《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 80
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 80
Kulawa ta musamman Sawwama ke samu daga wajansa gabaki daya ya manta da komai ya dauki hankalinsa ya maida akan komanta,
Idan ya sameta ta zauna tana tunani kuwa zaiyita janya da hira har sai ya kwantar matada hankali,
Idan kuma ya fahinci dalilin damuwar nata yakance mata tadaina tunani dan batasan yanda Allah zaiyi dasuba abun yana daure mata kai dan baifito ya fada mata abunda yake nufi da wannan kalmar ba amma akwai abunda maganar ta dosa bataso ta sakawa ranta cewa yana fadin hakanne saboda bazai saketa ba, idan kuma yazo ya saketa tashiga damuwa, ta tasan irin wannan hali Abubakar yake dashi to da bata fara bari tasake dashi ba, gabaki daya ya sabar da ita dashi koda yaushe yana manne da ita har labarai yake bata naban dariya kawai dan yaganta cikin farin ciki duk yanda take tunanin Abubakar a nuna kulawa abun yawuce nan, a yanda ta fahinceshi yana daukan dan adam da darajar gaske mutum ne shi mai kyawun hali, itakam zatace tayi sa'ar maza da sukasan menene kulawa wanda sukasan yanda ake tafiyarda ƴa mace,
Chewing gum yadawo mata ko fita bayayi sai dai idan zai daukesu ne su fita tare, sai dai zama dashi sam bayida gundura saboda mutumne mai ilimin gaske yayi nisa a fannin boko kuma masanine na addini shiyasa duk kalamansa suna fitowa a mizani kuma a yanda duka dace, komai nasa abun burgewa ne kama daga kalan fatarsa kyawunsa da surarasa kai hatta muryarsa wani lokacin idan yana wani abun tsayawa kawai takeyi kallonsa sai ya lakaci hancinta tukunna,
Hajiya ne tace "yanzu yakamat sudawo haka tunda laulayin da sauƙi itama tasamu kulawa ta iyaye a kusada da ita."
Lokacin dawowa suka sanya ita tanata murna amma shikam sai yakeji kamar su ƙara daɗewa dan baisan yanda zasu kaya da Dr ba."
Hajiya ta tanadar musu komai kafin isowarsu sauƙa tayi musu na musamman, tasanya aka kai can gidansu,
Saida ya huta sannan yanufi gidan Dr daƙaye yashwo kanta ta haƙura da fushin da takeyi dashi danko wayarsa tadaina ɗauka,
Albihir yayi mata da cikin da Sawwama takedashi amma yakasa gane shin murna tayi ko akasin haka,
Cikin wani yanayin da yakasa kintata tace "yanzu amfaninta yaƙare ka sawwaƙe mata kawai taatfi,
Cikin lallashi yace "ai bazamu yanke shawara haka dawuri ba mubari ta sauƙa mana! Bazan iya bari ta sauƙa ba yanzu nakeso ka sawwake mata tunda munrigada mun samu abunda ƴan uwanka sukeso bazai yiwu kacigaba da zama da itaba,
Nisawa yayi yace "idansu Hajiya suka tambayeni dalilin Sakin me kikeso nace musu? Ko yaya kibari musamu wata mafaka kuma ni inaso na raini yarona tare dani, idan bata tare dani kinga hakan bazai yiwu ba,
Baƙin ciki ya sanya tabar masa ɗakin gabaki ɗaya,
Kwanansu biyu da dawowa yakaita ta gaida Hajiya yanzu tabar laulayi sai azabar ci arana sai sAwwama taci abinci sau biyar,
Advertisement
Sawwama ta kawowa hajiya da Alhaji tsaraba sunyi murna sosai,
Dama tun acan Abubkatar ya shaiadawa mahaifansa cikinda Sawwama take dashi, Tun kafin su dawo zance yarigada ya ratsa dangi kowa yasan da zancen cikin, Hajiya kullum burinta ɗaya su dawo tacigaba da kulada lafiyar Sawwama."
Alhaji yana shigowa Hajiya ta sanar dashi zuwansu Sawwama, Alhaji dama ya rigada yagama tsara kyautar da zaiyi mata, takardun gidanda suke ciki alhaji yabata, dungurum gun,
Sawwama sai take ganin lamarin kamar amafarki, hawayene yafara gangaowa akan fuskaarta na tausayin kanta da mahaufansa tasan zasu shiga wani hali idan sunsan irin aurenda sukayi dakuma sharaɗin auren, dasunsani da basu ɓarnatar da dukiyarsu, akanta ba,
Tayiwa Alhaji godiya sosai da fatan alkahiri."
Bayan sun koma ta ɗauki takardun tabawa Abubakar amma yace mata wannan natane halak malak alhaji yabata ta ajiyesu a wajanta ko takai gidansu a ajiye mata,
Washe gari yakaita gidansu da mamakin Sawwama tasamu mama ta haifu Jaririnta kuma ko a waya babu wanda ya faɗa mata, dama ita duk ganin da take yiwa mama kamar mai cikine amma bata kaiga tambaya ba,
Haihuwar Halima kawai tasani itama ta haifi yarinyarta,
Mama kuma kunyace ta hanata Bayyanawa duk da cewa bawai tawani girma bane amma tana ganin yaranta suna haihuwa itama na haihuwa, ko taron suna basuyiba, yaci yaci sunansa Muhammad,
Sawwama tayi murnar ganin mahaifanta cikin walwala sunata godiya suna shaida mata irin abun alkahirin da mijinta da danginsa suke aiko musu dashi gabaki ɗaya sun canja sun dawo shar dasu,
Cikin dake jikin Sawwama kuwa suma sun rasa shin murna zasuyi ko fargabar auren ƴarsu daya kusa mutuwa, sudai yanzu sun zubawa sarautar Allah ido kawai suna jira suga yanda lamarin zai kaya."
Washe gari Sawwama taje taga Halima Abubakar da kansa yakaita, dama tun kafin su tafi ta aiki mai aikinta kasuwa tayi mata sayayyar kayan yara dana manya,
Halima tayi murnada ganin yanda Sawwama ta canja ita kanta haliman ta canja sosai saboda tana samun kula sosai,
Saida ya tsaya suka gaisa da Halima sannan yawuce Halima tace "yaya Sawwama a ido wannan mutumin kamar mutumin kirki, Harararta Sawwama tayi tace "dama ance miki mutumin banza ne shi?
Halima duk yanda kike tunanin kirkin mutuminnan toh yawuce nan kamar yanda kamanninsa yake haka zuciyarsa take, taɓe baki Halima tayi tace"komadai menene yaya Sawwama bai kamata ya biyewa matarsa su aikata wannan abunba wannan cutane zasu cutarda rayuwarki dana abunda zaki haifa saboda son zuciyarsu,
Murmushi Sawwama tayi sannan tace "Halima kenan inaji ajikina wannan mutumin bai waureni dan ya rabuda niba, mekika gani yasa kikace haka? Inji Halima, Sawwama tace "akoda yaushe nayi masa maganar rabuwa yakance nabari zuwa lokacin saboda bamusan yanda Allah zaiyi damuba wallhy kirkinda yake dashi yawuce yanda zakiyi tunani bantaɓa tunanin za'a samu mutum mai dukiya haka da azabar kirki ba, amma ni banaso na sakawa raina hakanne yazo kuma ba haka bane, kuma saboda matarsa komai zata iya aikatawa dan tarabani da mijinta,
Nisawa Halima tayi tace "nima ina fata ace bazaku rabuba yaya Sawwama Allah yasa kamar yanda yakeda ƙyawun fuska haka zuciyarsa take kyakkyawa gameda ke, itakuma matarsa karki damu da ita har indai mijinki yanuna yanasonki kuma zaici gabada zama dake toh ki toshe kunnuwanki, duk wani abunda zatayi taje tayi ai ita tafara, kuma dama irin wannan lamari ba'a cika farashi aƙareshi yanda rai yasoba, shiyasa karma ayi kar afara."
Advertisement
Sai magrib kafin yazo ya ɗauketa wannan lokacin Halima ta sake masa ba kaman ɗatsuba jin kalamansa akan yayartata."
Satinsu guda da dawowa amma baiji Dr tayi masa magana akan yafara ƙwana gidan Sawwama ba ranar haƙurinsa ya ƙare ya shaida mata cewa zaije wajan Sawwama saboda ba ita ɗaya bace yanzu tana buƙatar kulawarsa kusada ita,
Dr tace atafir batasan zance ba ita ai dole tunda yanzu tasamu ciki bazaije wajanta ba tunda anrigada ansamu abunda yasa yakeson zuwa wajannata, babu irin lallaɓin da baiyi mata akan tabarshi taƙi,
Cikin lallami yace "Dr kowane irin aure fa mukayi da ita inaso ki sani cewa itaɗin matata ce kuma akwai hakkinta akaina Allah zai tambayeni duk wani rashin adalcin dana mata banaso na kasance mutum maras adalci, alokacin da zan yanke igiyar aurena akanta shine kikeda ikon hanani zuwa wajanta, amma banda yanzu saboda ahalin ynzu tanada buƙatar na kasance kusada ita,
Kuka Dr tasaka tana faɗin kaci amanarta, idan baka mantaba kafin ka aureta saida nasaka kayimin alƙawarin cewa da zarar ta samu ciki bazaka sake kusantarta ba kuma bazaka taɓa sonta ba idan lokaci yayi kuma zaka saketa,
Abubakar yace"duk nayi miki waɗannan amma na gwammaci na saɓa miki akan na saɓawa mahaliccina, dan haka mu yanke wannan alƙawarin zanje gareta duk bayan ƙwana biyu kuma zan kulada lafiyarta har izuwa ta sauƙemun abunda yake cikinta, yana dauriyanr kawai yana faɗa mata haka amma yana cikin tashin hankali ganin kukanda takeyi, aranar haka baisamu zuwa wajan Sawwama ba amma kamada daga washe gari yafara zuwa babu irin rikicin da Dr batayi ba amma haka yaƙi sauraronta,
Ganin yanda yayi watsi da alƙawarin dayayi mata yasata ɗauki zafi sosai da lamarin, sau biyu tana zuwa yiwa Sawwama warning."
Duk abunda takeyi ko sau ɗaya Sawwama bata taɓa maida mata martani ba abun har mamaki yake bawa Dr da Abubakar, basusan haƙurin Sawwama ba tazauna da wacce tafi Dr hauka (Abida)😅
Cikin Sawwama sai sake girma yakeyi tana sake samun kulawa daga kowanne ɓangare,
Cikin yana shiga 9month Hajiya ta sanya Abubakar yadawo da ita gidanta da zama gabaki ɗaya, itake kulawa da ita yanda ya dace,
Sai fama takeda fargabar abunda zai faru bayan haihuwarta dan ahalin yanzu tama wufe EDD ɗinta,
Har bataso ta haihu kullum kuma da fargabar ko aranar zata haihu take,
Abubakar ne yashigo amma Aisha kawai yasamu a falo zama yayi ta gaidashi yana tambayarta ina hajiya, tana side ɗi alhaji tabashi amsa, "Hafsa fa? Ya tambaya, tana ɗakinta muna kallo tatashi tashiga,
Inadao lafiya ya tambaya?
Inaga lafiya amma bazan iya kintataba tunda dama kwanakinnan batajin daɗi, miƙewa yayi yanufi ɗakin da dake,
Azaune ya sameta bakin gado ta yi nisa cikin tunani harya ƙarasa ya zauna bata ankaraba ba saida ya riƙo hannunta, Arazane ta juyo sai kuma ta sauƙe ajiyar zuciya,
Jawota yayi jikinsa ta ƙwantarda kanta luff zuciyarta babu daɗi,
"Ko zan iya sanin abunda yake damunki? Ya tambaya cikin kulawa,
Runtse idanuwanta tayi bakinta ya kasa furta komai, cikin kulawa yacigaba da faɗin tunani baida ƙyau a lafiyarki a halinda kike yanzu,
Hajiya ce ta ƙaraso falon bata zaunaba taga babu Sawwama a zaune yanda tabarta duban Aisha tayi tace "ina kuma Anty Hafsa tayi? Aisha tace "tashiga ɗaki yaya Abubakar ma yazo yana wajanta, juyawa Hajiya tayi zuwa ɗakin Sawwama,
cakk ta tsaya daga bakin ƙofar ɗakin jin Sawwama cikin sanyin murya tana faɗin "Dole nashiga damuwa awannan yanayin koka manta cewa da zarar na haihu mun rabu dakai kenan?
Ko kasan yanda nakeji? Ni kenan rayuwata kowanne lokaci da irin ƙaddarar da zata zomin dashi, meyasa ka aureni? Da tun lokacin baka yarda da aurena ba saboda zakazo kayi dana sani bayan rabuwarmu,
Ni Dalili ɗaya yasa bazanyi dana sanin aurenka ba shine samun lafiyar ƙanwata, kuma nasamu kwanciyar hankali daga gareka, da san wannan kulawar zaka bani daga karshe kazo ka tsinketa
Da akwai yanda zamuyi da ban aureka ba domim ni duk wani ƙyaleƙyelen duniya bai dameni ba amma inason koda sau ɗaya arayuwata na samu kwanciyar hankali inason kwanciyar hankali mai daurewa ba wannan wacce kake bani mai iyaka ba, yanzu mai zan cewa abunda na haifa? Wani irin aure nayida mahaifinsa? Shin abunda na haifa idan ya girma zai fahimceni?
Ga mamakin Sawwama Abubakar murmushi yakeyi saida yabari da ida sannan ya sanya hannunsa ya share mata hawayen dake gangara akan kumatunta cikin kulawa yace "Ga dukkan alamu kin fara sona kamar yanda nima nake sonki, ni ban aureki da niyyar da nasakeki ba koda kin haihu Sannan kuma koda baki yarda da aurena ba tunda ta faɗamin nayi niyyar biyawa kanwarki kuɗin magani, naje asibiti sau biyu na ganki kuma na bibiyi rayuwarki ta baya naji abunda yafaru duk wasu halayanki na sansu da irin haƙurinda kike dashi, niba karamin mutum bane da zan yarda kawai nayi aure batareda bincike ba hakan bamai yiwuwa bane, alokacin dana daura niyyar aurenki tun daga lokacin nasakawa raina ko na aureki bazan rabu dakeba saboda Hali irinnaki kaddara ce kawai zaisa wanda ya aureki yarabu dake,
Zan iya cewa mutane masu hali irinnaki sabuda yawa, toni wane gigin zai kaini narabu dake?
zamana dake ya sake tabbatarmin da ke wacece, macecece ke mai sanin yakamata haƙuri da rashin son abun duniya samun mace kamarki is very rare sai dace, bani kadaiba kina tunanin akwai wanda zai samu kamarki kuma yarabu da ita?
Ban damu da abunda Sajida zata aikata ba dan nasan na wani lokaci ne amma bazan rabu dakeba zamu zauna ki haifamin yara masu kamada ke, yanzu ki kwantarda hankalinki kinga halinda kike ciki,
Hajiya dake jiyosu alokacin jikinta duk yabi ya mutu tambayar kanta takeyi shin mai yarannan suka aikata? Mai kunneta yake jiye mata? Ganin batada amsar wannan tambayoyin sai daga garesu ya sanya ta."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial395 Chapters
Blackthorne
One day the entire world fell asleep at the same time. No matter who or where, all people fell into a deep slumber. During that singular moment, a single dream was shared between the disparate members of humanity. It was a dream about creating a new life in a new world. Many people died during the first dream. Drivers crashed their vehicles. Surgeons collapsed atop their patients. Workers fell from rooftops, and many others met their end during the time that the first dream was forced upon humanity. Despite the tragedy of that day, the strangely videogame like nature of that dream and the world presented therein has caught the world in a web of interest and intrigue. One young man, decides to change his life by living for that strange new world and its untapped possibilities.
8 385 - In Serial6 Chapters
I'm A Professional Gamer, So How Did I Become King?
Watch as an Immortal, near All-Powerful being recounts the tales of his and his wives rise in power. I don't want to make the MC OP, but he will be incredibly strong and fight really strong beings. I make no promises when it comes to release dates, just so you know, however I don't plan on dropping this, as it contains ideas from multiple fictions I've written but never posted. I don't own the cover picture.
8 151 - In Serial50 Chapters
The Female
Nobody quite knows why women stopped being born, but as the numbers began to dwindle it didn't take long for men of all breeds to grow restless and aggressive, stealing any women they could find and claiming them as their own.Parents began to hide their daughters from the Seekers, stowing their females underground in an attempt to keep them safe.Charlotte, despite her desire to leave, has accepted that she will live out her adult life in the basement of her parent's house. Tucked away and hidden from the men that would tear her family and house apart to get her.When the Seekers show up for a surprise raid, Charlotte is one of the unlucky women who are found. Forced out of her home and thrown into a world that she has only experienced through stories from her parents, Charlotte must learn how to stay alive and serve the three powerful demons that purchased her._____Note: Charlotte is a grown adult (despite having spent her life in her parent's basement) and isn't going to portray any childlike, oblivious tendencies that similar stories in this genre (sheltered female) sometimes do.⚠️THIS BOOK CONTAINS MATURE AND TRIGGERING THEMES⚠️_____
8 112 - In Serial50 Chapters
Death's Emissary
Caught in a conflict between gods, Scarlet is forced to serve the goddess of Death to save her own life. When her mother goes missing, Scarlet becomes determined to use her newly acquired prowess as a mage to rescue her—which means entrenching herself further in Death's battle against Riordan, a power-hungry god who seeks to control mortals and immortals alike. Dante would do anything to protect the people he cares about, but he isn’t safe himself. Magic is illegal, and it’s getting harder to hide that he’s a mage. Visions of the past and future haunt him, and it won’t be possible to protect himself and his magically-inclined sister forever. When his quiet life is torn away, he’s forced to face his powers and a whole new world. Someone stole Jarrett’s memories. He isn’t going to stop searching until he finds out who—and why. In the meantime, his focus is on commanding a secret rebellion force in hopes of securing autonomy for the oppressed mages of the kingdom. Their fates collide as they become entrenched in the battle against Riordan. To have any chance of slaying a god and freeing themselves from his tyranny, they’ll have to place trust in the right allies and master newfound powers.
8 175 - In Serial9 Chapters
The Planes of Mil'Tish
The planes of Mil'Tish are plagued by the constant cycle of war, the gods who are supposed to guard the mortals are selfish, malicious, and greedy. entities in the chaos are constant threats who wish to enslave all life in the planes to do their bidding. James a denize of earth is reborn in this hopeless universe as a lowly goblin who are synonymous with the word cannon fodder. watch how james tries to break free from that cycle, how he elevates the goblin species, and more. *This is my first story, and sorry for the sypnosis i'm pretty bad at writting one*
8 166 - In Serial14 Chapters
The black phone x reader
It's 1978 you have two brothers and a sister your Friends with Gwen you are very smart and do well in school robin and Vance don't die in this story and the grabber is already dead sorry if that's what you didn't want but finney killed him already READ AND ENJOY THE STORY I LOVE THE BLACKPHONE BTW
8 161

