《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 79
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 79
Suna cikin meeting alhaji ya kirashi awaya bai samu ya ɗaukaba sai bayan yafito ya kirashi Alhaji yace masa yazo yana nemansa,
A ƙanƙanun lokaci ya isa wajan mahaifunsa bayan sun gaisa yake sanar dashi cewa yanaso suje saudi shida matarsa amarya sannan kuma suwuce wasu ƙasashe guda biyu itama ta buɗe idonta kuma duk tafiyarku ni zan ɗauki nauyinsu gabaki ɗaya,
Naga aurenku wata huɗu amma haryanzy bakada niyyar yin hakan, kuma mahaifinta basuda ƙarfi izuwa yanzu yaci ace kafara taimaka musu wannan nabar makane kai dakanka kayi kasamu ladan sirikanka da kanka,
Kansa yana ƙasa yace "in sha Allahu alhaji zanyi,
Alhaji yace "saiku fara shirin tafiya nanda wani lokaci,
Godiya yayi masa sannna yawuce wajan Hajiya ya faɗa mata abunda Alhaji yayi,
Hajiya tace "eh munga kai bakada niyyar kyautatawa shiyasa, wancan matarda ka aureta wace ƙasace bakujeba amma yanzu wannan aure wata huɗu kazauna kayi shiru, ko tsoronta kakeji shiyasa ita wannan kakasa kyautata mata?
Ƙasa yayi da kansa bai iya cewa komai ba, Har Hajiya tayi faɗanta tayi shiru, Sannan daga ƙarshe tace yakawo mata sawwama ta kwana biyu bata gantaba, ya sama da cewa zai kawota amma sai gobe,
Hajiya tace toh Allah yakaimu,
Taraddadin yanda zai gayawa Dr wannan maganar yakeyi dan baisan yanda zata ɗauki abunba,
Saida yabari ya daidaici lokacin da suke cikin farin ciki sanna ya dubeta cikin wani yanayin da bazata iya karantar mood ɗinsa ba yace "Alhaji ya nemi ganina 2days back so naje yake sanardani cewa yabiya mana saudi nida Hafsa and kuma bayan nan zamuyi tafiya zuwa wata ƙasar daban kuma komai shine yaɗauki nauyin hakan bansan yaya zaki ɗauki lamarinba shiyasa ban sanar dake ba amma yaya kike ganin zamuyi, tunda yafara magana tasake baki tana kallonsa, bazaku jeba tafaɗa ataiace sannan ta ɗaura da faɗin ai bawai an aurota bane dan taji wani daɗi tasake dakaiba meye nawani har zuwa wata ƙasa kabari idan ka saketa saika biya mata saudi tubda tarigada tadawo uwar ɗanka,
Shafo kanta yayi yace "Alhaji su duk basusan da hakanba sun ɗauki wannan aurene kamar kowani aure kuma bazan iya mayarda ƙyautarsa garenu ba saboda bansan wane dalili zance masaba kinsan Alhaji kinsan yanayin tsaurins bazan iya bijirewa maganarsa ba,
Advertisement
Kuma dana zauna nayi tunani sai naga mai zai hana mutafi da ita ɗin kema mutafi tare amma kibiyomu daga baya, bansan ko acan idan babu idonki zan iya kusantarta ba,
Fauce hannunta tayi tace nace maka A'a bazkaa tafi da itaba idan bazaka kusanceta ananba kabari kuma kasan a irin wannan lokaci da nakeda patient dayawa bazaiyiwu natafi nabarsu ba kawia ka janye zancen tafiya da ita,
Amma dai kinsan bazan iyaja da maganar Alhaji bakoh? A fusace tace ni ka saketa kawai, ka saketa tunda dama ni nace ka aureta yanzu nafasa,
Miƙewa yayi yace wai yaronki kika maidani? Duk wani abunda kikace kinaso shi nakeyi saboda na faranta miki amma ke kullum sai kiringa yin abunki da isa kinsan banason haka kuma akanki bazan ɓatawa mahaifana ba, yana gama faɗi yafice a gidan bai dawoba sai dare a ɗaki ya sameta ta zauna tayi zugum zama yayi a gafenta cikin sanyin jiki jawota yayi jikinsa yafara bubbuga bayanta yaɗauki tsawon lokaci ahaka sannan yaɗagota hawaye yagani a fuskarta cikin rawar jiki ya sanya hannu ya share mata hawayen, Haba haba Sajida wai har meyayi zafi haka baki yarda dani bane?
Soyayyar da nake miki yasa nake biye miki a komai da kikeso wanda yawancinsu daga ƙarshe muke zuwa muyi danasani, farkon aurenmu babu yanda banyi dakeba akan ko yaro ɗaya mu haifa amma kikaƙi kikace karatu haka soyayyarki ta sanya na amince dukda raina bayaso,
bayan kingama karatu haka kikace aiki yayi miki yawa nanma na biye miki, har mahaifana lokuta da dana nakan bijirewa maganarsu saboda ke meyasa duk wannan abun bazaki iya fahintar sonda nake miki bazai bari naci amanarki ba?
Yanzu ni banaso wani abun yasake haɗani da mahaifana ta dalilinki inaso a yanzu komai dake tsakaninku ya dai-dai ta kinsani sanin kanki cewa ke kika fara saɓaw ada ƴan uwana su basu nuna miki wani haliba basu taɓa nuna miki wani ƙi ta dalilin baki haihuba abunda kike mus yasa suka canja miki kuma hakanma ban goyi bayan dangina ba ke nabi baya, kinsani kinsan dangina mutanen kirkine bzasu taɓa ƙinki da baki haihu ba, kuma laifin rashin haihuwarmu duka laifimmu ne mun biyewa son zuciyarmu,
Toh yanzu ma idan bakiyi hankali ba koda wannan tatafi wata zasu sake sawa na auro kinga nikuma bazan zama sai auri-sake ba,
Advertisement
zan zauna da wanda zasu auramin nan gaba har indai baki tsaya kin kwantar da hankalinki Anyi komai kamar yanda aka tsara ba, maganar tafiya kuma zamu tafi da ita idan hankalinki bai kwantaba ki biyomu amma bazan saɓa umarnin Alhaji ba,
Lumus tayi ajikinsa tana sauraron abunda yake faɗa komai tasan ta aikatashi shiyasa tayi shiru dan itama duk zafin zuciyarta bata iya juran ɓacin ransa nan danan take shiga damuwa ko tafara kuka dake tasan baya iya jure ganin hawayenta."
Jin yayi shiru da maganar yasa Alhaju yasake tun tuɓarsa yace Alhaji inaso zanyi clearing schedule ɗina na month ɗin gaba gabaki ɗaya sai mutafi zuwa wancan month ɗin,
Alhaji yace toh hakanma yayi Allah yakaimu."
Sawwama na gaban mirror ta fito daga wanka ɗaure da towel ta zubo gashin kanta abaya tajiyo shigowarsa amma bata juyoba tacigaba da abunda takeyi tabaya yazo ya rumguneta janye gashin kanta yayi gefe yayi mata kiss abaya murmushi tayi tace sannu da zuwa, ƙara rungumota yayi ya saka kansa a wuyanta yana kallonta ta cikin madubi yace albishir,.
Goro tafaɗi tana sakar masa murmushi Hajiya tace nakaiki tun jiya amma bansamu dana nazo nakaiki ba idan kuma taga driver ne yakaiki zatayi faɗa yau zamuje saiki yiwa Alhaji godiya ya biya mana zamu tafi saudi, juyowa tayi tana kallonsa dan son gasgakatar da abunda yake faɗa,
Ganin babu wasa a fuskarsa ya sanya ta raba jikinsa da nata ta isa izuwa gado ta zauna bin bayanta yayi da mamakinsa sai yaga batayi murna da hakanba
Bai yanke mata hukunci ba dan baisan dalilinta ba ya isa bakin gadon shima ya zauna,
Kamo hannunta yayi cikin kulawa yace"mai kuma yafaru? Maimakon kiyi murna sai naga akasin haka, sunkuyarda kanta tayi hawaye yanason zubowa tana ƙoƙarin maidashi tace "duk waɗannan abubuwan bamasu ɗaurewa bane kabari kawai nagama abunda ya kawoni natafi banajin daɗin wannan muguwar shaƙuwa dake shiga tsakaninmu,
Kamo hannunta yayi ya sakar mata murmushi sannan yace nikuma inaso, karkiyi judging komai yanzu bakisan yanda Allah zaiyu damu nan gababa, kedai yanzu ki shirya muje kiyiwa Alhaju godiya,
Gabaki ɗaya takasa gane yanda maganarsa ta dosa amma saboda batason sakawa kanda damuwa kawai saita share tayi masa godiya,
Yakaita tayiwa Alhaji godiya kuma yaji daɗi sosai."
Acikin month ɗin suka fara shirye-shiryen tafiya
tun awaya ta sanarwa mama kafin taje ta sanar msu Mama akan cewa zasuje Saudi kuma daganna zasu wuce wata ƙasar,
Mahaifanta sunyi murna sosai dan sunce zuwa saudi komadai menene a auren ai alkhairi ne,
Saudi suka fara zuwa dayake yazo ɗaya da lokacin aikin hajji,
sukayi aikin hajji wtaansu ɗaya acan suka wuce wata ƙasar,
Tarairaya da kulawa sosai Sawwama take gani a wajansa, zuciyarta takan yabi irin kulawa da tarairaya dayake mata, wata zuciyar sauta haneta tace karta fara ta faɗa domin gaba zatasha wahala kuma duk abubuwan dayake bawai dan yana sonta yakeyi mata na sai dan neman cikar burinsu shida matarsa, Amma ahaka idan kukaga irin kulawarda yake nuna mata saiku rantse auren soyayya sukayi,
Shikansa yanajin daɗin zamansu da Sawwama sosai domin ta kuwa ta iya zamada mutane iya zamansu bazai iya faɗin wani halinta da takeyi wanda bayaso ba, komai nata a nutse tajeyinsa Sam batada hayaniya gashi tanayi masa biyayya akan duk wani abunda yakeso,
Satinsu biyu acan Sawwama tatashi da zazaaɓi ya matsa sutafi asibiti tace dasauƙi basai sunje ba, ƙwana biyu da samun lafiyarta still wani ciwon yasake dawowa wannan lokacin kam dolenta saida tayarda sukaje asibiti, likita sun shaida masa tana ɗauke da ƙaramin cikin na wata ɗaya, Alhamdulillahi kawai yake faɗi yana godiya ma ubangiji,
Ita kam Sawwama tarasa wani irin hali take ciki shin murna zatayi? Kokuma baƙin cikin takusa rabuwa da mijinta?
Shi kansa saida ya fahimci halinda take ciki sai tabashi tausayi yasan koda ace bata sonsa sai taji wani iri idan tayi tunanin cewa da zarar da haihu zata rabu dashi saboda shi kansa yanzu bazai iya cewa baya sonta ba bare ita mai sanyayyar zuciya,
Kwantar matada hankali yayitayi harya samu ta ɗan sake tadawo kamar yanda suke."
Tunda Aka tabbatarda cikinne kuma sai jinya laulayi kala-kala, shidai yanan yana kulawa da ita kamar ƙwai saida cikinta yakai 4month kafinnan ya sanarwa su hajiya lokacin harya ɗan fara fitowa laulayin kuma yayi sauƙi sosai."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial76 Chapters
Path of Divinity
The world has been assimilated by the Celestial Archives, a vast system designed to fight the forces that seek to destroy the universe. For most, it's a holy cause that rewards victory with stats, levels, and skills. For Hunter Gold, it's the start of a nightmare. Even in a system dominated by paths, he finds himself taking the road less traveled. This is a work in progress. Major editing will be done after the book is complete, so there will be egregious typos and parts that make no sense whatsoever. Please feel free to point any and all of these things out. Chapters WILL get edited, and that editing might break earlier chapters. I will attempt to keep readers apprised of all changes. As always, feedback is welcome and appreciated. This is kind of something fun I wanted to write after reading stories like The New World, System Apocalypse, and the Legend of Randidly Ghosthound. I don't know how serious I will be about this story, but I just want to try it out. I imagine that it will become a love child between Fable, Diablo, and Devil May Cry. Enjoy! The Scourge Wars Universe Evolve: The Scourge Wars Book 1 (published) Adapt: The Scourge Wars Book 2 (published) Resist: The Scourge Wars Book 3 (published) The Othryrian Archives Advent (Read on RoyalRoad) To stay up to date on all my writing, get exclusive e-books, and be eligible for Audible audiobook codes (no purchase required) please sign up for my mailing list.
8 232 - In Serial6 Chapters
Pushers
Within the span of a few hours, the stability of Delilah's world is shattered. Her father has gone missing, leaving only a cryptic note as an explanation. Desperate to find her dad, she partners with the only people who may be able to provide some answers - the very people her father warned her of, who also happen to have abilities she wouldn't have believed if she hadn't seen them with her own eyes. Now caught up in an age-long, secretive war, and unsure who to trust, Delilah fights to unravel the mysteries surrounding her and discover the truth about her father - and herself.
8 107 - In Serial6 Chapters
Nend Ardhon Chronicles
In a future not so far away, a young female pilot was flying back to her home Planet transporting the junior team of Chess, that was returning victorious from a Galaxy tournament.Upon being hit by a small meteorite, she had to do an emergency landing on a moon of a desertic Planet. With all her effort and resolution, she managed to land everyone safely, except for her. A huge chunk of metal was stuck on her chest and the team’s Teacher held her hand on her last breath.When she woke up, she was surrounded by darkness. Reaching out with her hands, she felt a surface that she scratched. A hole opened, that she made bigger and bigger. Around her, water everywhere. In front of her, was a big smiling Dragon. That was when the young pilot noticed that she was reborn with claws and a tail. She was now a Water-Dragon. The chock of the events that followed her exit from the egg, blocked her former life memories.Join Byia Calla on her new life as a Water-Dragon. Will her memories help her in her new life? Or will they become a burden too difficult to endure?
8 125 - In Serial61 Chapters
The Bride of Gojo Satoru
Ena Kita is the last member of the Kita Clan, who were the gift of God during the prime era of sorcery. Because Ena's lineage is sacred, she's forced to marry Gojo Satoru, a powerful sorcerer whose offsprings can bring luck to the world. At first, she only used him for freedom when she was eighteen, but now she's head over heels for the man after ten years of being engaged."I can't believe I've been engaged with you since young," "Why are you complaining?! I know you love me!" However, when shamans heard about Sukuna incarnating a teenager's body, the Kita Clan grew worried for their last descent. Ena was never told by her family members that her face resembled the past lover of Sukuna. "Sukuna, you better watch how you speak to my wife." Gojo Satoru stood in between me and Sukuna. ///PUBLISHED: 11/5/2020ENDED: 06/07/2021This is on fanfiction, ao3, and quotev :)
8 102 - In Serial10 Chapters
The Legend of The Demon Prince
Kong Yue was born in a royal demon dynasty , had an abnormally high innate talent regarding elemental affinity. But was unable to cultivate all because he had a dantian which was already full to the brim with something. He was not able to absorb energy neither use the thing filling his dantian. Will he give up or continue tostruggle to become the strongest immortal ever?
8 64 - In Serial31 Chapters
Flutter ||pjm (COMPLETED)
"Don't you remember changing clothes by 'yourself'?" "Oh did i....??" "Yes pabo" Oh, did I changed my clothes on my own? Well...I'm not sure about thi- waittttt did jimin............O.M.G.........Jimin ff/ for all Jimin biased :) actually for all armys hahaCOMPLETED!
8 200

