacin hakanba amma gai gashi dake ubangiji mai rahama ne yabada wani mjin mai kula da nuna soyayya kuma mahaifansa na sonta kamar yarda suka haifa a cikinsu, a rayuwar da take ciki a yanzu batada wata matsala sai dai ta godewa ubangiji mai kyauta da kari, ta haduda Kaddara dayawa a rayuwarta amma kowacce takanzo mata kala biyune wani barin ta zame mata mai kyau wani barin kuma tazame mata mummuna, ta rigada ta yarda cewa dama ita rayuwa ba koda yaushe bane zaka kasance cikin farin ciki."
Bayan sati biyu Sawwama da yan uwan Baba suka rakasu gidansu suka tare, kowa sai sam barka yakeyi, Baba a rayuwarsa bai taba tunanin zai shiga gida irin wannan bama ya mallaka ba amma yau sai Gashi Allah ya mallaka masa ta dalilin yayansa mata da ake gani basuda wani amfani,
Manyan Shaguna Sawwama ta budewa Baba da kudaden da suke hannunta a kankanin lokaci Allah yasawa kasuwancin albarka abu sai fadada yakeyi."
Zazzabi Dr takeyi Sama-sama Abubakar ya kwana gidan Sawwama amma yabiyo ya dubata ganinta a kwance yasa hankalinsa ya tashi yace tatashi yakaita asibiti, tace yaje meeting dinsa kawai zataje bawani ciwo serious bane kawai stress ne tanada patients da zata gani idan tagama dubasu itama zataje frnd nata ta dubata, flashing na kiss yayi mata akan lips dinta ya rumgumeta ajikinsa yace dan Allah kije asibiti kinji? Inasonki sosai,
Shiru tayi saboda yanzu koda yace yana sonta bata iya maida masa,
Yayi mata sallama yafice saida yakara bi tagidan Sawwama yace mata ta shirya masa abinci kafin yadawo idan yadawo kuma zasuje su gaida Dr idan babu damuwa batajin dadi Sawwama tace Allah yakaimu babu komai adawo lafiya,
Rumgumeta yayi yace "Allah yayi miki albarka ta amsa da amin, yafita domin halartar meeting dinda yake dashi."
Dr bayan tagama ganin patients dinda take dasu tawuce wajan kawarta ta dubata gwajin farko ya nuna tana dauke da ciki na wata hudu,
Dr sai takejin abun kamar al'amara tace tayaya za'ace ina daukeda ciki har wata hudu bayan banda yan wash kananun alamu banajin komai tayaya za'ayi ahak antabayi kuwa? Kiduba result din dakyau kigani, mika mata tayi tace gashi ke kije kiyita dubawa amma ciki kam kina dauke dashi."
Alokacin Dr tafara kiran Abubakar yana cikin meeting bai daukaba hakan yasa ta ajiye masa sako akan idan ya fito ya kirata."
Yana fitowa yaci karo da sakonta alokacin ya kirata babu yanda baiyi ta fada masa ba tace sai yazo gida yanda yajita da muran ya tabbatar wani abun farin cikine yasamu."
Vote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial63 Chapters
The Dungeon Hive
One thing I noticed about most dungeon stories is that most races mistakenly believe that dungeons have a hive-mind and I go, “That make sense.” Considering the various powers and how big dungeons can get, wouldn’t it make more sense for them to have a hive-mind? So this is it; my take of the world’s first dungeon and the hive that controls it. Watch as it stumbles, fall, survive, strive and…procreate? Watch as it changed the world of Ioplon…for better and for worse. -------------------------------------------------------------------------------------------------------------- For edited version of the story, the full trilogy (Book_1: Fantasy Begins, Book_2: Dungeon Flames, Book_3: Spread of the Dungeons) are now available on Amazon. Please take a look, and leave a rating. Thanks
8 299 - In Serial76 Chapters
The Purple Jade Palace: The Hummingbird's Plan
When Teal helps an injured soldier by hand-delivering a scroll to the Emperor, he is offered a place in the Emperor's harem for his courage and efforts. Teal is of Lombock descent however, a cannibalistic race of beings who were believed to have died out. Having grown up on the outskirts of the Empire, Teal finds adjusting to life as the Emperor's concubine difficult and as he begins to learn about his origins, he also stumbles on old dark secrets lurking in the palace. Traitorous spies, unfinished disputes, and old enemies from neighboring kingdoms hide in plain sight within the palace walls, all threatening to ignite Teal's true identity and with it, cause the return of a race of beings who once controlled the world with horrific consequences. The only way out? A possible alliance with a defiant and strong-willed princess and a group of magical assassins who wish to control the world as they see fit. Please don't be shy. Feel free to comment if you enjoy the story. Feedback is always welcome! Artwork for cover purchased from Canstock: by 'AtelierSommerland' I'm currently working on Book Two. I won't post book two until I have a decent amount written. Current word count on book two is 43,000 so you know I am working on it (19/5/22)
8 218 - In Serial6 Chapters
Just Your Average Isekai
a guy gets hit by truck-kun and is reincarnated into another world. after learning why he was summoned he said "No" and got thrown out. now he has to figure out how to live without the help of others.
8 54 - In Serial11 Chapters
Purple Lipstick Designer Club Vol. 1: Let's Be Cute Maids!
Purple and Teal are roomates, best friends, college students, magical girls, maids, and able to summon psuedo-demonic entitites to fight on their behalf. Life as a 20-something is hard enough, but when you come home to find a blood-covered body on your white carpet... well, that's just the last straw, isn't it? Featuring a story by Maru and artwork by Vanilla, Purple Lipstick Designer Club was a planned start in a long-running series. Originally published in 2017 for Comic Fiesta. Check out the illustrated version at Maru's itch.io!
8 90 - In Serial38 Chapters
Olympus: The Agency
Hundreds of years in the future, a government-backed black ops group clones people who died in the past to form a group of deniable assets to perform missions. Stripped of names, these people are granted codes to live by instead. Agent Zeus leads this group of dead people to survive in a universe they do not understand. But as time goes on, they must make difficult decisions just to get to the next peril.Sometimes death is preferred.
8 151 - In Serial3 Chapters
Kpop smuts
These are sexual and shouldn't be read by younger audiences....
8 84

