《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 71
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 71
Wata iriyar kwala ya challa wanda yasa Sadam dake ƙoƙarin shigowa faro saurin neman ɗakin dayakejin ihun,
Da gudu Sawwama ta ƙarasa wajan ta ɗagoshi ya buga kansa jikin drawer sai jini yakeyi gashi ya shuɗe harcensa har ɓari yakeyi saboda azabarda yakeji arikice Sawwama ta ɗagoshi tariƙe ajikinta,
Its kanta Abida saida ta rikice ganin yanda jini yake zuba, dasuari ta ƙaraso wajan takai hannunta zata taɓa yaron Sawwama cikin zafin rai ta buge hannun,
Miƙewa tayi da yaron ajikinta tana niyyar Abida abida tabita itama arikice tana shirin ƙara taɓa yaron Sawwama ta juya a zafafe ta wanke fuskar Abida da mari hakan yayi dai-dai da shigowar Sadam ɗakin, Sawwama na kuka ta raɓa gefensa zata wuce, a ɗimauce ya tsaida ita ganin jini duk ya ɓata kayanta ga Hamdan dake ta tsala ihu a hannunta,
Hannu yasa ya karɓeshi yayi wane da gudu sukaci karo da mummy wacce take shirin shiga ɗakin jin yanda ihun yaron yayi yawa,
Gabaki ɗayansu suka wuce zuwa asibiti banda Abida da aka bari a gida, jinin ya tsaya an yinasa inki kamu uku a wajan sai aka rufe da bandage ana gamawa aka sallamesu, Saida Sadam yayita rarrashin Sawwama kafin ta yarda aka koma gidan mumny da ita, Abida kuwa ido yayi tsuru-tsuru daowarsu kawai take jira,
Sun koma alokacin dady shima ya dawo, anata jajantawa dady yace har ya akabar haka tafaru, mummy wacce kamar tana wajan abun yafaru tacewa dady ai yaron dama yamada ƙiriniya kuma sands nacewa uwarsa ta kula dasu tashiga ciki tabarsu yaje yajiyawa kansa ciwo,
Dady yace subhanallahi Sai kidinga kula idan Allah yabaka yaro irin haka takatsantsan akeyi, hawayen take zuba a fuskar Sawwama, Sadam yace banajin hakane tafaru dady dan makamancin hakan baitaɓa faruwa ba Sawwama ya akayi haka?
Sawwama wacce take kuka ƙasa-ƙasa face nashiga toilet yin alwala fitowana naga Abida ta sanya ƙafa ya wullashi gefe, Sadam yace jikina yabani hakan saboda nasan Sawwama da wuya tayi zafin zuciya irin haka batareda wani kwakkwaran dalili ba,
Mummy ta dubi Abida tace ya akayi haka tafaru? Ke kika tureshi, da sauri Abida ta girgiza kai tace bani na tureashi ba mummy zuwa wajan yayi ya buge ita kuma tana zuwa sai tahau kaina harda marina atunaninta ni nabige mata yaro, tayi maganarne cikin rashin gaskiya wanda dady da Sadam sun fahimci hakan amma mummy son kai ya rufe mata idanuwa,
A fili ta furta mari! ta mareki akan yaron dan tana hauka,
Dady yace dakata kamar yanda bamunan Tature yaron haka bamanan itama ta mareta so acikinsu mu ɗauka cewa kowa yafaɗi son ransa ne abarsu ahaka bbu wacce zaki zauna akan maganarta kiyiwa ɗaya faɗa idan hakane dukansu haɗasu zakiyi ki musu faɗa ita ta wulla mata yaro itakuma ta mareta,
ke kuma ya nuna Abida har indai kinsan kin wulla yaronnan kiji tsoron Allah shi yaro ba'a masa mugunta dan gaba bakisan wazai taimakeki ba, yaro baisan komai ba, har indai ya tabbata kin tureshi to tabbas baki kyautaba dan wannan abun ko ƙara takaiki mu bazamuga laifinta ba dan kinyi ba dai-dai ba,
Advertisement
Mummy tace dadynsu ba'a an tabbatar ta cewa ita tatureshi ba amma kanata yimata faɗa, its wacce ta mareta ai itama yakamata kayi mata faɗa tunda gashi har shatin hannunta yafito a fuskarta ta faɗi tana juyoda fuskar abida wanda take kumbure da marinda Sawwama tayi mata"
Dady yace koma menene its tasaya da kuɗinta danni bazan yi shari'a datake ba dai-dai ba yaro dai gashinan yanda ta kasance dashi ai abunda tayi tsantsan rashin kirki ne idan da kara ɗan Sadam ai nata ne saita rumgumesu hannu bibbiyu itama Allah yakawo mata nata,
Abida sai tsuru-tsuru takeyi da ido jin abunda dady ke faɗa,
Faɗa dady yayita musu sannan yace sutashi su tafi,
Alokacin Sawwama tamiƙe ta ɗauki Hameeda hamdan yana wajan Babansa yana bacci a mota tajirashi yazo, suna shirin tafiya saiga abida man tafito Harara Sadam ya watsa mata yace badai motata tunda zaki iya halaka ɗana nasan nima wata rana zaki halaka ni kiwuce kitafi amma batareda niba, yana ƙarasa faɗi yaja motarsa yabr wajan,
Cikeda ƙunar zuciya Abida ta bisu da kallo har suka wuce, komawa tayi ciki da kuka ta shaidawa mummy abunda yafaru, Mummy ta ɓata rai face aiko me yayi miki ke kika jawo bansan cewa rashin hankalinki har yakai haka ba, ke a kullum ina nuna miki yan zakiyi ki ƙwace mijinki amma daɗa taɓarɓare all'amura kikeyi, sai kije ni yanzu bansan abunfmda zanyi miki ba ki tashi kije gida kibashi haƙuri,
Abida jiki a sanyaye takoma gida."
Sadam kuwa rarrshin Sawwama ya tsaya yi dan yasan tana cikin wani yanayi a duk lokacin daya kaita gidan mummy sai an samu matsala gashi wannan matsalar tafi kowacce duk kawaicinda take dashi amma yau yaga zallan ɓacin rai a tattare da ita
duk sanadin faruwar hakan kuma Abida ne yau bayajin zai iya ɗagawa Abida ƙafa sai ya hukuntata da abunda ta aikata,
Sai dare sosai kafin yabar gidan, yabarsu Hamdan sai kuka take yana shiɗewa ko bacci yafara sai yafarka arazane yasaka kuka,
Yasamu Abida agida kamar yanda yayi zato yana shiga ko zama baiyiba yace "Abida kitafi gidanku bazan iya da halinki ba duk ranar da kikaji zaki iya zamadani da matata da ƴaƴana cikin kwanciyar hankali saiki dawo,
Da mamaki Abida ta kalleshi tace natafi gidanmu? natafi gidanmu fa kace? kai kanka kasan wannan zance ne babu yanda zanje, Sadam yace tabbas saikin tafi ko kin ƙi ko kinso, Shewa Abida tayi face ɗan adam butulu ko kamanta da bazar mahaifina kake rawa? Aikinda kake taƙama dashi make cida wancan ƴar talkawan da ƴaƴannaka duk sanadin mahaifina ne, nasan bazaka iya rabuwa daniba saboda gobenka ko Abaya dakaji inacewa ka zaɓa koni ko waccar shashashar matar taka ina faɗin hakanne dan nasan dole ka zauna dani dan gobenka na hannuna, babu yanda za'ayi karabu dani mahaifina yabarka ayanda kake yanzu,
Dan so nasan cewa its kakeso amma ni nice ƙarfinka dan idan bbu kuɗi rayuwarma kanta bazata yiwuba,
Ran Sadam yakai ƙololuwa wajan ɓaci wato its tana tunanin duk abunda takeyi kuɗin mahaifinta ne yasa bai rabu da ita ba?
Advertisement
Cikin ɓacin rai yace na sakeki saki ɗaya kifice kitafi gidan mahaifin naki kuma aikinma ajiye miku shi zanyi kiga ko zan rayu ko akasin haka,
Cikin faɗuwar gaba Abida tace mene ka sakeni? Ka sakeni fa kace?
Nashiga uku ta sanya hannu akayi riƙe ƙafafunsa tayi tana kuka yaja ƙafarsa ya kalleta yace har indai kuma kika kuskura kikaje gidanmu saina ƙara akan ɗayan da nayi miki,
Juyawa yayi ya fuce gidan Sawwama ya nufa itadai taga ransa aaɓace amma bai sanarda abubda yafaru ba, ta tace masa ya koma can yace mata bazai iya barinsu da yaro cikin wannan halin ba,
Ran mahaifin Abida yayi matuƙar ɓaci ganin yanda Sadam ya sako masa yarinya da dare, Sassafe ya nemi ganin mummy, itama kanta mummy ranta ba ƙaramin ɓaci yayiba,
Tana gidansu Abida ta kira Sadam kamar bazaije ba sai kuma yaje faɗa sosai takeyi hhat saida abun yabashi mamaki dan tunda take da mummy bata taɓa yimasa irin wannan faɗan ba,
kuma a wajan ta sanya ya mayarda Abida, badan ransa yasoba ya maidata, Takarda ta miƙa masa da mamakinsa sai yaji tace itama waccar kayi mata saki ɗaya ɗagowa yayi jikins ahar raw ayake yace Mummy mai tayimin da can saketa?
Mummu ta ɓata rai tace itama Abida mai tayi maka daka saketa? Girgiza kai yayi yace kiyi hakuri mummy bazan iya ba, Allah bazan iya rabuwa da matata ba,
Mummy ciki tsananin ɓacin rai tace hanya ɗaya ce da zata sanya na yafe maka abunda nayi maka itama ka dawo da igiyar aurenta biyu kamar na Abida
Sadam yace mummy dan Allah dan girman Allah mining rai wallhy bazan iyaba,
Mari mummy takai masa tace saketa saketa yanzu nace, ka saketa saki ɗaya tall ni can riƙe takardar a wajena ba lallai saika nuna mata ba ranar dana huce dance kadawo da its amma dole sai igiyar aurensu ya dawo ɗaya,
Idan kuma ba haka ba toh can saka ka zaɓa ko ni ko its, hhat indai its zaka zaɓa kasan sauran dan yafeka zanyi gabaki ɗaya ya zamana ban taɓa haifan wani yaro mai suna Sadam ba, wannan itace hanya ɗaya da zaka gujewa rabuwa da ita na har abada ko rabuwa da mahaifiyarka na har abada,
Duk wannan abunda yake faruwa a idon mahaifin Abida amma ko alamu baidashi na hana mummy abunda take aikatawa,
Sadam ya dubi mummy cikin tsantsar tashin hankali yaga babu alamun wasa a fuskarta,
cikin sarƙewar murya yace toh mummy kimin Alƙawarin idan na rubuta bazaki taɓa bari taga letter ɗinba ko tasan cewa na saketa ba hhat lokacin da zaki bank umarnin maida auren,
Jijjiga kai mummy tayi tace"you have my words,
_Cikin mutuwar jiki Sadam ya rubuta saki ɗaya ma Sawwama kamar haka, Ni Sadam na saki matata Sawwama saki ɗaya batareda ta aikatamin wani laifi ba sai dan bin umarnin da zai zame mana maslaha gabaki ɗaya_
Taɓe baki mummy tayi bata damuba idan yaga dama yarubuta cewa na saketa saboda mummy ta sakani,
Ƙarɓan takardar tayi tace tashi kaje karka sake nunamin furkarka hhat ranarda na nemeka da kaina nabaka umarnin dawo da ita, idan kuma ka dawo da ita bada izinina ba toh ban yafe maka ba,
Miƙewa yayi har wani dushi-dushi take kallo yafice yana fita Abida ta rumgume mummy tana faɗin mummy kin burgeni wallhy gara da kikayi masa haka,
Mummy tace "yarinyar nan ta tsayamun a wuya fiyeda yanda ta tsaya miki Abida duk tabi ta maida yaro shashasha,
Sanya hannu Abida tayi ta ɗauki letter tace ni zan ajiyeta mummy saboda kashe bakin yarinyar nan mumny tace nidama bbu amfanin da zatayi a wajena,
Sadam yana fita yayi kuka amota saida ya isheshi ya tada its yatafi yana zuwa yacewa Sawwama ta haɗa masa kaya zaiyi tafiya da mamaki tace Yaya Sadam tafiya haka kwatsam wani abunne yafaru?
Sadam cikin dauriya yace haka tafiyar tataso,
zan tafine kawai dan bbu yanda na iya, Sawwama taga yanayinsa wani iri amma duk yanda taso ta tambayeshi yaƙi faɗa mata,
Ta shirya masa kayan a jaka har mota ta rakashi, Sadam zaiyi tafiyane saboda bazai iya zama da Sawwama wane ɗaya ba cikin inuwar sure ba zai tafi yajira har lokacin da mummy zata umarceshi ya maida matarsa, yatafi yabar Sawwama akan kwana ɗaya kawao zaiyi amma yana fita bada daɗewa ba taga alert na 700k a account ɗinta, alokacin ta kirashi amma bai ɗaukaba jikinta gabaki ɗaya yayi mata wani iri sai takeji kamar akwai abunda yake faruwa,
Saida yakusan isa yanda zaije kafinnan ya kira wayar mahaifinsa take sanar dashi cewa mummy tasaka yasaki Sawwama,
Dady ya tambayeshi garinda zaije ya faɗa masa sannan yace masa yadawo zai samu mummynsu itama zaiyi mata hukuncin abunda ta aikata, yana gama faɗin haka yaji wayar ta yanke, yayita nema bai sameshi ba"
Itakuwa Abida aranar ta shirya takoma gidanta,
Har washe gari Sawwama nata kiran wayan Sadamma amma yaƙi shiga, haka dadyma,
Dady shiru yayiwa mummy kamar bai san abunda ta aikata ba ganin batada niyyar sanar dashi yasa ya kirata batareda jan dogon bayani ba yace taje gida duk ranarda sadam ya dawo da matarsa itama saita dawo,
Mummy ta ruɗe ta kiɗima haƙuri take bawa dady amma yace takira Sadam idan ya amsa ta sashi yadawo da matarsa sai itama tazauna basai tatafi ba idan kuma bai amsa ba tatafi sai yadawo,
Mummy takira wayar Sadam yafi sau 70 amma akashe tayi kuka harta gaji,
sun doshi shekara talatin da aurensu ko yaji bata taɓa yiba gashi yau an korata gida gabaki ɗaya,
Har dare bata sameshi ba dady yace mata karta bari dare yayi gara tatafi, tana kuka tana bashi haƙuri amma hka yaƙi saida tatafi."
Kwanan Sadam biyu da tafiya Sawwama tana cikin wani hali na rashin samunsa,
knocking akayi tatashi da sauri tayi bakin ƙofa dan azatonta Sadam ne, ganin Abida ya sanyata haɗe rai tace "mai kikazomin gida?."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial23 Chapters
Golem core
Alex's life changed when it ended. Hit by a car and reincarnated into the core of a golem and then discarded he finds himself in a new world he needs to find his place in and figure out what life as a golem means. Starting small maybe one day he will be great.
8 209 - In Serial6 Chapters
Princess Aria and the Gem of immortality
This is the story of Brynhilde Von Aria who lost her parents at an early age and has lived on her own for a very long time. she one day finds out there is gem of power that can help here so sets out to find. along the way finds friends to help her in her search. the tale of princess Aria starts here.
8 109 - In Serial61 Chapters
A Pirate's Life, The Virus, and A New World
Alexandria knew from her attendants how harsh 'outside' was and how no one but pirates survived the vast oceans. Still, she was tired of living cooped up and contained in the walled remnants of an old-world city, denied the chance to explore the new. Alexandria swore she would get out, one day, and do whatever she wanted. Regardless of what anyone said. Regardless of the virus that changed everything. The virus kills men. Genetically engineered babies are made from what remains. The virus gave Alexandria her own ability that no one could match. Of course Alexandria would need her own crew. She would find others like her—others that wanted explore the new world and were strong enough that they wouldn't end up walking the plank for it—however, three hundred years into the end of the old world, the new had already carved out settlements, people content to claim and conquer, and less inclined to explore. The virus, the settlements, their disputes: Nothing would stop Alexandria. [participant in the Royal Road Writathon challenge]
8 102 - In Serial99 Chapters
World of Six Civilizations
Is death a sad ending for one who is destined to lead a mediocre life? When our hero dies in an accident after a boring working day, he gets the chance to be reborn as a completely different person. He belongs to a race he had only read in fantasy stories before, and the mishaps do not stop there. Nafız, who has come to miss even the mediocre days in her previous life, attains the power she desires with the help of the webs woven by fate. Of course, great power meant a great price to pay, and this event that would upset all balances on the continent would change the lives of many. The story of Nafız, who passes like the wind over the World of Six Civilizations, begins.
8 212 - In Serial27 Chapters
The Fallen Council
Downside-up has been opened and the past has been wiped from people's memories. The Council has fallen and been replaced by The Admins' and The Watchers' own alliances. They hate each other and are the worst enemies. Two of The Council's members managed to escape and now they have to save their siblings from the void and safe their friends and enemies from the Watchers' evil leader. But they need allies that remember the time when The Council still existed. Are they going to make it or run out off time? Part 2 of 'The Endless War'°Doesn't include shipping! °I don't own the YouTuber's characters!°But I do own the oc's!°Includes violence and swearing!°The fanart is drawn by me!°I haven't posted this anywhere else than here! Please DO NOT repost this anywhere! #3 - Admin 24.1.2021Started: 6.1.2021Finished: 7.2.2021
8 124 - In Serial19 Chapters
Darlentina | Darna x Valentina
This story is inspired to the original Darna fiction this year 2022. Narda and Regina's chemistry is undeniable, so what if Darna and Valentina were lovers.In this lifetime a love between a Hero and a Villain will happen.This is Darna's untold story...
8 97

