《ƘADDARAR RAYUWA》K page 65
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 65
Dawa kake waya? ta jefo masa tambaya kai tsaye cikin gadara ko juyowa sadam baiyiba yabata amsa da fadin bana tunanin kina bukatar jin wannan amsar, a kufule tabi bayansa tana fadin da wannan mayyar kake waya koh? Bai kulataba yaci gaba da tafiya batareda tabar bin bayansa ba tace "Sadam dakai nake magana fa kana wucewa wannan rashin adalcine kana tare dani kana waya da ita acan gefe wai ance maka zuciyar kashi ne dani? Na tabbata da atare da ita kake bazaka taba yarda ka kirani ba,
Juyowa sadam yayi yace abida muryarki tana cikakin kunne idan kina magana dani ya kamata kina sassauta muryarki danni ba danki bane karki ga mummy tana yimin fada kema kice zakina min duk wani abunda ranki yakeso bazan lamunta ba ya karashe maganar hadeda furzarda huci da alamun ransa ya matukar baci, abida cikin fushi tace menee bazaka lamunta dinba?
Nice dai bazan lamunci rashin adalci ba, wannan wawiyar matar taka akanta kake yimin duk wannan abun, toh sai dai ka zaba koni ko ita,
Haka sadam yaji maganar kamar wacce take zolayarsa ya zaba ko ita ko Sawwama? wata yar dariya sadam yayi cikeda mamaki yace what?
Inzaba koke ko ita? Kinada hankali kuwa?
Itafa ni naganta nace ina sonta amma kefa?
Bance ina sonki ba dole aka sani na aureki dan babu yanda na iya, duk da hakan kina tunanin har matsayinki yakai ki hada kanki da ita? Wacecec ke tukunna ma?
Mtsww yaja tsaki Sadam baida zafin rai amma da gaske Abida takeso ta maidashi mai zafin rai,
juyawa Abida tayi tafice a dakin ya zauna a bakin gado hadeda wullar da wayarsa yaja wani huci hannuwansa buyu yasanya ya rufe fuskarsa, sam bayason raini baya lamuntar raini ko wajan kannensa, Abida tana kona masa rai idan tanayi masa abu cikeda gatsali itafa matarsa ce yakamata tasan irin kalaman da zata dinga fada masa, bai ankareba yaji sallamar mummy da sauri ya dago ya dubeta hijabi a jikinta har kasa ga dukkan alamu tafara bacci amma cikin darennan abida taje ta tasota da wani kallo tabishi kai cikeda ma'anoni da dama sannan tace "Sadam fito falo muyi magana dadynku yana kiranka, miqewa yayi cikeda takaici da baqin ciki yabi bayanta,
A falo ya samesu harda dady sanyeda jallabiya yayinda abida take zaune a daya kujerar dake gefen dady sai wani shesshekar munafurci takeyi,
Ya zauna akasa gefe kusada dady, dady ya dubeshi yace "Sadam me yafaru?" Matarka ta kawo kararka sadam cikin darennan? Koma me tamaka bazaka bari izuwa safiya ku fahimci juna ba? Iyyeh! Meye haka ne wai Sadam shin kai rashin zaman lafiyar dadi yake maka ne? Yakamta ka ringa adalci a tsakaninsu,
Idon sadam ya kada ya ciko da kwalla ya dago ya dubi mahaifinsa yace dady ka yarda da abunda tafad'a maka kenan? Shikenan tana zuwa ta fada saika zauna akai batareda ni an tambayeni ba?
Miqewa sadam yayi yace tunda ba antara mu aji abunda yafaru ta bakin kowa bane babu amfanin zamana anan,
Ganin yanda ran Sadam ya baci ya sanya dady yayi saurin kamo hannunsa yana fadin haba Sadam haba bawai ma goyi bayanta bane kawai ina maka fada ne, shiru sadam yayi baice komai ba ransa yana tafasa mummy tace toh kuma har me akayi na harzuqa haka? naga fada kawai ya maka sadam yace "dady ka sakeni natafi sam mummy bata ganin laifin yarinyar nan komai tayi dai m-dai ne a wajanta, dady yace " yi hakuri naji dawo ka zauna, dawowa sadam yayi ya zauna amma har lokacin ransa yana bace, "inajinka sadam yimin bayani dady yafadi cikin sigar lallashi,
Advertisement
Nisawa yayi kafin yace yau nadawo inaso naje naga matata da yarana tsawon lokaci bana tareda dasu amma haka aka hanani, yanzu meye laifi dannyi waya da ita? Tanada hakki akaina kuma inada damar yin waya da ita naji lafiyarta, dady menene aibu ayim hakan? An hanani ganinta wwayrma baza'a bani wannan damar ba?"
Bayan haka mafa agabanta nayi ba saboda gudun karta ga kaman nayi mata cin fuska yasa nafita wani waje daban, amma wannan yarinyar ta tsaya tana fadamin magana duk yanda taga dama, ni nake aurenta ko ita take aurena?
Wai tana cemin na zaba tsakaninta da sawwama dama ni nace ina sonta? Ko a zatonta auren hadi yafi na soyayya n,,,,,,,, saurin dakatar dashi dady yayi yace "ya'isa haka toh menene kuma na fadin wannan maganganun, kuka abida tasaka tana fadin "kaji koh? Kunji abunda yake fada ba,
Mummy aharzuqe tace "kai sadam menene hakan? Wannan ai wulakanci ne, yanzu wnacan kazar har takai ka wulakanta yar uwarka akanta? Anya kuwa Sadam anya lafiyarka kalau? Kana tunanin bazaji zafin abunda kayi ba shin ita ba mace bace da zakayi waya da wata gabanta,
Sadam yace ba gabanta nayi ba kuma bada budurwa nayi waya ba matata nakira,
Kirji mummy ta dafa tace eh lallai ba lafiya ba sadam mai biyayya amma yanzu muna magana kana maida mana har kana muna maka magana kana tashi zaka tashi zaka bar wajan,
Dady ya daga mata hannu dakata tukunna aiba yayi hakan da wani nufi bane karki juya lamarin, shieu mummy tayi dady yace" sadam waye ya hanaka zuwa ganin matarka? Sadam ya dago idons aya dubi mummy, mummy ya kawarda kansa gefe yace mummy ce tace nagaji basai najeba, da mamaki mummy ta dubeshi dan batayi tunanin zai ambaci sunanta aciki ba, dady yadubi mummy yace "wannan ba dalili bane da zaisa a hanashi zuwa ganin iyalinsa kekuma Abida bakida hujja da zakice bazai kira yaji lafiyar iyalansa ba, bbu wanu dalili da zaisa ki hanashi ganin iyalansa saboda son zuciyarku,
Yadubi mummy yace "bake kike auran masa mata ba kibarshi yayi ikonsa da iyawarsa akansu idan kikaga ya aikata ba dai-dai ba saiki kwabeshi, su dukansu matan yayanki ne, na sha fada miki ki dauke idanuwanki daga gidan yaronnan,
Kai kuma Sadam karka sake nuna wata tafi wata cikin matanka haka babu kyau, ke kuma kiyiwa mijinki biyayya ki dauke kanki daga mu'amalarsa da dayan matarsa tanada hakki akansa kamar yanda kikeda hakki akansa bazan lamunci daya ta cutarda daya a cikinku ba ni wajena bbu wacce tafi daya dukanku matan Sadam ne na daukeki kamar yanda na daukeshi, dady yayita musu fada dukansu babu wanda yabari sannan yadubesy yace "kuje ku kwanta karna sake jin waji abun yataso sannan gobe da sassafe kuwuce gidanki ku tafida masu aiki da hassana da hussaina su gyara muku,
Allah yamuki albarka ya qara muku zaman lafiya da hakuri da juna kutashi kuje, amin sadam ya amsa sannan ya miqe Abida ma ta miqe jiki a sanyaye tabi bayansa,
Suna wucewa yadubi mummy cikin jin haushinta yace "kingani kinga abunda kika jawowa kanki? Kinaso ki zubda kimarki ta uwa a wajan danda kima haifa na fada miki a kullum kifidfa idanuwanki daga raywuar m yarannan amma bakyaji, yanzu in banda abunki menene na hanashi zuwa ganin matarsa? Mummy wacce kr cike damm zuciyarta kamar ta fice ta fado dan bakin ciki ga sadam daya bata mata rai ga kuma dady sai sauke mata masifa yakeyi, afili tace "shin menene aibuna dan naso yarona ya huta naga sun dawo ga gajiya shiyasa na nemi ya huta, dady ya murmusa yace karki fiye son kanki dayawa kefa kinaso kiga danki kusada ke ya kwanta ya huta amma shi bakiso ya kalli jasa yayan da koda sau daya hai taba sanyasu a idanwansa ba, tashi muje mu kwanta dare ya tsalla amma itama yarinyar nan yakamata kija mata kunne ba komai ne ake kaiwa kara ba abubuwa dayawa ma'aurata sukanui a tsakaninsu su shanye batareda wani yaji kansu ba, idan tana irin haka zata fitar masa akai ne ba'aso mace tacika qorafi dayawa. Ita dai mummy batace komai ba tayi shiru kawai abubuwa dayawa take ayyanawa aranta wanda Allah kadai ya sansu."
Advertisement
Suna shiga ciki Sadam ya dubi abida yace "rashin kirkin ki har yakai kibi mahaifana ki tashesu cikin darenan koda yake ba rashin kirki bane rashin wayo ne dan a iya tsawon rayuwata banga mace maras wayonki ba, kuma anyi na farko anyi na karshe karki sake hadani da iyayen, narai-narai abida tayi tace kagani koh ina yanzu dady yayi mana fada shine bayan mun shigo zaka sake yabamun baqara magana,
Kwanciya sadam yayi bai ko sake kallonta ba."
Washe gari da safe baba bai fita kasuwa ba bayan sun gama karin kumallo sawama tafito ta samesu zaune kofar daki shida mama da sauran yan kananun yaran wanda ya kasance yau weekend basu kaiga zuwa makaranta ba,
Zaunawa can gefen baba tayi ta gaidasu cikin girmamawa, baba yace mamana jiya ummi ta sanarmin da dawowar mai gidanki tunda yadawo babu amfanin zaman sai kuma ayi maganar komawa ni ayanda naso ki koma dakinki yau toh mamanki tace abarki izuwa ranar litinin ko talata nace mata duk yanda kukayi Allah ya kaimu da yau dakuma litinin ko talata duk dayane a wajan Allah, idan da wasu abubuwan da kike bukata saiki sanar dani idanna shiga kasuwa saina taho miki dashi,
Allah yamiki abarka ko qara hakuri shi zaman aure dan hakuri ne ki zauna da kowa lafiya, kuma zuciya daya, sawwama kanta na kasa tace "in sha Allahu baba, da hantsi baba ya shirya ya tafi kasuwa yayinda mama tacewa sawwama ta shirya izuwa jimawa su tafi lallae washe gari idan Allah ya kaimu sai taje kitso ranar litinin kuma su halima suke su gyara mata gida zuwa talata sai ta koma."
Sawwama ta kira Sadam bugu biyu ya dauka da sallama ta amsa hadeda fadin "ina kwana yaya sadam? Lafiya qalau Sawwamaty kun tashi lafiya? Ya yarana? Lafiyarsu qalau ina ina lafiya tabashi amsa atakaice sannan ta daura da fad'in 'yaya Sadam inaso zanje lalle, lalle! Sadam ya maimaita Eh sawwama tace sannan ta daura da fadin naso alokacinda zaka dawo zanyi maka ado na lalle da kitso yanzu zan cika alqawarina dan nasan kitso da lalle suna daya daga cikin abunda kafiso. Murmushi sadam yayi sannan yace tabbas barinma idan ya kasance lallen a fatarkine kitson kuma a kanki suna matukar yimiki kyau, yar dariya tayi najin dadi sannan tace "aikuwa zanyi maka kwalliyar na lalle da kitso domin nishadantar dakai kuma duk wani abunda kakeso nima shi nakeso tayi maganar cikin sauti madaidaiciya, lallai Sadam dan gata ne wajan Sawwmarsa dariya tayi tace "dole sadam yazama dan gata a wajan sawwama kamar yanda itama sawwama tadawo take yar gata wajan yaya Sadam, dariyar jin dadi sadam yayi sannan yace toh shikenan jirani ganinan zuwa na kaiki, Sawwama tace "ina jiranka yaya Sadam sai kazo, sallama sukayi sannan ta shirya tana zaman jiransa,
Awah daya ya dauka kafin ya iso yakira wayarta ya sanarda ita yana qofar gida cikin kankanin lokaci suka gama shiryawa suka fito itada halima,
Jingine yake jikin motarsa ya harde hannuwansa da kafafunsa yana jiran idowarta yayinda yake sanye da light blue din shadda sai sheqi takeyi kansa sanye da hula sai bakin takalmi budadde daya kawata kafafunsa hannunsa daure da agogo na fata shina baki Sadam yayi matukar kyau sosai yayinda ya dauke hankalin Sawwama ta shagala da kallonsa shima kallon nata yakeyi har suka qaraso yanda yake sallama sukayi masa sannan suka sake gaisawa basu dauki lokaci ba suka wuce izuwa wajan lallen shago yakaisu dake da layi ya sanya yabasu kudin kawai yace idan sun gama ta kirashi ya juya."
Kai tsaye wajan najeeb ya nufa dake sunyi waya kafin ya fito ya sanar masa wajanda yake,
Najeeb yayi murna sosai ganin sadam, shima sadam haka ne anasa wajan, najeeb yadubi sadam yace "tunda yanzu kadawo zan bar komai a hannunka kaci gaba da shirye-shiryen biki, Sadam ya dan dara sannan yace "najeeb ango, najeeba ma dariyar yayi yace saura kiris ayi babu kai, haba-haba ai hakan bazai yiwuba dole nasan zan dawo kafin zuwa lokacin tayaya za'ayi bikinka bana nan Najeeb? Aiko da ace bangama abunda yakaini ba zan dawo ayi bikinka sai na koma,
Najeeb yace kai ina karka manta baka dawo saboda an haifa maka babys ba tayaya zaka dawo saboda aure na?
Sadam yace "wannan daban kowanne da muhallinsa kuma nafada maka cewa ni banma san anyi haihuwar ba sai daga baya dan qin fadamun sukayi daga mummy har Sawwama kuma dalilin dayasa basu fada ba kenan suna tunanin zan iya dawowa, nisawa Najeeb yayi yace "koni daka sanar dani nasha mamaki duk da tawata gabar basuda laifi konine idan naga zaka ajiye abu mai muhimmanci ka taho dan bikina toh bazan fada maka ba, cigabanka shine namu idan zakama wani abu nan gaba nima bansan me zan zama ba, ta dalilinka gashi yanzu na samu aiki mai kyau na gina gidana har ina shirin ajiye iyali Sadam kai aboki ne na kwarai ba Mummy da Sawwama ba kadai ko nine bazan fada maka abunda nasan zaisa kayi sakaci da cigabanka da ban gaba zai amfanemu gabaki daya ba,
Uhmm kawai Sadam yace ya canja wani zancen, lokaci-lokaci yake duban wayarsa ko sawwama zata kira amma shiru, lokaci ya duba kusan 3hours kenan yanzu da kaita wajan yaci ace sun gama, Najeeba daya fuskanci cewa hankalinsa yana wani waje daban ya taboshi juyawa gareshi Sadam yayi Najeeb ya yayi kasa waving hannu alamun yana tambayarsa mai yafaru, Dan siririn tsaki sadam yaja sannan yace "3hours fa kenan dana kai Sawwama wajan lalle amma har yanzu shiru, Najeeb yayi murmushi yace "Sadam na Sawwama idan aka zauna dakai kana iya kiran Sawwama sau ba adadi, wanda yake tare dakai har kosawa yakeyi da zancenta sannan ya daura da fadin "kwanatr da hankalinka har indai lalle ne irinna mata dana sani to tabbas yanzu basu saka shekarar gamawa ba sukan dauki wuni guda wajan lalle,
Nisawa sadam yace Najeeb mutum yana gajiya da fadin abunda yake sone? Ni inason Sawwama yanzu ankai matakin da banajin zan iya boye sonta gaban ko waye, yanzu bazaka fahimta ba amma kabari kayi auren tukunna na tabbata zaka fahimta, Najeeb ya murmusa yace nasan soyayya sadam tunda ina yinta amma abunda nakeso ka gane matanka biyu ne ba daya ba, ko sau daya kana zancen abida haka koda kwatankwacin yanda kake na sawwma idanba haka ba zataji babu dadi, harara sadam ya watsa masa yace "kasan soyayya? Aina kasan soyayayr? Malam dakata kana shirin saninta ta dai, soyayyar baki kadai ce maka akayi ta isa akirata soyayya? Kana nan wani katon tuzuru dakai ana magana kan soyayya kana saka baki A fusace Najeeb yace "kaga dakata malam dama kazo nanne dan ka gayamin magana?" Sadam ya miqe kafarsa a doguwar kujerar falon hadeda lumshe idonsa a fili a furta "kanka akeji, za'aji kanmu ma Najeeb yafadi'i a kufule."
Dake da layin amare a shagon ya sanya su sawwama basu sami lallen dawuri ba hakanma masu lallen ba sunada yawa, ganin bata lokacin da suke a zaune ya sanya kawai tashiga shahin da ake gyaran kai aka gyara mata kafin agama lallen yazo kanta ma halima aka fara yiwa sannan bayan an gama gyara mata kai itama akazo kanta, Sadam yakirata hakai sau uku duka tana ce masa basu gama ba, tun lokacin sai qunquni kawai yakeyi yana fadin wannan ko wani irin lalle ne haka? Shi yaranma yafiji akan manyan yasan dole zasu galabaita."
Lallen Sawwama yayi matukar kyau sosai kamar na amare haka mai lallen ta zauna da zane mata shi yanda kasan inji ne yayi, ita kanta sawwaman ganin lallen takeyi cikeda sha'awa, duk mutanen da suke wajan saita suka tofa albarkacin bakinsu gameda lallen Sawwama wata ciki har tana fadin itama irinsa za'ayi mata, abunda duka kasa gamewa shine Sawwama ita tayiwa lallen kyau ba shi ya mata kyau ba."
Sun gama ana daff da za'ayi magrib hakan yasa Sawwama tacewa halima su wuce kawai basai sun kirashi suna tafiya izuwa bakin titi sukaji halima na goye da hameeda yayinda ita Sawwama ta goyi Hamdan horn din mota akeyi a bayansu alamun anaso su tsaya, Sawwama ta juya a zatonta Sadam ne sai taga bashiba hadeda rai tayi ta juya taci gaba da tafiya adai dai lokacin mai adaidaita yazo wucewa suka tsara suka tafi, tana lurada wannan motar har lokacin bata bar binsu a baya ba da sauri suka sallami mai adaidaita suka shige gida."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial54 Chapters
Erden : Tale of a Land Forgotten
Magic, monsters, and mystery— Fate uses the unexpected meeting of two children to spark a wave of change upon the land. Comic Adaptation: https://tapas.io/episode/2299612 What to expect : 3rd Person, 800-1400 word chapters, Slow-burn A rewrite of Land of Erden. Weekly updates on Friday!The plot stays the same as the original work, with just a few tweaks. I've decided to write in a way to further display each character's individuality as well. (I hope it shows.) Feel free to point out mistakes, or roast me if things become a bit hard to read because of confusing prose.
8 167 - In Serial7 Chapters
Heartseed: The fanged huntress
A World Reborn: The fanged huntress (Bonus Story)Mature! Involves death and violence.Follow Asiu, a huntress of the land of Cles as she comes to terms with the loss of self and her partner. As she flees her homeland in search of a new home to raise her son. As she travels into a distant land and a previously unknown realm; motherhood.
8 160 - In Serial13 Chapters
Tyizor's Shorts (and Poems)
I like shorts! They're comfortable and easy to wear write! These are just a series of shorts that I've written at some point in time. They're just something to distract myself from the struggle of my main story (not posted on here yet). A few poems are mixed in as well. Note: Tags/Genres have been picked, but some stories may be tagged independantly if the content is on the more disturbing side. ^^ Short stories that will be related to my main story will be tagged [EOS] Short stories featuring some of my EOS characters in a story unrelated to the main one entirely will be tagged [eos] Hope you all enjoy :).
8 154 - In Serial28 Chapters
Beyond Midnight
"I've been taught that girls have no value, and he's the only one who assures me that I do." Soleil is a girl. A young woman. A female. She couldn't hate it more, because in her society that cursed gender makes her expendable.The war that was wrought on Earth years ago destroyed society, and men almost went extinct. Repopulation is the propriety, even if it means marrying a man with 8 other wives to become a baby making machine.When she meets an enormous alien man through a window, she slowly comes to realize that she is meant for more. She sneaks away every night after that to meet him, finding herself falling for all 7 feet of him.... even if she can't understand a thing that he says.Fray has come from Rytaria to collect human females, the salvation of his race. As soon as he meets his precious Soleil, he knows he has to have her. Little does she know that Fray will do whatever it takes to make her his mate, and he will worship the very ground she walks on.
8 151 - In Serial12 Chapters
Dungeon Sect
On hiatus. Just have too much that happen in succession to have regular updates. will keep writing just wont be posting chapters for a while Jade was once a human on earth, many eons ago. He died and went to a cultivation universe. Sadly he was never heaven's choosen with heaven breaking luck. He was average and bland. When his brother was shining light he was the stabling post supporting him. Many sought to take down the light, but knew they were nothing to light so they tried to take down the post. Jade died in the cultivation universe, not without learning more than most in their billion year life times. He was not a genius by any means he was just well learned. Now he is a dungeon, with mana instead of Qi. Still he can cultivate and learn again. Who will he teach and help become a shining light Warning I am not the best writer, and it will take awhile to build to more of an action adventure story with dungeon building as a side as the story will shift from Jade the dungeon to his choosen students I use Cultivating Dungeon, and The bound dungeon as systems to build off of, but the story is all mine
8 141 - In Serial34 Chapters
A Bromance to Remember
{Completed}This is a PLATONIC Dream Team story, so no ships here. Just some dudes hanging out and causing trouble.Keep in mind: this is a FICTIONAL story, meaning that the events that this story entails never actually occurred.If any of the people mentioned throughout the story express discomfort with this story or it's topics, I'll take it down.#6-wreck (7/16/2020)#19-dreamxgeorgenotfound (7/24/2020)#1-dreamnotfound (7/28/2020)#13-gream (7/28/2020)#7-dreamteam (7/28/2020)#2-sapitusnapitus (11/19/2020)
8 138

