《ƘADDARAR RAYUWA》K page 81
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 81
Sallama Hajiya tayi tashigo da sanyayyan jiki da zauna Sawwama tayi saurin janye jikinta daga nasa, Hajiya tace "Abubakar me nakeji haka?
Nakasa fahimta ko zaka iyamun bayani sunkuyarda kai yayi Hajiya tace "kai nake sauraro."
Cikin tsaron faɗa irinna hajiya ya zayyano mata abunda yafaru kafin auren,
Da mamaki Hajiya ta dubeshi sannan tace "Lallai na yarda Abubakar bakada hankali wato kai duk wani abunda matarka tace shi kake biye mata, kai matsayinka na mai hankali bazaka yi tunani ba kafin?
Sawwama kuwa jikinta har rawa yakeyi dan batasan yanda Hajiya zata ɗauki lamarin ba,
Hajiya tacigaba da faɗin toh wallhy yanzu-yanzu ka tsgunna ka nemi gafarar yarinyarnan nan dan kun cutar da ita daga kai har matarka, kunyi amfani da rashin lafiyan ƴar uwarta sun sanya ta amince muku bada son ranta ba, wato dayake su basuda gata basuda komai shiyasa zaku zalince ta toh wallhy baku isaba wannan aure anyishi har abada kenan mutuwa ce kawai zata raba, ayanzu haka idan takaiku ƙara wajan Allah sai Allah ya saka mata dan wannan abunda kuka aikata zalinci ne, tashi hajiya tayi tazauna kusada Sawwama tace "Hafsatu kiyi haƙurin wannan abunda suka aikata miki wallhy bada hannun mu ba bamuda masaniya akan hakan ko Alhaji daya sani daya cimusu ƙaniya, Yanzu dawane ido zamu kalli mahaifanki? Dole mu nemi gafararsu,
ki kwantarda hankalinki kidaina fargabar mutuwar aurenki dan babu wani abunda ya'isa yasamu aurenki ninan zan tsaya miki Allah ya tsaya mana gabaki ɗaya matarsa kuwa babu wani abunda ta'isa tayi ni godiya ma yakamata nayi mata dan tasamo matarda ta dace da Abubakar ta haɗasu sam banyi baƙin ciki da wannan abuba ta hanyarda suka nemi aurenne kawai banji daɗinsa ba amma in sha Allahu wannan kuskuren ya gyaru nayi tunani cewa ko Alhaji bazan sanarwa ba dan da Abubakar da matarsa gabaki ɗaya zasu shiga matsala kuma suna saane rashin kirki ne kawai yasa suka aikata hakan amma yakamata ya sani dan yanemi yafiya awajan iyayenki, ba'a kyauta musu ba hakika,
Niba fata nake makaba amma bazaka samu mace kamar hafsa ba, yarinyace ƙarama amma tasan zamantakewa tasan girman kowa koda kuwa ƙaramin yarone sam batada wata matsala muma kanmu munajin daɗin zamada ita bare kai wanda kake aurenta tana maka biyayya sannan kuma tana baka girmanka, Ko bayan raina Abubakar har indai ka saki hafsa toh ban yafe makaba,
Advertisement
Abubakar yayi saurin faɗin "kiyi haƙuri hajiya amma nima araina banida niyyar sakinnata dan ban aureta da wannna niyyar ba amma dukda haka nasan nayi kuskure in sha Allahu bazan sake aikata koda makamancin hakanba,
Kuma zanyi mata riƙo na gaskiya Hajiya naji daɗin zama da ita da gaske yau bazance miki ga wani halinda takeyi wanda banaso ba,
Hajiya tace zaka faɗa ai dan anty Hafsa mutumce tasan mutumci ainun, Jinta nakeyi kamar Aisha ni bana iya nuna bambamci tsakanin kuda matanku ko Sajida halinta yaja mata wallhy bantaba ƙin Sajida ba sai halayanta na wulaƙanta dangin miji da bazan iya ɗaukansu ba,
amma ita a yanzu gani takeyi saboda bata haihu bane bama sonta ni na'isa inja da hukuncin ubangiji ne? Bazan taɓa kinta ta wannan dalilin ba ko muna da Allah yabamu ba wayonmu ba ba dabararmu ba idan shekara dubu zakuyi idan bata haihuba bazan kitaba banda mugun hali irinnata, Kuma ko yau tagyara halinta ashirye nake da na manta komai,
Abubakar baice komaiba yayi shiru kawai yana sauraron Hajiya dan idan tafara magana akan Sajida bada wuri take dainawa ba itakuwa Sawwama kanta yana ƙasa hawaye kawai ke zarya a kumatunta kuka takeso tayi na godiyar ubangiji daya bata irin wannan miji da danginsa yanda hajiya taɗauki wannan zancen da zafi ko iyayenta basu ɗauka hakaba, soyayya iya soyayya baiwar Allahn nna tanuna mata sai dai tayi addu'a Allah itama yabata ikon kyautata mata,
Miƙewa Hajiya tayi tace gobe kashirya zuwa bawa mahaifanta haƙuri tafice, juyawa yayi ga Sawwama yasake riƙota ajikinsa ya rumgune sai alokacin tasamu damar yin kuka bubbuga bayanta yayi yana rarrashinsa saida tayi shiru sannan yaɗago fuskarta yace "Hafsa karki riƙi Dr da wtaa manufa aranki batada matsala sai dai rashin fahimta zanyi duk yanda zanyi naga kun samu daidaito atsakaninku, a halin yanzu dole sai munyi haƙuri da abubuwanda zatayi saboda kinga ita akayiwa rashin kyautatawa a zahiri duk kuwa da cewa a baɗini kece wacce ba'a kyautawa ba, amma haka zamu jure komai zai biyo baya dagani harke,
Murmushi Sawwama tayi sannan tace "baban unborn idan ban godewa Dr ba bazan kullaceta ba farin cikin da nake tunanin ya gushemin itace wacce tadawomin dashi ta dalilinka, banaji akwai abunda zaisa na ƙullaceta kuma in sha Allahu komai zai faru bazanyi reacting akaiba har komai yalafa,
kiss yayi mata agoshi cikeda son sunanda Sawwama take kiransa "baban unborn afili yafurta "nagode Hafsa nagode da kika kasance cikin rayuwata,
Ɗagota yayi yana kallon cikin idanuwanta yace "toh baki sanar dani irin sonda kikemin ba, ko yanzu kawai ki gwadamin a aikace, zaro ido Sawwama tayi tace"agidan Hajiyan? Babu ruwana, hajiya fa tatafi shashin alhaji Aisha kuwa nasan yanzu tacanja falo dan hira zatayi koda nazo naga saurayinta ya iso kawaidai bata fita bane saita ja masa ajinku irinna mata,
Advertisement
Tureshi Sawwama tayi tace "nikam dai A'a kaga girman cikina fa, toh wai har yaushe zanyita jirane? Kinsafa tunda hajiya tadawo dake gidannan bamu samu keɓewa ba gashi kina haihuwa nasan zasuce sai kinyi arba'in bazan iya jiraba gaskita,
Wani abu ya tuno cikin ransa sai kuma shi kaɗansa yace "shikenan saida yaraba dare yana wajanta sannan yatafi da nufin sai washe gari."
Washe gari da 11:00am Abubakar yashigo gidan sanye da farin kaya ya matukar yimasa kyau sai kamshi yake zubawa fuska cikeda fara'a kamar wani sabon ango,
ya samesu duka zaune a falo Hajiya da Sawwama, ta zauna kafafunta a mike wata dattijuwar mata tana mammatsa mata kafafunta,
Zaunawa yayi yana shaigeda Hajiya ta amsa cikin fara'a Sawwama ta gaidashi ya amsa sannan yace "Hajiya kafar ciwo takeyi ake matsa mata?
Hajiya tace "toh ciwon kenan za'ace kumbura sukeyi kuma ba'aso su kumbura din shiyasa ake mammatsawa danta samu sudan kwanta, cikin tausayawa ya kallo Sawwama yace "sannu murmushi kawai tayi masa yadubi Hajiya yace "Hajiya nazone mutafi da ita saita shirya muje mubasu hakuri, Hajiya tace A'a abubakar kaje abunka kana ganin halinda take ciki kace ahaka zaka dauketa kutafi?
Kaje kai kadai kabasu hakuri ai kai kayi musu laifi ba itaba,
Hajiya dan Allah kibari muje tare wallhy bazan iya zuwa ni kadai ba kuma ganinta zaisa suji zuciyarsu ta sanyaya, Hajiya tace "nidai wallhy Abubakar danka matsane amma da kabarta kaje kai kadai,
Kuje amma karka dade kadawo da ita, murmushi yaui yace "daga can nan zamuyo hajiya,
Hajiya tace tashi ki shirya anty hafsa mikewa Sawwama tayi ta sako hijab Hajiya tabada tsaraba aka kai mota,
Sawwama na fitowa hajiya tace "toh maza zo ka taimaka mata kuma kutafi a hankali, riketa yayi har zuwa mota yabude saida tashiga sannan yajuya shina yashiga mota,
Ahankali yake tafiya a motar cikeda nishadi cike duka a zuciyoyinsu,
Baya jinawa saiya juya ya kalleta daukeda murmushi akan fuskarsa,
Abakin kofa ya tsaya itakuma ta karasa ciki tayiwa mama magana sannan tadawo tayi masa iso,
Yashiga mama ta shinfida masa tabarma ya zauna ya gaidata ta amsa cikeda fara'a,
Sawwama tace "mama yazo zaiyi magana dakune kuma baba yana kasuwa ko za'a kirashi yadawo?
Mama jiki a sanyaye tabugawa baba waya, lokaci kalilan ya iso dan hankalinsa a tashe yake tunaninsa ko har anyi sakinne,
Bayan sun gaisa yafara da namen afuwarsu akan abunda yafaru sannan yayi musu alqawarin mutuwace kawai zata raba aurensa da Sawwama,
Shiru Mama da baba sukayi kowanne zuciya cikeda farin ciki Baba ne yayi karfin halin fadin baka tunanin idan anyi hakan ba'ayiwa matarka adalci ba?
Alkawari mukayi da ita, murmushi yayi yace baba wacce akayiwa rashin adalci itace Sawwama kuma ina fata Allah yabani ikon gyara kuskuren baya, banajin akwai wani abunda Sajida zatayi yanzu dazaisa na rabuda ita kuma ni dama ban aureta da niyyar sakinta ba,
Kuyi mana addu'a in sha Allahu wannan aure alkahirine a cikinsa,
Fara'ar fuskar baba takasa boyuwa cikeda annashuwa yake fadin "Toh Alhamdulillahi Allah yasa hakanne mafi alkahiri Allah yabaku zuri'a dayyiba godiya baba yayi masa Abubakar yace nine wanda zan gode muku baba hakika ku mutane ne masu hakuri da sanyin hali yanzu nasake fahimtar wacecce hafsa d ahlinta baki daya kuba irin ahlin da za'a samu kuma ayi watsi dashi bane.
Baba yakoma kasuwa cikeda farin ciki sai yakeji kamar amafarki daga karshe dai auran yarsa bazai mutuba yana addu'a duk wani abunda zai biyo baya yakasance alkhairine,
Mama taso yabar mata Sawwama amma haka yanuna yanason tafiya da ita mama bata tsawwalaba tabarshi yatafi da ita,
Ga mamakin Sawwaama gidansu yawuce ba gidan hajiya ba, Sawwama tace "baban unborn naga hajiya tace karmu dade?
Ba dadewa zamuyiba yanzu zamu tafi yafadi yana bude mata kofa,
Kai tsaye daki yawuce da ita Sawwama tagane abunda yake nufi kuka take shirin yi dan taga halinda take ciki baima dameshi ba,
Cikin muryar kuka tace "hajiya fa tace kamaidani gida kuma kana ganin halinda nake ciki zaka yiyo dani nan ni gaskiya mutafi gida, kalan tausayi yayi yace "Toh yaya kikeso nayi hafsa? Jiyafa kikacemin hajiya da Aisha na gida yanzu ina suke?
Bawani dadewa zanyiba dan Allah karkice A'a
Badan rai yasoba Sawwama ta sakar masa jiki amma tun kafin subar gidan mararta tafara ciwo daurewa kawia take har suka isa gidan Hajiya,
Da dare haka abu ya tsananta kasa daurewa tayi saida ta sanarawa matarda take kwana da ita, a daren takira hajiya dama Hajiya tunda Sawwama tazo gidan a ankare take tana kallon kira kuwa tace haihuwa tatashi, kai tsaye asibiti suka wuce daga Hajiya har Aisha sai aka kira Abubakar aka shaida masa amma su sunwuce saiya bisu abaya."
Yau mantawa nayi daku gabaki daya😅😅
Sai yanzu natuna daku baby yawa kuyi hakuri in sha Allahu gobe za'ayi mai yawa."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial419 Chapters
The Supreme Sovereign System
Alfonso was a historian of earth who suddenly appear in the body of Alfonso Lockheart, a fallen prince that is the Lord of a formal city known as the wasteland valley, with infertile land and losing the protection of their god, the wasteland valley is land that is destined to be destroyer by the extreme weather and the attacks of beast.
8 1295 - In Serial16 Chapters
A secret
Alan is a young man who just turned 25 this year and is going to be married to girl he met and dated with, her name is Diana she is very beautiful but she is holding a secret that is that she is a Vampire and not just some random Vampire and she is starting to get obsessed with him slowly But what she doesn't know that Alan is holding onto a secret that is something that no one can understand except him. And soon enough Alan is going to enter a world which he didn't knew could have existed. But with his cautiousness and intelligence coupled with his strength, he will face it. {There will be world travel and there will be all types of worlds like from advanced technology to Magic and Swords mediaeval period, to worlds where the basic logics are different and so many more....} {The MC is a bit cautious so be cautious ;) } Link for my novel on another site, it's a little bit more organized there at scribble hub site but almost same except some comments and pictures . https://www.scribblehub.com/series/415854/a-secret/ This novel is also available on https://dynamic.webnovel.com/book/22098951106485605?utm_source=writerShare&utm_campaign=4317269558 I update regularly here and there. THERE IS NO CHARACTER UNDER THE AGE OF 18 INVOLVED IN ANY OFFENSIVE SEXUAL ACTIVITIES .
8 225 - In Serial8 Chapters
Anathema
The Prince used to dance — until he discovered the strings moving his legs. The Rebel used to hope — until reality slammed a door in her face. The Spy used to live for nothing but money — until he found himself a family. And the Slave craved freedom more than air — until a small hand reached to her for help. Eskela has known conflict for centuries. War had been engrained into the very soil of every one of the eight kingdoms, and blood has been smeared over history to paint a lie. When young prince Aldric, heir to the Aguki throne, learns his position is nothing but a farce, his world crumbles down around him. As he tries desperately to find power in a world determined to rob him of it, his cousin Rhiann plots to find freedom through more extreme and destructive means. Conflict does not reside in Cinthra alone, though. Erden, newly hired spymaster for the crown prince of Promnir, is tasked with keeping an eye on the kingdom’s council. The job that was supposed to just be about money quickly spirals into a fierce loyalty, one that leads him to the front lines in order to desperately prevent another war from beginning. Azala, a slave bought by the royal family of Azmosir, finds her loyalty is not nearly as solidified as that of Erden’s. But while the prince she serves plots to steal that which does not belong to him and the queen she respects holds on to a lingering desire for revenge, Azala realizes that she must choose whom to save: herself or Azmosir's defenseless and young princess.
8 181 - In Serial16 Chapters
Reincarnator Ranker
I am Akira Sakamoto the one you called a reincarnator. It all start when boy soul wandering for ten thousand of years in the abyss but luckily god meet him and gave him second chance in life. The legend of the young boy who one day will make a great ripple of changes in the world of high fantasy nicknamed “infinity world” a world rank SSS difficulty. Will the boy survive in the most dangerously world in the galaxy that even god fears the infinity world full of mystery and adventure ?
8 100 - In Serial10 Chapters
BOSS | LayChan/ChanLay
."Yixing es el jefe. Domina, manda y obtiene lo que quiere. Quiere a Chanyeol y hará lo que sea por obtener cualquier cosa de él, y cuando lo logra, no espera que su mundo se venga patas arribas gracias a ese dulce tonto de casi dos metros. Chanyeol era la debilidad de Zhang Yixing, quien no había obtenido negro o blanco sino una gama de colores."...✎ Pareja: Chanyeol + Yixing (Lay). ✎ Semi-songfic, basado en BOSS de Lay. Aunque hay menciones de otras letras. ✎ "Songfic" | Humor | CEO!Lay x Profesor!Chanyeol | Lay!Top x Chanyeol!Bottom + Versatilidad | ✎ No copiar ni adaptar, por favor.
8 145 - In Serial22 Chapters
reborn in the beast world
Because of a bracelet that attracted me , I was reborn as a nonexistent character of my favourite novel the beauty and the beasts .How will I survive in this world with my space and handsome husbands.
8 168

