《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 77
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 77
Ranar Asabar da safe aka daura auran Sawwama da Abububkar ko walima ba'ayiba zallan daurin aurene,
Sawwama babu abunda takeyi sai kuka Mama na rarrashinta tana fadin in sha Allahu babu abunda zai biyo bayan wannan aure sai alkahiri,
Da dare aka dauki amarya izuwa gidan mahaifansa aka fara kaita daga ita sai can kowa ya watsa cikeda al'ajabin irinna gidanda suka kai Sawwama da yawansu idanba a TV ba basu taba cin karo da irin wannan gida ba, an watse an barta daga ita sai Halima sai wasu biyu yayan yan uwan baba,
Gidan acike yake dam sai da jama'a kai kace taron siyasa akeyi,
kowa yazo taya hajiya murnar Samun karuwa,
Sawwama tayi kuka harta gaji jikinta yayi sanyi har wani zazzabi takeji ita ba aurenne damuwarta ba manufar aurenne ya dameta,
Bacci ne ya dauketa dake dama saida sukayi Sallar isha'i aka daukosu, wata yar yarinyace tashigo bazata wuce shekara ashirin da biyar ba, da fara'arta ta zauna ta gaidasu sannan tace musu an ajiye musu abinci yana falo, da duk wani abun bukata
Duk yanda taso taga fuskar Sawwama abun baiyiwuba haka tafita,
Palour suka nufa komai an ajiye musu abincin sama da mutum ashirin,
Dakyar Halima ta rarrasheta tasamu taci abinci kadan sai dare sosai sannan su Halima ma suka tafi,
Wannan yarinyar datsunne tasake dawowa taganta ita daya,
Zama tayi adakin shiru babu wanda yacewa wani komai, can yarinyar tagaji da zaman shiru tace anty amarya dan Allah kibude fuskarki ni kadaice a dakin,
Sawwama taja gyalenta ta bude fuskar ta murmushi ta sakarwa budurwar itama ta maida mata tace kai ma sha Allah lallai yaa abubakar yayi sa'ar kyakkyawar mata, murmushi kawai Sawwmaa tasake yimata,
Tace ni Sunana Aisha nice autarsu yaa abubakar, hira sosai take tayiwa Sawwama itakuma sa'i-sa'i take amsata, yarinyar tafice tace ina zuwa,
Shashin Hajiya taunufa tashiga tasamu hajiya da yayanta mata da yan uwanta dukda dare yayi amma suna zaune suna hira, aisha ta isa zuwa jikin Hajiya tace Hmm hajiya naga amaryar Ya Abubakar kin ganta? Wallhy kyakkaywa, Hajiya ta fadada fara'arta tace kai ma sha Allah,
Bakiga wani abun mamaki ba hajiya wallhy karamar yarinyace, Hajiya tace eh ance karamar yarinyace ta'iya yiwuwa bazata wuce sa'anninki ba, A'a hajiya batama kaini ba dan wannan bazata wuce shekara sha ba atayi takai ashirin, Hajiya tace ah lallai yarinyace kam toh Allah yabasu zaman lafiya yasa tanada halaye masu kyau, mikewa Aisha tayi tace barina koma dan abunda nazo fada miki kenan,
Hajiya tayi dariya kawai itakuma ta juya yayyunta sai tsiya suke mata wai takawo gulma,
Atare suka kwana da Aisha cikin kankanin lokaci har sun saba, dasafe tayi wanka ta canja kaya,
Da yamma akayi budar kai amma ango bai halarta ba Hajiya ta kirashi tanata fada yace mata bakinda sukazo aurenne basu gama tafiyaba so babu hali yatafi yabarsu,
Kowa sai sanya albarka yake yiwa Sawwama
Advertisement
Da dare Hajiya dakanta tasa yan uwanta suka raka sawwama gidanta,
Gidan ya tsaru sosai wuce tunani, Nasiha da addu'a sukayi mata sannan suka barta,
Wanka tashiga tatsaya kallon tsararren toilet saikace a film, na'urori dayawa bata iya amfani dasuba haka ta taba iya yanda ta iya tayi wanka tafito,
Tana zuwa kwanciya tayi tafara tunane-tunane kawai sai Sadam ke fado mata aranta kuka tayi sosai sannan bacci ya dauketa,
Abubakar yana wajan matarsa ko niyyar fita bayi dashi itakuma kuma bata cemasa yatafi ba dan aganinta tunda ita ta sanyashi yayi aure toh ita zata bashi umarnin yaje ko akasin haka,
Kwanciya bacci sukayi batareda damuwar sunbar amarya ita kadai ba,
Washe gari Hajiya ta aikowa Sawwama abin karyawa hakama da rana harna dare,
Kwananta uku a gidan banda masu kawo abinci da yan aiki bataga idon kowaba,
Bayan tayi sati saiga mama dasu laraba da kannen Baba sunzo dubata bata gwada musu wata matsala ba sunata yaba kyan gidan banda mama wacce tasan zamanta ciki na wani lokaci ne,
Basu dadeba suka tafi sai gabaki daya taji babu dadi, takoma gidan jiya ita daya sai wayarta idan damuwa ta dameta tayi kuka ta gaji sannan ta lallashi kanta."
1month kenan da auransu Abubakar ko matarsa babu wanda yataba lekota aciki,
Suna zaune da Dr, Dr tace Naga baka motsa gameda zancen yarinyar nan ba nayi maka magana kaki cewa komai ko kanaso tayita zama a matsayin matarka na lokaci mai tsayine?
Gara ayi mai yiwuwa ta wuce mana kayi ka tsinke igiyar aurenta akanka,
Kwantarda ita yayi ajikinsa cikin lallashi yace. "Sonda nake mikine banaji zai iya bari na kusanci wata macen bayan ke shiyasa kikaga har yanzu ina wannan abun amma zan san abunyi,
Murmushi tayi tace "ni nasani nasanda irin sonda kake mini amma kuma zamanta a matsayin matarka na tsawon lokaci yafi dagamin hankali fiyeda abunda zaka aikata."
Yau kaje gidanta ka kwana kallonta yayi da mamaki yace kin tabbata? Zuciyarki ta aminta da hakan? Iska ta furzar tace idanma zuciyata bata aminta ba yaya zanyi? Nidai kawai banaso tayita jimawa da auranka nida tana samun ciki kawaima ka saketa ta haihu ka karbi kayanka, murmushi kawai yayi batareda yace komai ba,
Da dare haka ta sashi agaba saida yatafi can, karfe tara na dare yayi parking din motarsa a harabar gidan mai gadi ya rufe gate ya zo yana gaidashi amsawa yayi cikin fara'a cikin takunsa na kasaita yawuce ciki."
Lambobi ya danna kofar shiga palourn ya bude komai na palo farine kujeru set biyu aciki sai can gefe wani palour daban sai dakuna wanda zasu kai 10 haka aciki,
Daya kofara da zata sadashi da palourn ya nufa yashiga dan anan aka shirya masa dakinsa daya dakin kuma yasan natane, kai tsaye dakinsa ya nufa saida yayi wanka yagama duk wani shirin kwanciyarsa sai kuma zuciyarsa take kwadaita masa son ganin matar tasa, wanda shi bada niyyar sanyata a idanuwansa yazo ba,
Wanka tashiga tayi da turaren wanka ta fito daure da towel ajikinta fuskarta sam babu wani walwala,
Advertisement
Bude dakin yayi da sallama ahankali yashiga bata jiyoshi ba saboda yanda yayi maganar baya-baya, idanuwansa ya sauka akanta wacce ta juya baya batamasan da shigowar wani dakinta tun daga kasa yake kare mata kallo gabansa yana faduwa har izuwa gashin daya sauka a bayanta,
Kamshin taji dakin ya dauka gabaki daya ko'ina ya kaure da wani ni'imtaccen kamshi bata kawo komai aranta ba tafara murzawa lallausan fatar jikinta mai kasa tayi da towel na jikinta tana shafawa kawai sai taji kamar ana tsaya ana kallonta a razane ta dago sukayi ido biyu. Gabanta yayi mummunan faduwa dan tadauka aljani tagani. Saurin jan towel din tayi yadawo yarufe kirjinta tayi kasa da kanta, sai yanzu take gane yanda tasan fuskar hoton da Dr tanuna mata cewa mijinta ne, Lallai Allah yayi halitta domin a filima yafi hoton kyau nesa ba kusa ba,
Sake murfin kofar yayi yajuya da baya sai dai ba dakinsa ya nufaba palour ya nufa ya zauna ya kunna kallo amma baya fahintar komai gizo kawai surarta take masa. Anya sajida kanta kalau? Ta kalli wannan yarinya tace zata aurawa mijinta? Bata tsoron abunda zaije yazo? Nisawa yayi ya lumshe idanuwansa bacci yakeso ko zai daukeshi amma yakasa saboda yasan irinsa bazai yiwu ya ganta haka kuma bacci ya daukeshi ba,
Sawwama saurin saka rigar bacci tayi ta kashe wuta ta kwanta,
Bude idanuwansa yayi harsun fara canja kala ya mike ya nufi dakinda take tanajin bude kofarsa tayi saurin runtse idanuwanta, a hankali yake tafiya amma sautin tafiyar yasa za'a gane cewa cikin kasaita yake yinta,
Dake dakin baiyi duhuba yabar kofar palour a bude ya karasa har gaban gadon cikin husky voice yafara magana, tashi kije kiyi alwala kidawo muyi sallah,
A sukwane ta mike bayan yanada alwala amma haka tasake yin wata, sallah yajasu sukayi sannan yayita yimusu addu'oi bayan sun idar ya juyo ya dafa kanta yayi addu'a sai bayan yagama ta iya bude baki cikin sanyayyar murya tace ina wuni?
Kallonta ya tsaya yanayi bai amsaba amma kamar yanda tayi masa kyau haka muryarta tayi masa dadi, jin shiru ya sanya ta dago tana dubansa, idonsu ya hade waje daya tayi saurin sauko nata kasa shikuam yazuba mata kyawawan idanuwansa yana kallonta, kara nanatawa tayi ina wuni? Sai a sannan ya amsa sannan yace jeki kwana babu musu ta hau gado taja bargo ta kwanta, yayi tsawon minti araba'in yana zaune yana addu'oi sannan shima yahau gadon ya kwanta,
A hankali yafara tabata ta runtse idanuwanta zuciyarta tanayi mata zafi na sanin cewa zai kwanta da itane kawai dan yana neman haihuwa amma badon wani shauki ba,
Mirginota yayi zuwa jikinsa kamshin turarensa ya sanyata lumshe idanuwa sai takeji gabaki daya kamshin yafi dadi datazo kusadashi,
Wata duniya daban ta fada zuciyarta tayi saurin dawowada ita duniyar asali,
Abubuwan da yake mata sun fara wuce tunaninta hawaye yafara gangarowa a fuskarta toh indai haihuwa kawai yake nema menene duk na wannan abubuwan? take tambayar kanta,
Wahala sosai Sawwama tasha hannun wannan bawan Allah, ta yabawa aya zakinta. Kuka sosai tayitayi dukda gakan bai rabuda itaba har saida ya cimma gaci, rumguneta yayi ajikinsa Kamar wanda yake bacci, yayinda ita kuma kuka takeyi maras sheshsheka Allah sarki Sadam ashe yana sonta sosai shiyasa yake tausaya mata amma yanzu data shiga hannun wanda baya kaunarta yanemi kasheta,
Ahankali ta zare jikinta ta shiga toilet ta yi wanka tadawo ta kwanta duk abunda takeyi yana jinta harta da kukan da tayi maganganun ne kawai baijiba dake azuciya tayisu, saida bacci ya dauketa kafin yatashi yakoma dakinsa acan yayi wanka, amma hankalinsa yana wajanta."
Bayan tatashi tayi Sallar asubahi tana gamawa ta kwanta wani baccin ya dauketa har 10am sannan tatashi tasamu masu aiki sun gama shirya mata komai, bata nemi ganinsa dan bata bukatar hakan shima kuma tasan yagama aikin daya kawoshi bazai sake nemanta ba sai wani,
taci abincinta ta koma daki."
Da asuba kafin yayi sallah dakin Sawwama yafara wucewa yadade akanta yana kallon wanda shi kansa baisan dalilin kallon ba,
Jin motsin rufo kofarsa bayan yafita ya tadata a bacci amma dake a baccine batayi tunanin wanine yashigo dakinba, ganin babu kowa a gefenta yasa ta kyabe baki wato dama zuwa yayi kawai ya kusanceta koh? Shikenan yagam bazaima iya kwana da ita daki dayaba, dama ko ba'a fada ba tasan ita ba sa'ar auransa bane ganinsa na yau datayi da raina kanta domun Allah ya hada masa kyau kudi ga aji da nutsuwa,
Sallan tayi sannan tadawo da kwanta da safema kafin ya fita dakinta yasake komawa nanma tana bacci yafice yakoma gidan Dr,
Sassafe Dr taganshi ya shigo da kallon tuhuna tabshi cikin kishi tace kaje ka kwana da ita shine sassafe zata taso ka dawomin nan?
Zama yayi gefenta hadeda rumgunota yace "nayi missing dinki ne shiyasa na taho sassafe, batareda ta sake fuskaba tace "kun kwana tare kenan?
A'a ni kadai na kwana aina fada miki bazan iya kwana da wata bayan keba yasamy kansa dayi mata karya, ajiyar zuciya mai karfi ta sauke da saida yabashi mamaki, toh dayace mata yakwana da ita baisan yaya zata dauki abunba."
Mikewa tayi tace ni zan wuce Asibiti saina dawo peck tayi masa a kumatu sannan ta kama hanyar tafice, bayan fitarta shima ajiyar zuciyar ya sauke."
Karfe uku na yamma Hajiya takirashi bayan sun gaisa take cemasa yakawo mata Sawwama, yace bayan la'asar zai kawota sukayi sallama,
Wanka ya sakeyi ya sanya farin shadda ya saka hula sannan yawuce gidanda Sawwama take,
Sawwama na zaune a palour na biyu tana kallo kamshin turarensa ya sanarda ita zuwansa dukda cewar tun jiya kamshin turarensa baibar gidanba, sallama yayi a hankali ya shigo ciki ta amsa ta dago kai ta saci kallonsa aranta tana fadin ikon Allah shi komai ya sanya kenan sai yayi masa kyau?
Karasawa yayi ya zauna a kujerarda take kallon nata a kunyace ta gidashi ya amsa yana mai kare mata kallo so kawai yakeyi ta dago idonta amma taƙi dagowa."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial18 Chapters
GENERIKA 0FFLINE
The world of Generika Online is a total disaster. When this VRMMO's servers closed, the Heroes who descended from Earth to protect it vanished—leaving its native characters to fend for themselves! Now, dungeons overflow with monsters. Job boards are plastered with unfinished quests. The World Devourer, endboss of a storyline that never concluded, unleashes wave upon wave of vicious mobs. Yet, life continues. Be they spun from data or DNA, humans are adaptable, and Generika's denizens scramble to pick up where absent Heroes left off. Witness the unexpected comedy of a defunct MMO's bit players as they adapt to this chaotic new world! ??? Author's Note: This webnovel is democratic as hell. Certain plot points may be determined by reader vote, so stay tuned, okay?
8 171 - In Serial8 Chapters
The London Phantom: A Superhero Webnovel
London is an old city. It has survived floods, fires, plagues and the man-made smog of industry. It has stood firm against the armies of Vikings, Saxons, Normans and the aerial might of the Luftwaffe. It has borne witness to dynsatic feuds, civil wars, military occupation and the sin of regicide. Through all these disasters the city has survived not through force of arms, though its walls were once the envy of the world, but through adapting to the times. Enemies become dependant on the city, and the wealth of the world that flows through it, and so become new allies. If the rulers change, then the city welcomes them with open arms, and open lines of credit. In this way the city seeks to preserve its ancient rights and position of power. Superheroes are a new phenomenon. The first superpowered man walked out of the Nevada desert in 1950, and the world was forever changed. Across the planet, men and women with exceptional abilities made themselves known. At first, they were little more than another source of fear in the era of Mutually Assured Destruction, but over time attitudes changed and the concept of the Superhero was created in the city of Los Angeles. From there the phenomenon spread across the globe; superheroes went from being feared arms of the state to a symbol of hope in these maddening times. Times have changed. Sixty years from the emergence of the first superhero, the City of London stands on a precipice. Two years have passed since the madman Fawkes nearly brought down the United Kingdom and the remnants of the Bow Street Runners, London's premier superhero team, are struggling to keep order in a city that seems on the brink of collapse. London stands on a knife's edge, with criminal organisations that once stuck to the shadows becoming more bold, and ancient powers from myth and legend making themselves known. Alexander Laszewski has recently 'awakened' and has become entirely unremakable, effectively making himself invisible to the world. He must use his newfound power to navigate a city on the edge of collapse. If only he could figure out how to turn it off.
8 60 - In Serial13 Chapters
D.W
Dungeon. War this story is about a young 10 year old boy who wanders into a dungeon after his childish father and reckless mother who travels with him who both though it was just a very deep cave.the result of this is the ultimatum with both the mother and father dying to a pitfall trap and the boy being left alone in the dungeon lost, till though wandering about the dungeon he reaches the worst place possible. the boss room!(inspired from other fiction -the slime dungeon- but inst connected in anyway)(mature language)
8 130 - In Serial11 Chapters
I AM GAMER IV
The continuing adventures of Lawrence Wrath who has been sent back in time to before there was the United States. Join Lawrence, Moon Flower, Billy, Patty, and of course Freak and Winston as they save the past by rewriting it! I Am Gamer is an Epic LItRPG and GameLit time travelling adventure.
8 56 - In Serial30 Chapters
Kookv oneshots
Once he reached the top there was a lot of wind and it smelt better "Who are you?" A masculine voice asks, Taehyung jumps up standing, He sees a black haired male sitting down while looking at him- Seperate worlds-------Top KookBottomTae-------Mentions of anything serious that can trigger people will be mentioned inside the stories
8 97 - In Serial201 Chapters
Bruised
"You poisoned me with your potion,Hexed me with your love and devotion. Now I lay in pieces, broken and brittle."Bruised is a poetry collection for the broken hearts and disappointed souls.It speaks words of wisdom, words of pain, and words of advice. Written by @cmitchellsACHIEVED RANKS -#5 in poetry#1 in poembook #2 in poetrycollection #3 in poetic#3 in sadquotes#1 in poem#2 in heartstrings#2 in poemcollection#1 in writing
8 195

