《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 72
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 72
Taɓe baki Abida tayi haɗeda sakin murmushi sannan ta raɓa ta gefenta tawuve, saida ta isa man kujera ta zauna sannan tadubi Sawwama wacce itama tajuyo itan take kallo,
Tsawon lokaci suna ahaka Sawwama afusace tace idan bbu abund ya kawoki zaki iya fitarmin a gida bana gayyar rashin hankali da rashin imani,
Abida harta buɗe baki zatayi zaki sai kuma tayi shiru, dariya ta sanya kamar wata mahaukaciya tace Au gidanki? Wai gidanki kikace? Labari bai iso gareki ba kenan? Ai yanzu ni dake matsayinmu ba ɗaya ba kuma nan ba gidanki bane,
Sawwama cikin rashin fahimtar abunda take nufi tace koma menene naji amma tashi ki ficee,
Na ɗauka kinyi danasanin abunda kika aikata ne yasa kima biyo sawu ki bada haƙuri ashe ba haka bane rashin hankali ya kawoki, toh bazan ɗauki rashin hankalinki ba dan haka kificemin agida gun dawuri,
Abida tace sai dai ke ki five amma baniba dan yanzu nice mallakin gidannan dakuma wancan gidan danni kaɗaice matar Sadam,
Sawwama tace"shiyasa nace kin fara hauka dan haka kifita kibani wuri,
"Au wai baki yarda ba? Cewar Abida hannu tasaka ajakarta taciro wata takarda ta mƙa mata, ƙin karɓa tayi Abida ta ɗage kafata tace "baki iya karatun bane I guess so barina karanta miki,
Ni Sadam na saki matata Sawwama saki ɗaya
batareda ta aikatamin wani laifi ba sai dan bin umarnin da zai zame mana maslaha gabaki ɗaya,
Sawwama na ƙarasa jin haka ta isa wajan da sauri ta fauce takardan kuma abunda abida ta karanta shine arubuce ajiki kuma tabbas wannan rubutun Sadam ne,
Cikin rashin Gaskata abunda tagani ta juya ga Abida da kallon tuhuma, Abida tace "mijinki zaki kira ki tabbatar danni nagama aikina,
Wurga mata Sawwama tayi face shirinki bazai taɓa aiki akainaba kuma nasan Sadam bazai taɓa sakina ba har abada dan haka kitashi ki fita,
Miƙewa Abida tayi ta shure takardar gefe tace "ki ajiyeta ke zata yiwa amfani sannan please idan antashi tafiya kar ayi mana sata dan nasan kayan Mijina ne ya saya
ficewa tayi bayan gama faɗin hakab tabar Sawwama jiki rawa,
Tana fita Sawwama ta ɗauki wayarta tafara kiran Sadam amma bai shigaba takira yafi say ashirin duk baya shiga, zama tayi tana kuka
Abunda yafaru ne yasa Mummy ta saka ya saketa kenan ita akaiwa laifi kuma ita za'a hukunta?
Adakeka ahanaka kuka kennn,
Har dare Sawwama takai tana kiran layinsa amma bai shigaba
Washe gari taga zaman bazai kaita ba ta ɗauki yaranta da takardar tawuce gida,
Bayan sun gaisa da mama take cewa wanu abunne yafaru naganki duk kin koɗe, kuka Sawwama tasaka tabawa mama labarin abunda yafaru mama ta zauna jigum takasa cewa komai,
A lokacin takira Baba yadawo daga kasuwa suka shaida masa abunda take faruwa Baba yakarɓi takardar ya karanta sannan yace nagodewa Allah daya kasance ba laifin komai kikayi masa ba, Allah ya zaɓarda mafi alkhairi ki kwantar da hankalinki kishiga ɗaki kihuta,
sai kuje ki ɗebo kayan sakawanki mu zuba ido muga hukuncin ubangiji."
Sati guda kenan da faruwar wannna lamari amma sam wayar sadam bata shiga,
Mummy har izuwa lokacin tana gidansu, lokaci-lokaci Sawwama tana neman wayan Sadam amma baya shiga,
Advertisement
Har yanzu tana cikin damuwa dan gani take idan baby Sadam bazata iya rayuwa ba,
Wani lokacin kuka zata zauna tayita yi,
Mama takan rarrasheta wani lokacin kuma idan haushi ya cikata saita barta tayita kukan,
Ranar ma haka tashirya zata fita kai Hindu Asibiti dake jikinnata har yanzu tashiga sanar da ita akan tatafi, ta sameta tanata rausa kuka, mama ta tsaya akanta tana faɗin Hafsa haka zamuyi dake?
Kin takura kanki kin hana kanki sukunu akan namiji idam babushi bazakiyi rayuwa ba kenan?
Ke bazaki ɗauki Ƙaddara ki fawwalawa Allah komai ba? Shin wannan kukan zai sama miki mafita ne?
Toh barina faɗa miki ke yanzu uwa ce yakamata ki zama jajirtacciya sakin sure ba akanki aka fara ba, idan da rabo atsakani zaku komawa aurenku, amma kukanku bai is aya canja rubutaccen all'amari ba, ki sawa kanki salama ki tsaya ki kulada yaranki su kansu sun rame, Duk kinbi kin fita hayyacinki,
Sharae hawaye Sawwama tayi tax "mama ba haka bane ni rashin samunsa da ake a ways ne abun take damuna kar wani abunne ya sameshi,
Mama tace ki kwantar da hankalinki hafsa in sha Allah baby abunda ya sameshi shima yana cikin zullumin rabuwar aurenku ne shiyasa yayi nesa daku,
Kibashi lokaci in sha Allahu bbu wani abunda yafaru dashi,
Murmushin yaƙe Sawwama tayi sannan tace fita zakiyi yanzu? Mama ta amsa da faɗin Yauce ranar komawarmu asibiti da Hindatu yanzu hakama tafiya zamuyi,
Miƙewa Sawwama tayi tace "barina shirya muje tare, mama tace "ke ki zauna bazamu bar gidan babu kowa ba,
Sawwama ta girgiza kai face A'a mama mutafi kawai dannima zaman nawa ni kaɗai bazanji daɗinsa ba,
Mama tace "toh kimtsa kifito karmuyi latti mikimin wannan yaron na goyeshi saiki goyi ƴar uwarsa, mika mata hamdan tayi itakuma ta shirya ta goyi hameeda suka nufi asibitin,
Wash gwaje-gwaje aka sake rubuta musu sannan aka basu ranarda zasu kawo sakamako,
Sawwama duk ita tayita jigilar biyan kuɗi da sauransu saida sukayi gwaje-gwajen sannan suka koma gida mama nata mita tana faɗin "yanzu dai zuwa asibiti yazama wahala sai gwaje-gwaje kawai suke rubutawa yarinya tanata jin jiki amma bazasu bata wani abun da zata dan samu dama-dama ba, wannan ai idan yazo da ƙarar kwana sai arasa rayi,murmusawa Sawwama tayi tace "ai mama idan ba'ayi gwaje-gwajenba ba'asan akan wani irin magani za'a ɗaurata ba, sai sunyi kafin su game abunda take damunta, taɓe baki mama tayi tace uhmm,
Sun dawo gida agajiye liƙis bayan sun huta Sawwama ta ɗaura musu abinci,
Bayan tagama tacigaba da kiran wayar Sadam amma taƙi shiga haƙura tayi ta kira ta ajiye wayar zuciyarta cikeda damuwa fall,
Tausayin kanta takeji tana tunanun shin zata iya samun mutum irin Sadam mai sonta da tausayunta?
Hindatu sunata komawa Asibitu an gano wani ciwone a zuciyarta sun daurata akan magani da saka ran ciwon zai baje idan kuma hakan bata faruba sai dai aiki,
Sati biyu da fara shan maganunta anga sauyi sosai."
Tun suna ganin lamarin kamar wasa yanzu abun ya wuce tunaninsu,
Suna jira Sadam zai kira ways yaune? gobene?
Shiru saida akayi sati uku,
Mummy mahaifanta jin takaicin abubda t aaikata ya sanya ko neman dady basuyiba,
Yanzu haka zaune take da wayarta a hannu ta rafka uban tagumi, wata dattijuwar mata tafito tana ta tsaya akan mummy dake zaune a babban fall da rafka tagumi,
Advertisement
gyaran murya tayi mummy ta kalleta, murmushi tayi irinna manya tace ai baki fara damuwa ba da saura,
Kuka mummy ta sake tace ni momma da wane zanji
da ɓatan Sadam ko dadynsu da yaƙi saurarena kema wajanki danake tunanin zanji sanyi kullum magana kike yaɓamin,
Dariya ƴar dattijuwar tayi tazauna idonta naga Tv kamar bazata tanka ba sai kuma face "aishi ba yaro bane zai dawo kawai ya raba kansa da fitinarki ne, kin tabka babban kuskure kina ƙoƙarin gyaran auren wata ke kina shirin tubuƙe naki, gashi yaronki ma ya nesanta kansa dake, idan kina ganin kin ruguza rayuwar aurensa ko naki kika ruguza,
Banda rashin basira ke kina ƙuntatawa ɗanki kina farantawa ran wasu gashi kina gani dai yayanki tunda kikazo gida ko say ɗaya bai tambayi daliliba baima damu ya saniba tunda shi aurrn ƴarsa ya gyaru na kowa ma ya ɓaci,
Bansan a'ina kika ɗauko wannan baƙin halin naki ba ni ai kina kallo nida matan ƴaƴana kamar ni na haifesu,
Amma ke kin fitina yara gabaki ɗaya kin hanasu zaman lafiya shiyasa nace miki ai bakiga komai ba sakayya tananan agaba,
Muƙus mummy tayi tanajin mahaifiyarta nata yimata faɗa tasan ko menene ma yafaru toh ita ta jawowa kanta."
A halin yanzu duk wani wanda yasan da ɓacewar Sadam yana cikin matsananciyar tashin hankali domin kuwa wayarsa Sam bata shiga dady ya saka har garinda yaje an nema ba'a sameshi ba,
duk abokanansa an kirasu bbu wanda yasan yan yake, har najeeb duk kusancinsu amma bai sanar dashi yanda yake ba,
abun da yaƙici yaƙi cinyewa dady da kansa ya tafi garin nemansa a ganin babu yanda ba'a bincika ba ba'a sameshi ba yasa dady yace ayi tracing na layin man ma akashe iyakacin wajanda aka kashe layin ya sanar dashi daff da za'a shigo gari,
Police dady yasa a maganar suka nemansa har yanda layin yadaina aiki sunje, wajanma ba wajan mutane bane jejine daff da za'a shiga gari,
daga ƙarshe Asibitoci suka shiga dubawa cikin ikon Allah kuwa sami Sadam yayi accident tsawan sati uku bai farfaɗo ba sannan kuma babu wanda yazo nemansa yasa suka barashi basu wani damu dayi masa magani ba,
Dady har kuka saida yayi ganin halinda Sadam yake ciki yana can wani ɗaki kamar maras gata ɗakin hhat wani wari take da dukkan alamu marassa lafiyan dasuke wannan ɗaki ba wani cikekken kulawa suke samu daga likitocin ba,
Dady yayi faɗa kamar me gabaki ɗaya likitocin suka taru haƙuri kawai suke bashi sanin cewar idan magana tayi nisa su kansu zasu samu matsala saboda sakacin da sukayi da maras lafiya,
A ranar ya nema transfer suka koma gida kai tsaye babban asibitin dake garin aka wuce dashi,
likitoci sun taru sunyi iya bakin ƙoƙarinsu amma basu samu ya farfaɗo ba,
Sun alaƙanta hakan da rashin kula daya samu alokacin daya samu hatsarin, bai samu immediate treatment ba,
Satinsu biyu a asubiti amma baby wani canjin kirki mummy tazo tayi kuka harta gaji tayi danasanin abunda ta aikata,
Ba'a wani ganin canji gameda lafiyarsa hakan yasa likita yabawa dady shawara akan yafita dashi ƙasar waje domin ayi masa magani,
Kullum mummy a asibiti take wuni wajan Sadam amma dady ko waiwayen yanda take bayayi, yace shi bazai hanata jinyar ɗanta ba, zai barta tazo tayi jinyarsa kodan tayi hankali nan gaba."
Abida ma tashiga tashin hankali ba ƙarami ba ganin halinda suka jefa Sadam, kullum zuwa asibitin kusan koda yaushe tana tare da Sadam ko fita batayi sai dare take komawa tabar mummy."
________
Yanzu damuwar dake damun Sawwama taɗan ragu dan har tana fita suyi hira da mama kasancewar Hindatu babu lafiya koda yaushe tana gefrnta,
Kamar kullum yauma suna zaune da mama cikin gida sai sukaji Sallamar Halima,
Tana ganin Sawwama ta ƙaraso da sauri ta zauna tana faɗin yaya Sawwama kema ashe kina hanya naji daɗin ganinki, inata so naje gidanki amma a cikin satinnan zan zoni, murmusawa kawai Sawwama tayi,
Mmaa tace Halima dududu yaushe akayi auren da har zaki fara yawo? Har yaushe akayi bikin yabarki kika fara fitowa, Halima face wallhy Mama nayi ƙoƙari kusan wata biyu fa kennan ban ganku ba,
Mama wata uku akeyi kafin a fara fita a zamanin yanzu kenan ma zamanin iyayanmu kuwa sai sun shekara kafin suje gida, Dariya dukansu suka saka sannan ta gaida mama da Sawwama, ganin Hindatu a kwamce yasa ya tambayi abunda ya sameta, mama ta faɗa mata kuka Halima tayitayi wai ba'a sanarda itaba, haka dataji mutuwar auren Sawwama ma saida tayi kuka, tace Yaya Sawwama zamanku keda Yaya sadam gwanin sha'awa yana sonki sosai, amma wannan shu'umar matar saida ta rabaku in sha Allah baku rabuba sai sun koma, mama tace kull Halima karna sake ji uwartasa ce shu'uma, Halima tace toh mama fisabillahi me yaya Sawwama tayi har haka da zafi?
Rabuda its zata gani a ƙwaryarta amma banaso nasakeji kin aibatata, Kubarta da halinta amma uwa ce a girmama ta kota wannan dalilin, Ko karamci irinna Sadam kaɗai ya isa ya wanke laifin mahaifiyarsa, duk wani abunda ta aikata kanta ta cuta abarta da fitowar rana da faɗuwarta zataga sakayya akanta in Sha Allah."
Sai dare sannan Halima tatafi."
maganin Hindatu yaƙare hakan yasa Sawwama ta shirya domin rakata ganin likita,
Likitan da suka saba gani suka samu, macece da bazata wuce shekaru 36 ba tanada kirki sosai,
Bayan sun gama ganin likita ta rubuta musu magani acikin asibitin suka says sannan suka fito,
Suna daff da fita daga asibitin taga su mummy suna ƙoƙarin shigowa, saurin juyawa gefe tayi dan bataso su ganta, aranta idan tace batajin zafin mumny tayi karya,
Tana ganin motar tawuce tajuya suka koma gida."
Da mummy dady da abida aka tafi can ƙasar amma dady zai dawo bayan yaga yanda treatment ɗin zai wakana na wani lokaci."
Yanzu jikin Hundatu yana ɗan tashi lokaci-lokaci duk da cewar tana ƙarban magani,
Yanzu harta kaiga ana basu gado a asibiti a sallamesu idan jikin yatashi a sake dawo da its,
Likitan na nuna musu kulawa sosai barinma ga Sawwama da yaranta,
Tanason yara sosai koda yaushe tashiga asibitin saita ɗaukesu."
Wani lokacinma offices take wucewa dasu."
watansu Sawwama Huɗu da rabuwa amma hhat yanzu mikin son Sadam yananan acikin zuciyarta
Kuma har yanzu wayarsa bata shiga, dady akai-akai take mata aika amma ba'a taɓa sanarda its halinda sadam yake ciki ba."
Twins kuma sun cika shekara dan shirin yayesu ma takeyi dake bawani shan nonon sukeyi ba, abinci kuwa kowani iri ci sukeyi."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial21 Chapters
Digital Demons
Dispite how it sounds, activating the device that melted her brain was probably the best thing that ever happened to Blade, a former member of the slum districts. Though the process was extreme, instead of endless nothing or eternal suffering our heroine finds that her death was just a nessisary part of the digitization of her brain. Now she has joined the millions of rich and powerful who gave up their lives for a second chance in the fully imersive game world of Templa. Not one to be detered by a challange (or her death), Blade chooses to start in the unforgiving Demon Lands. This is known to be the hardest starting zone in all of Templa, but those who make it through are some of the best players in the game. Does Blade have what it takes? Chapters are always 2000+ words with no relese schedual at the moment. Thanks for reading! -------------------------------------------------- Droped due to poor quality.
8 181 - In Serial7 Chapters
Chromanorel
Go to work. Stare at your screen. They'll steal your soul to power their world. Lauren was having a bad week at work, and that was before a giant dragon turned up and attacked her horrible boss. Running from the fire-spewing beast, she escapes into a strange tunnel in the bathroom. Where does it lead to? Has she shaken off the dragon for good? And has she really gained the terrifying power of harming people by thought? Lauren is about to find out that everything she thought she knew about the rat race is wrong. Lost and confused in a strange new world, she stumbles into a quest that threatens to take everything she has... including her life. Chromanorel will be updated every Wednesday, and sometimes on other days if I have time. Author's note: In case you're wondering about the -"our"s and -"ise"s, they're because I'm British :)
8 147 - In Serial12 Chapters
PROTOTYPE
Alex mercer wakes up without his memories and mysterious powers, follow his quest to find out who he was and more importantly what he has become.
8 96 - In Serial18 Chapters
The Assassin System
In the modern - era of 20XX. Gamers all around the world were on anticipation of the new 'realistic' MMORPG. Astral Fantasy. It featured tags like 'swords and magic' and 'sci-fi'. In short, on Astral Fantasy you could be anyone you want. Be it the heroes from Fantasy Novels or those Space Mercenary on the Sci-fi genre. Now, Lilia Evergreen, a famous gaming streamer, became a beta tester for the anticipated MMORPG, which of course gained the envy of many. On the day of its beta release however, she suddenly heard a voice in her head. *Initiating power up* Amidst her confusion at the voice on her head, she suddenly noticed one thing. "Why does the sky have Hexagons on it?" Disclaimer: I do not own the photo. Credits to Shadowfox on pinterest. https://www.pinterest.ph/pin/743094007247328772/?nic_v2=1aRgsUGv8
8 266 - In Serial7 Chapters
(DEMO) Colorless vol.1- Phantamoire Enigmata
This is a demo volume consisting only seven chapters. The sole reason of this publication is to show the world a glimpse of the project. Therefore, the final quality of the product will be lot more refined and polished. This demo might get deleted from RoyalRoad after the actual publication. Synopsis: "Knights wearing their shining armor serving righteous justice riding their glorious horses." We all have heard that story- Heroes who do the right in the purest way without any tampering. But, is it really that easy? Is the world and it's heroes really that pure? After all... fairytale is just a lie. I might be the first author in the world who despises writing. I haven't read any story books or novel in my entire life but children's story book (not even ten of them). So, why do I write? Simple answer- the story. Inexperienced I may be but I believe my project and it's quality. The actual story will be posted somewhere in 2019. The story will be devided into 7/8 volumes and 90 (approx.) chapters. I have been working on this project for 1 year now. It took me 5 months to finalize the concept and plot, 7 months for the story and it's already been 6 months in writing along with 2 times of total revamp.
8 194 - In Serial7 Chapters
The Emperor's Least Favorite Daughter is Kicking Ass
"So, The only person I could have reincarnated into is this loser princess?" "You are to be executed at the dawn of today." "Are you serious, you are going to behead me, your own daughter!" Anna a ball of mischief and grief was shoved into make belief world where everybody wants her dead.
8 97

