《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 73
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 73
Izuwa wannan lokaci Sawwama ta kwantar da hankalinta sai dai baza'ace babu wani abunda take damunta gabaki ɗaya ba, Mama da Baba suna iya kacin ƙoƙarinsu wajan ganin basu barta da wata damuwa ba duk wash buƙatunta suna ƙoƙarin biya mata, daɗin ɗaɗawa abunda ya ƙara ɗauke mata hankali shine ciwon Hindatu domin wata damuwar ta kori wata,
Kullum yawon asibiti sukeyi amma da zarar ansamu canji na lokaci ɗaya jiki zai sake dawowa sabo,
Ga cin kuɗi da jinyar take musu taimakonsu ɗaya Kuɗin dake account na Sawwama wanda Sadam ya tura mata dashi suke amfani, hakanma yanzu abubda yarage baida wani yawa."
Sadam yanacan jiki anata ganin canji yayinda dady ya daɗe da dawowa yabarsu acan sunata jinya, ya farfaɗo hhat yana magana kuma sam bai nunawa mummy komai ce domin a cewarsa iya wannan abunda yafaru dashi ma darasine ne daga wajan ubangi, Sawwama kuma ƙoƙarin yakiceta yakeyi da aransa dan bazai iya dawo da its cikin rayuwarsa yanzu a wannan hali dayake ciki ba, hhat indai yayi mata haka baiyu mata adalci ba,
Bayan haka bayaji ajikinsa mummy tayi shuryiwar da zata barsu su zauna lafiya, duk wani abunda yafaru yanaji laifinsa ne daya kasa daina sonta alokacin da mummy ta furta batason aurensa da ita, da yayi haƙuri da ita wancan lokacin to da bai jefata cikin damuwa ba toh amma yaya zaiyi? Bai isa jaa da abunda Allah ya rigada ya ƙaddara ba, ya ɗauki ƙaddararsa ya rumguneta Hannu bibbiyu kuma zaiyi koƙarin yin rayuwa batareda Sawwama ba awannan lokaci, bazai iya sake jefata cikin wani halin ba,
Zai nesanta kansa da its gwargwadon yanda zai iya hhat yaga yanda Allah zaiyi dasu,
Watansu biyar yasamu lafiya ya warke sai dai likitoci sun shaida masa abune mawuyaci ya sake haihuwa, amma basusan wani hikima na ubangiji ko yaya zaiyi dashi man gaba ba, bazasu ce masa kwata-kwata bazai haihu ba dan ni'imomi da ubangiji da yawa take,
Murmushi Sadam yayi a fili yafurta idan wannan ne ni banida damuwa dan yara biyu sun isheni rayuwa fatana kawai Allah ya rayaminsu."
Dady ta kansa yaje tafowa dasu likita yayi masa bayanin halinda ake ciki Dady yashiga tashin hankali matuƙa dagaske,
Bayan sunbar asibitin izuwa masauƙinsu yanda mummy da Abida ke zaune dady ya tarasu gabaki ɗaya ya dubi Sadam cikin tausayawa yace" cikin hikima da rahma ta ubangiji yau gashi Sadam ya miƙe kamar baiyi jinya ba, amma sai dai abunda likita ya sanar dani ya matuƙar ɗaga mini hankalina,
Ya dubi mummy yace"duk wani abunda yafaru da yaronnan ke kika jawo, duk faɗin duniya babu wanda ya takura miki agidan aurenki amma ke kin takurawa ɗanki, sunkuyarda kai mummy tayi dady yacigaba da faɗin yanason matarsa amma kin hanashi zaman lafiya da its gashi yanzu halinda kika jefashi, likita ya shaidamin abune mawuyaci ya ƙara haihuwa, Salati mummy ta sanya sannan tafashe da kuka dady zaro ido Abida tayi afili ta furta bazai sakw haihuwa ba?
Dady yace kwarai kuwa kuma kune sila keda uwarsa, nayi danasanin barinta danayi ta tilasta masa akan aurenki, aurenki bai zame mana alkahiri ba Aurenki bai ƙari ɗana da komaiba keba mace bace ta rufin asiri dalilinku ku biyunnan kun tarwatsa rayuwar ɗana kuma ban yafe muku ba, sakayyar abunda kukayi masa tananan biyowa baya banajin zan iya zama da ke ya nuna mummy sannan ya dubi Sadam yace "kai idan zaka iya zamada matarka ban hanaka ba, kuma daga yanzu duk wani hukunci daya shafi yarana babuke aciki zamu yankeshi ne daga ni sai su,
Advertisement
Bazan hanasu zuwa yanda kike ba amma bazasuyi rayuwa tare dake ba, domin son zuciyarki da son duniya zaisa ki jefasu cikin wani hali, dady yadubi Sadam yace Sadam ka yafemin nima nasan danawa laifin acikin abunda yafaru domin bana dakatar da mahaifiyarka ni atunanina bazata sanyaka aikata abunda zai cutar dakai ba, ashe ba haka bane hasashena baizo dai-dai ba,
Sannan kuma kaje kadawo da matarka in sha Allahu bazata sake takura maka ba,
Sai alokacin Sadam yayi magana yace "Dady kayi hakuri dan Allah karkace zaka rabu da mummy kamin wannan alfarmar, zaka iya mata wani hukunci na daban amma karla rabu da its kodan DARAJAR ƳAƳANTA, nasan mummy tayi ba dai-dai ba amma hakan bazaisa na yanketa matsayinta na uwa ba, matsayinta nanan so bazanso wani abun ya cutar da itaba, zanyi matuƙar jin baby daɗi idan kuka rabu ta dalilin abunda yafaru,
Sannan zancen Sawwama kuma Dady bazan maidata ba tacigaba da zamanta Allah yamata zaɓin daya fini alkahiri zanyi hakanne bawai don bana sonta ba saidan soyayyar danake mata zaisa na nisanta kaina da ita banason tasake iron rayuwar da tayi abaya, .kuma dady ni yanzu ba kamar da name ba zama da ita zai mana na cutar da it bazan iya jure ganinta ta cutu ba,
Zancen Haihuwa kuwa koda ace bantaɓa haihuwa ba wallhy bazan damuba na fawwalawa Allah komai shine majiɓanci duk wash lamurana, bare inada yara hhat guda biyu toh Alhamdulillahi nagode Allah da wannan baiwar,
Abida kuma bazan saketa ba can zauna da ita ahaka ko yaya zatayi kuma bazan taɓa sakinta ba dalilinta wannan abun ya faru So tazauna ta shuke abunda ta girba,
Kawo wannan lokaci kuka sosai Mummy keyi tama kasa buɗan baki ta nemi yafiya wajan ɗaya daga jikinsu, Allah idan yasoka da rahma ne zai baka ikon neman yafiyar laifinda ka aikata,
Ga mamakinsu kuka sosai Abida tasaka tana faɗin wallhy ni bazan zauna dakai ba haka kawai dannice bakaso saika cutar dani, ko cemaka akayi ni banason na haihune wallhy saika sakeni,
Dady ya dubeshi yace Sadam bazan tursasa makaba amma gani nake kaman rabuwa da itan shi yafi dan bazata yarda ta zauna ba, Ka sawwaƙe mata Allah zai baka wata wacce zata zauna dakai tsakani da Allah."
Ɗage kafaɗa Sadam yayi yace toh karta zauna mana dady! Ni narigada na yanke shawara tatafi bangon duniya nima bason zama da itan nakeyi ba kawai dai igiyar aurenne bazan sakeba,
Mummy jin maganganun Abida yas ata tsaya da kukan da dakeyi tace "Sadam ɗinne kikr cewa bazaki zauna dashiba dan lalura ta sameshi?, Abida tace kwarai da gaske bazan zauna da maras haihuwa ba,
Ƴar dariya Sadam yayi yace aini inada zuri'a ko yau na mutu nabar baya amma kefa? Ke koda ban bar kowa ba nasan na shuƙa abun kirki wanda zaiyita bibiyata, Rabuwa dake kuma bazanyiba zakiyita haukarki ki dawo ki daina,
Yanzu haka ni da kika ganni bama zanbar nan ƙasar ba haka zaku koma bandani,
Idan kinji zaki bisu saiki bisu amna igiyar aurena guda biyu na kanki,
Jin abunda Abida tafaɗi yasaka zuciyar Mummy ƙara karyewa tace lallai Abida ke butulu ce duk wannan abun danayi nayishi ne danke, amma yau kika rufr ido ni kika watsamin ƙasa anawa, tashi Abida tayi tabar wajan dan bazata iya mata rashin kunya ba bakuma zata iya tsayuwa taji kalamanda zata faɗa ba,
Advertisement
Murmushi Sadam yayi yace "mummy kingani koh?.na tabbata da Sawwama ce wani abun ya sameni bata dalilinta bama bazata taɓa iya guduna ba zata tsaya mu fuskanci koda wani iron ƙalubalene tare,
Mummy cikin muryar kuka tace "toh kadawo da ita ku zauna ta kula dakai, murmushi Sadam yayi yace "bazan iyaba,
Tsaki dady yaja yace "ashe bakida kunya? Dama aakwai rabarda zaki buƙaci taimakon abunda kike wulaƙantawa? naɗauka ƴar gidan talakawa batada wani abunda zata iya miki,
Nanma kuka kawai mummy tasaka,
Abida tana shiga ɗaki takira mahaifinta ta shaida masa abunda take faruwa, bala'i yahauyi yana faɗin ai kuwa bazata saɓuba nima inaso naga jikokina ko yaso ko yaƙi dolensa ya sakarmun ke."
Washe gari su dady da mummy suka koma gida akabar zallan Sadam da Abida,
Saida tayi kwana uku bata sanyashi a idanuwanta ba balle tayi masa rashin kirki tasa ya saketa."
Mahaifinta yanajin labarin dawowar su Dady ya kira mummy tazo yanason magana da its,
Mummy wacce ko kallon arziki bata samu wajan dady taje a ɗarare ta sanar dashi nema yayanta take mata, dady baiko juya ya kalleta ba yace "tace masa shi yazo ya sameshi,
Mummy ta sanar dashu yanda sukayi da dady, hhat gida yazo ya samu dady yace yanason takardar Abida,
Cikin rashin damuwa Dady yace aini aurenta ba akaina yakeba Sadam zaka samu da wannan maganar sannan kuma banajin zai iya saketa saboda duk halinda yashiga dalilinka ne da its yarinyar dakuma uwarsa,
Kai matsayinka na babba ka biyewa mata kuka aikata ɓarna ko nice son zuciya da nuna son naka afili, itakuma uwarsa dake shashasha ce kia ka nuna son ƴarka itakuma tabada nata ɗan toni a wajena ba haka abun yakeba, ina son ɗana sosai kuma zan iya komai dan tsaya masa, banajin yanda nakesonsa kanason ƴarka, So yanzu kowa zai nuna iron soyayayyar dayake yiwa nasa, awannan lokaci kome Sadam ya yanke ina bayansa kuma zan goya masa baya ɗari bisa ɗari,
Dady ya ɗaura da faɗin kana kallonsu suka aikata abunda suka aikata amma baka hanasu ba, gashi yanzu Abun yadawo man ƴarka, shiyasa akace kawa zai gina ramin mugunta ya gina dai-dai kansa."
Kaca-kaca sukayi da mahaifin Abida kafin yabar gidan, Mummy kuwa tsananin mamaki ya hanata cewa komai, wato ita suka maida doluwa tayiwa ɗanta rashin kirki amma gashi su afili suke nuna son nasu yarinyar,
yana fita yakira abida Yace ta tattaro tadawo zai turo mata kuɗin jirgi,
Abunda bata saniba shne Sadam ya ɗauke passport ɗinta kamar wanda dama yasan da faruwar hakaan"
Bayan dady ya shaida masa yanda sukayi da mahaifinta nanma yabi ya ƙwace wayarta iyakacin abunda ya barmata shine abunci,
Batayi gigin fitaba saboda tasan ƙasar idan ta kuskura ya fita ba passport aka kamata toh ba ƙaramin tashin hankali bane tattare da hakan."
Sai dare liƙis Sadam yake dawowa gida yana zuwa sai kulle ƙofar ɗakinsa yayi wanka ya kwanta bacci baya taɓa neman yanda Abida take."
______
Bayan sungama karin kumallo mama tadubi Baba tace baban hafsa naga baka shiryawa fita kasuwa ba, ko bazaka fita dawuri bane? Baba yace "yau gabaki ɗaya banajin can fita kasuwa jikin yarinyar man jiya da dare yabani tsoro gara mamana ta shirya mukaita Asibiti ke seki zauna agida duk yanda ake ciki ma buga miki ways, Mama tace "da katafi abunka kawai naga jikin da dama yanzu hakama bacvi takeyi, idan yaso zuwa jimawa saimu kaita asibitin,
Baba yace A'a jikin nata abun ba'a cewa komai ko naje kasuwa hankalina bazai ƙwanta ba gara nakaita da kaina,
Kicewa mamana ta shirya sai tabar yaran wajanki muje,
Mama tace toh tatafi ta faɗawa Sawwama akan tashirya sai suwuce asibiti,
Cikin ƙanƙanin lokaci tayi wanka ta shirya suka tafi,
Suna zuwa aka basu gado taimakon gaggawa aka fara yimata kafin likitan da take gani tazo,
Ƙwanansu uku a asibiti sannan Baba ya sanarwa ƴan uwansa da yawansu daga ciki zunzo dubata, mama da Sawwama ke karɓe-karɓe idan wannan tahuta sai wannan tazo,
Mama ce ta kwana a wajanta sai Sawwama tazo ta karɓeta Mahaifiyar Baba laraba ce tacewa baba yazo yakaisu asibitin itada Ikilima ƙaramar ƙanwarsu da Hindatu dan basusan wajan da yarinyar takeba,
Baba yazo yayi musu jagora har izuwa ɗakin sun samu likita na dubata hakan yasa suka zauna a gadon dake gefen na Hindatu,
Sawwama ta gaidasu suka amsa Baba cikin kulawa yace "sannu Sannu mamana Allah yasaka miki da.mafificin alkahiri, ko zaki koma gida tunda gamunan saimu ƙarɓeki?
Girgiza kai Sawwama tayi tace A'a baba ban daɗe dazuwa ba mama takoma gida,
Laraba tace toh madallah tare kuke jinyar kennan? Baba yace eh karɓe-karɓe suke da mahaifiyarta,
Laraba tace ita tunda ƴar uwarta takama jinya tadawo gida kenan? Dan kullum akan cemin anganta agida,
Shiru baba yayi dan duk cikin danginsa bai faɗa musu mutuwar auren Sawwama ba,
Jiki a sanyaye yace auren nata ne ya mutu shiyasa take gida,
Taɓe baki laraba tayi tace nasa arina ai ƙwarya tabi ƙwarya ina ƴarka in auren wannan mutanen?
Kaƙi jinika da zai rufa maka asiri ka zaɓesu gashi sun kwance maka zani a kasuwa, kuma auren ya mutu kaƙi faɗa mana mu maƙiyanka koh?
Hindatu ƙanwar Baba tace ko menene abun yayatawa a saki mama?
Dan lay kibar wannan zancen kibarshi yajida abunda yake damunsa yanzu,
Sawwama wacce kanta take ƙasa ko ɗagowa takasa yi,
Likitan dake duba hindatu wanda dama gun ɗazu su take sauraro, taso ta fahinci cewa Sawwama batada aure ganin yanda take zirga-zirga a asibiti bata sake gaskatawa ba sai yanzu,
cire abun kunneta tayi tadubesu face dan Allah ko zaku iyayin wane? Asibiti ba wajan irin wannan magamganun bane kubar maras lafiya taji da abunda yake damunta, dukansu suka miƙe laraba harna tuntuɓe zasu fice Dr tace Bandake Sawwama ki zauna ki kulata ita, kaikuma ka biyoni ta nuna baba."
Dukansu suka fice a ɗakin Baba yabi bayanta Sawwama kuma tazauna kusada Hindatu."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial21 Chapters
Hazelsong: A LitRPG Novel
Release Schedule: I will be moving to a set release schedule as of 1/1/2022. A new chapter will be released every Saturday at Noon EST. If I have time that week for a second chapter, I will leave a note on the Saturday chapter and post the second chapter on Sunday at Noon EST. An up to date character sheet for the MC Erik will also be posted on Sundays at 12:15 PM. If life happens and I am for some reason unable to write that week, I will post a blank chapter giving you an update on where I am with my writing. Saturday Noon EST: First weekly chapter Sunday Noon EST: Second weekly chapter (if I have the time) Sunday 12:15 EST: Updated character sheet Synopsis: Years after surviving a deadly accident, Erik struggles to come to terms with his painful disability. When offered the chance to playtest the world's first full immersion VRMMO, he wants nothing more than to retreat back into his secluded life, until he learns what Hazelsong really offers. An escape from the pain. Hazelsong is a world of magic and adventure, a place where friendships are formed, loot is won, and glory and fame are there for the taking. While the threats feel real and the stakes are always high, there is only one thing Erik is really in danger of. Forgetting which world is actually real. Story Themes: Hazelsong is a LitRPG novel that not only explores the fictional world of a realistic online fantasy realm but the life of a man suffering in silence from chronic pain and PTSD due to a significant physical injury and disability. Mental health is an important subject and we all know at least one person in our lives who has or is dealing with some form of mental illness. I plan on putting my best effort forward to represent these illnesses in a fair and accurate manner. Not as a cheap plot device to help make the protagonist more unique, but to help paint an accurate picture for those of us who have been lucky enough to not have to suffer in silence. About the Author: I am Ash Durra, general video game nerd and a connoisseur of fantasy and sci-fi of all shapes and sizes. Needless to say, I am not a professional author (B.S. and M.S. in Education, 8 years teaching). After really getting into LitRPG novels over the past several years, I found my way to Royal Road, which has inspired me to use my spare time to begin writing a story of my own creation. As this is a hobby, I am not writing and posting chapters on any kind of specific schedule at the moment, though my goal is to post on average 1-2 chapters a week. I am incredibly excited to share this story with others as I write it, and I look forward to any constructive feedback about how I can improve in my writing.
8 92 - In Serial17 Chapters
The Wired Phantasmagoria Grimoires
In a time not so far from our own, in a city not so far from you, strange things are happening. Deaths, monsters, mysterious and poetic final letters, madness, machinated abominations... Is this all the result of one conspiracy? Or, has this gauntlet been wrought by a collective, unconcious desire for danger, a feral and instinctual life in the food chain? What is happening? What, if anything should we do to stop it? Who will rise in these times, who will crumble, and who will even notice a difference? This is but one of my Serial Experiments in fiction writing.
8 133 - In Serial63 Chapters
Intercosmic
Space, the final frontier, or so we're told. The problem is things can never seem to be final in the vast never ending reaches of space. Efrem Gray has been a good soldier for nearly a decade and a routine mission to the planet Xioshaa to stop an ever growing civil war was nothing but another stop for him. Things go south when his team is ambushed and stranded in a jungle, left to argue amongst themselves about the best way to survive. Despite the misadventure, Efrem makes it out alive, but he doesn't come back the same. Finding a place in this great big galaxy of ours is never easy. Unfortunately, Efrem has to start from scratch before he can find not just a place to call his own, but a new life beyond what he thought he knew.
8 60 - In Serial54 Chapters
#2: Mister Sweet Talker || Beomryu √
Mister Series 2 of 5 taglish epistolary completedJust because of his consistency and bubbly personality, she started to get interested on him that it came to the point where she tried to entertain him, just so she can know if the guy will still be the same or not despite her cold treatment towards him.
8 146 - In Serial34 Chapters
Revival of Undead King
Around 1000 years ago, there was an Undead king who made a winter when it's suppose to be summer. The winter called nightmare winter and countless lives taken thanks to it. People from all races gathered to defeat the Undead king and stop the winter. However, the price for that wasn't small and many people died. If not for the Dragon king arrival. They would be dead. the between Undead king and Dragon king went fierce. In the end, the winner was Dragon king. The Undead king is gone and nightmare winter is stopped. However, that is a history written by false historician. The truth is hidden behind the darkness and there is always a reason behind it. As the present is living in calm before storm. A young man from a certain village, Evan must face his unavoidable destiny.
8 81 - In Serial12 Chapters
False Assumptions
After running away from her last foster care Mariah was living on the streets for a few years. She makes a decision that almost lands her in jail but instead she gets taken in by Ms.Valentine the best thing to ever happen to her...Chris and his siblings have had a hard life, but one things for certain his mom always made a way. Helping his mom take care of his siblings and working to help pay the bills, he had to step up early but he never complains...Chris see's Mariah as a stuck up brat, who's never had to worry about anything in her life. She sees him as an arrogant asshole, who can't admit when he's wrong. After being forced to work together on a project they realize their assumptions are way off.
8 183

