《ƘADDARAR RAYUWA》K page 65
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 65
Dawa kake waya? ta jefo masa tambaya kai tsaye cikin gadara ko juyowa sadam baiyiba yabata amsa da fadin bana tunanin kina bukatar jin wannan amsar, a kufule tabi bayansa tana fadin da wannan mayyar kake waya koh? Bai kulataba yaci gaba da tafiya batareda tabar bin bayansa ba tace "Sadam dakai nake magana fa kana wucewa wannan rashin adalcine kana tare dani kana waya da ita acan gefe wai ance maka zuciyar kashi ne dani? Na tabbata da atare da ita kake bazaka taba yarda ka kirani ba,
Juyowa sadam yayi yace abida muryarki tana cikakin kunne idan kina magana dani ya kamata kina sassauta muryarki danni ba danki bane karki ga mummy tana yimin fada kema kice zakina min duk wani abunda ranki yakeso bazan lamunta ba ya karashe maganar hadeda furzarda huci da alamun ransa ya matukar baci, abida cikin fushi tace menee bazaka lamunta dinba?
Nice dai bazan lamunci rashin adalci ba, wannan wawiyar matar taka akanta kake yimin duk wannan abun, toh sai dai ka zaba koni ko ita,
Haka sadam yaji maganar kamar wacce take zolayarsa ya zaba ko ita ko Sawwama? wata yar dariya sadam yayi cikeda mamaki yace what?
Inzaba koke ko ita? Kinada hankali kuwa?
Itafa ni naganta nace ina sonta amma kefa?
Bance ina sonki ba dole aka sani na aureki dan babu yanda na iya, duk da hakan kina tunanin har matsayinki yakai ki hada kanki da ita? Wacecec ke tukunna ma?
Mtsww yaja tsaki Sadam baida zafin rai amma da gaske Abida takeso ta maidashi mai zafin rai,
juyawa Abida tayi tafice a dakin ya zauna a bakin gado hadeda wullar da wayarsa yaja wani huci hannuwansa buyu yasanya ya rufe fuskarsa, sam bayason raini baya lamuntar raini ko wajan kannensa, Abida tana kona masa rai idan tanayi masa abu cikeda gatsali itafa matarsa ce yakamata tasan irin kalaman da zata dinga fada masa, bai ankareba yaji sallamar mummy da sauri ya dago ya dubeta hijabi a jikinta har kasa ga dukkan alamu tafara bacci amma cikin darennan abida taje ta tasota da wani kallo tabishi kai cikeda ma'anoni da dama sannan tace "Sadam fito falo muyi magana dadynku yana kiranka, miqewa yayi cikeda takaici da baqin ciki yabi bayanta,
A falo ya samesu harda dady sanyeda jallabiya yayinda abida take zaune a daya kujerar dake gefen dady sai wani shesshekar munafurci takeyi,
Ya zauna akasa gefe kusada dady, dady ya dubeshi yace "Sadam me yafaru?" Matarka ta kawo kararka sadam cikin darennan? Koma me tamaka bazaka bari izuwa safiya ku fahimci juna ba? Iyyeh! Meye haka ne wai Sadam shin kai rashin zaman lafiyar dadi yake maka ne? Yakamta ka ringa adalci a tsakaninsu,
Idon sadam ya kada ya ciko da kwalla ya dago ya dubi mahaifinsa yace dady ka yarda da abunda tafad'a maka kenan? Shikenan tana zuwa ta fada saika zauna akai batareda ni an tambayeni ba?
Miqewa sadam yayi yace tunda ba antara mu aji abunda yafaru ta bakin kowa bane babu amfanin zamana anan,
Ganin yanda ran Sadam ya baci ya sanya dady yayi saurin kamo hannunsa yana fadin haba Sadam haba bawai ma goyi bayanta bane kawai ina maka fada ne, shiru sadam yayi baice komai ba ransa yana tafasa mummy tace toh kuma har me akayi na harzuqa haka? naga fada kawai ya maka sadam yace "dady ka sakeni natafi sam mummy bata ganin laifin yarinyar nan komai tayi dai m-dai ne a wajanta, dady yace " yi hakuri naji dawo ka zauna, dawowa sadam yayi ya zauna amma har lokacin ransa yana bace, "inajinka sadam yimin bayani dady yafadi cikin sigar lallashi,
Advertisement
Nisawa yayi kafin yace yau nadawo inaso naje naga matata da yarana tsawon lokaci bana tareda dasu amma haka aka hanani, yanzu meye laifi dannyi waya da ita? Tanada hakki akaina kuma inada damar yin waya da ita naji lafiyarta, dady menene aibu ayim hakan? An hanani ganinta wwayrma baza'a bani wannan damar ba?"
Bayan haka mafa agabanta nayi ba saboda gudun karta ga kaman nayi mata cin fuska yasa nafita wani waje daban, amma wannan yarinyar ta tsaya tana fadamin magana duk yanda taga dama, ni nake aurenta ko ita take aurena?
Wai tana cemin na zaba tsakaninta da sawwama dama ni nace ina sonta? Ko a zatonta auren hadi yafi na soyayya n,,,,,,,, saurin dakatar dashi dady yayi yace "ya'isa haka toh menene kuma na fadin wannan maganganun, kuka abida tasaka tana fadin "kaji koh? Kunji abunda yake fada ba,
Mummy aharzuqe tace "kai sadam menene hakan? Wannan ai wulakanci ne, yanzu wnacan kazar har takai ka wulakanta yar uwarka akanta? Anya kuwa Sadam anya lafiyarka kalau? Kana tunanin bazaji zafin abunda kayi ba shin ita ba mace bace da zakayi waya da wata gabanta,
Sadam yace ba gabanta nayi ba kuma bada budurwa nayi waya ba matata nakira,
Kirji mummy ta dafa tace eh lallai ba lafiya ba sadam mai biyayya amma yanzu muna magana kana maida mana har kana muna maka magana kana tashi zaka tashi zaka bar wajan,
Dady ya daga mata hannu dakata tukunna aiba yayi hakan da wani nufi bane karki juya lamarin, shieu mummy tayi dady yace" sadam waye ya hanaka zuwa ganin matarka? Sadam ya dago idons aya dubi mummy, mummy ya kawarda kansa gefe yace mummy ce tace nagaji basai najeba, da mamaki mummy ta dubeshi dan batayi tunanin zai ambaci sunanta aciki ba, dady yadubi mummy yace "wannan ba dalili bane da zaisa a hanashi zuwa ganin iyalinsa kekuma Abida bakida hujja da zakice bazai kira yaji lafiyar iyalansa ba, bbu wanu dalili da zaisa ki hanashi ganin iyalansa saboda son zuciyarku,
Yadubi mummy yace "bake kike auran masa mata ba kibarshi yayi ikonsa da iyawarsa akansu idan kikaga ya aikata ba dai-dai ba saiki kwabeshi, su dukansu matan yayanki ne, na sha fada miki ki dauke idanuwanki daga gidan yaronnan,
Kai kuma Sadam karka sake nuna wata tafi wata cikin matanka haka babu kyau, ke kuma kiyiwa mijinki biyayya ki dauke kanki daga mu'amalarsa da dayan matarsa tanada hakki akansa kamar yanda kikeda hakki akansa bazan lamunci daya ta cutarda daya a cikinku ba ni wajena bbu wacce tafi daya dukanku matan Sadam ne na daukeki kamar yanda na daukeshi, dady yayita musu fada dukansu babu wanda yabari sannan yadubesy yace "kuje ku kwanta karna sake jin waji abun yataso sannan gobe da sassafe kuwuce gidanki ku tafida masu aiki da hassana da hussaina su gyara muku,
Allah yamuki albarka ya qara muku zaman lafiya da hakuri da juna kutashi kuje, amin sadam ya amsa sannan ya miqe Abida ma ta miqe jiki a sanyaye tabi bayansa,
Suna wucewa yadubi mummy cikin jin haushinta yace "kingani kinga abunda kika jawowa kanki? Kinaso ki zubda kimarki ta uwa a wajan danda kima haifa na fada miki a kullum kifidfa idanuwanki daga raywuar m yarannan amma bakyaji, yanzu in banda abunki menene na hanashi zuwa ganin matarsa? Mummy wacce kr cike damm zuciyarta kamar ta fice ta fado dan bakin ciki ga sadam daya bata mata rai ga kuma dady sai sauke mata masifa yakeyi, afili tace "shin menene aibuna dan naso yarona ya huta naga sun dawo ga gajiya shiyasa na nemi ya huta, dady ya murmusa yace karki fiye son kanki dayawa kefa kinaso kiga danki kusada ke ya kwanta ya huta amma shi bakiso ya kalli jasa yayan da koda sau daya hai taba sanyasu a idanwansa ba, tashi muje mu kwanta dare ya tsalla amma itama yarinyar nan yakamata kija mata kunne ba komai ne ake kaiwa kara ba abubuwa dayawa ma'aurata sukanui a tsakaninsu su shanye batareda wani yaji kansu ba, idan tana irin haka zata fitar masa akai ne ba'aso mace tacika qorafi dayawa. Ita dai mummy batace komai ba tayi shiru kawai abubuwa dayawa take ayyanawa aranta wanda Allah kadai ya sansu."
Advertisement
Suna shiga ciki Sadam ya dubi abida yace "rashin kirkin ki har yakai kibi mahaifana ki tashesu cikin darenan koda yake ba rashin kirki bane rashin wayo ne dan a iya tsawon rayuwata banga mace maras wayonki ba, kuma anyi na farko anyi na karshe karki sake hadani da iyayen, narai-narai abida tayi tace kagani koh ina yanzu dady yayi mana fada shine bayan mun shigo zaka sake yabamun baqara magana,
Kwanciya sadam yayi bai ko sake kallonta ba."
Washe gari da safe baba bai fita kasuwa ba bayan sun gama karin kumallo sawama tafito ta samesu zaune kofar daki shida mama da sauran yan kananun yaran wanda ya kasance yau weekend basu kaiga zuwa makaranta ba,
Zaunawa can gefen baba tayi ta gaidasu cikin girmamawa, baba yace mamana jiya ummi ta sanarmin da dawowar mai gidanki tunda yadawo babu amfanin zaman sai kuma ayi maganar komawa ni ayanda naso ki koma dakinki yau toh mamanki tace abarki izuwa ranar litinin ko talata nace mata duk yanda kukayi Allah ya kaimu da yau dakuma litinin ko talata duk dayane a wajan Allah, idan da wasu abubuwan da kike bukata saiki sanar dani idanna shiga kasuwa saina taho miki dashi,
Allah yamiki abarka ko qara hakuri shi zaman aure dan hakuri ne ki zauna da kowa lafiya, kuma zuciya daya, sawwama kanta na kasa tace "in sha Allahu baba, da hantsi baba ya shirya ya tafi kasuwa yayinda mama tacewa sawwama ta shirya izuwa jimawa su tafi lallae washe gari idan Allah ya kaimu sai taje kitso ranar litinin kuma su halima suke su gyara mata gida zuwa talata sai ta koma."
Sawwama ta kira Sadam bugu biyu ya dauka da sallama ta amsa hadeda fadin "ina kwana yaya sadam? Lafiya qalau Sawwamaty kun tashi lafiya? Ya yarana? Lafiyarsu qalau ina ina lafiya tabashi amsa atakaice sannan ta daura da fad'in 'yaya Sadam inaso zanje lalle, lalle! Sadam ya maimaita Eh sawwama tace sannan ta daura da fadin naso alokacinda zaka dawo zanyi maka ado na lalle da kitso yanzu zan cika alqawarina dan nasan kitso da lalle suna daya daga cikin abunda kafiso. Murmushi sadam yayi sannan yace tabbas barinma idan ya kasance lallen a fatarkine kitson kuma a kanki suna matukar yimiki kyau, yar dariya tayi najin dadi sannan tace "aikuwa zanyi maka kwalliyar na lalle da kitso domin nishadantar dakai kuma duk wani abunda kakeso nima shi nakeso tayi maganar cikin sauti madaidaiciya, lallai Sadam dan gata ne wajan Sawwmarsa dariya tayi tace "dole sadam yazama dan gata a wajan sawwama kamar yanda itama sawwama tadawo take yar gata wajan yaya Sadam, dariyar jin dadi sadam yayi sannan yace toh shikenan jirani ganinan zuwa na kaiki, Sawwama tace "ina jiranka yaya Sadam sai kazo, sallama sukayi sannan ta shirya tana zaman jiransa,
Awah daya ya dauka kafin ya iso yakira wayarta ya sanarda ita yana qofar gida cikin kankanin lokaci suka gama shiryawa suka fito itada halima,
Jingine yake jikin motarsa ya harde hannuwansa da kafafunsa yana jiran idowarta yayinda yake sanye da light blue din shadda sai sheqi takeyi kansa sanye da hula sai bakin takalmi budadde daya kawata kafafunsa hannunsa daure da agogo na fata shina baki Sadam yayi matukar kyau sosai yayinda ya dauke hankalin Sawwama ta shagala da kallonsa shima kallon nata yakeyi har suka qaraso yanda yake sallama sukayi masa sannan suka sake gaisawa basu dauki lokaci ba suka wuce izuwa wajan lallen shago yakaisu dake da layi ya sanya yabasu kudin kawai yace idan sun gama ta kirashi ya juya."
Kai tsaye wajan najeeb ya nufa dake sunyi waya kafin ya fito ya sanar masa wajanda yake,
Najeeb yayi murna sosai ganin sadam, shima sadam haka ne anasa wajan, najeeb yadubi sadam yace "tunda yanzu kadawo zan bar komai a hannunka kaci gaba da shirye-shiryen biki, Sadam ya dan dara sannan yace "najeeb ango, najeeba ma dariyar yayi yace saura kiris ayi babu kai, haba-haba ai hakan bazai yiwuba dole nasan zan dawo kafin zuwa lokacin tayaya za'ayi bikinka bana nan Najeeb? Aiko da ace bangama abunda yakaini ba zan dawo ayi bikinka sai na koma,
Najeeb yace kai ina karka manta baka dawo saboda an haifa maka babys ba tayaya zaka dawo saboda aure na?
Sadam yace "wannan daban kowanne da muhallinsa kuma nafada maka cewa ni banma san anyi haihuwar ba sai daga baya dan qin fadamun sukayi daga mummy har Sawwama kuma dalilin dayasa basu fada ba kenan suna tunanin zan iya dawowa, nisawa Najeeb yayi yace "koni daka sanar dani nasha mamaki duk da tawata gabar basuda laifi konine idan naga zaka ajiye abu mai muhimmanci ka taho dan bikina toh bazan fada maka ba, cigabanka shine namu idan zakama wani abu nan gaba nima bansan me zan zama ba, ta dalilinka gashi yanzu na samu aiki mai kyau na gina gidana har ina shirin ajiye iyali Sadam kai aboki ne na kwarai ba Mummy da Sawwama ba kadai ko nine bazan fada maka abunda nasan zaisa kayi sakaci da cigabanka da ban gaba zai amfanemu gabaki daya ba,
Uhmm kawai Sadam yace ya canja wani zancen, lokaci-lokaci yake duban wayarsa ko sawwama zata kira amma shiru, lokaci ya duba kusan 3hours kenan yanzu da kaita wajan yaci ace sun gama, Najeeba daya fuskanci cewa hankalinsa yana wani waje daban ya taboshi juyawa gareshi Sadam yayi Najeeb ya yayi kasa waving hannu alamun yana tambayarsa mai yafaru, Dan siririn tsaki sadam yaja sannan yace "3hours fa kenan dana kai Sawwama wajan lalle amma har yanzu shiru, Najeeb yayi murmushi yace "Sadam na Sawwama idan aka zauna dakai kana iya kiran Sawwama sau ba adadi, wanda yake tare dakai har kosawa yakeyi da zancenta sannan ya daura da fadin "kwanatr da hankalinka har indai lalle ne irinna mata dana sani to tabbas yanzu basu saka shekarar gamawa ba sukan dauki wuni guda wajan lalle,
Nisawa sadam yace Najeeb mutum yana gajiya da fadin abunda yake sone? Ni inason Sawwama yanzu ankai matakin da banajin zan iya boye sonta gaban ko waye, yanzu bazaka fahimta ba amma kabari kayi auren tukunna na tabbata zaka fahimta, Najeeb ya murmusa yace nasan soyayya sadam tunda ina yinta amma abunda nakeso ka gane matanka biyu ne ba daya ba, ko sau daya kana zancen abida haka koda kwatankwacin yanda kake na sawwma idanba haka ba zataji babu dadi, harara sadam ya watsa masa yace "kasan soyayya? Aina kasan soyayayr? Malam dakata kana shirin saninta ta dai, soyayyar baki kadai ce maka akayi ta isa akirata soyayya? Kana nan wani katon tuzuru dakai ana magana kan soyayya kana saka baki A fusace Najeeb yace "kaga dakata malam dama kazo nanne dan ka gayamin magana?" Sadam ya miqe kafarsa a doguwar kujerar falon hadeda lumshe idonsa a fili a furta "kanka akeji, za'aji kanmu ma Najeeb yafadi'i a kufule."
Dake da layin amare a shagon ya sanya su sawwama basu sami lallen dawuri ba hakanma masu lallen ba sunada yawa, ganin bata lokacin da suke a zaune ya sanya kawai tashiga shahin da ake gyaran kai aka gyara mata kafin agama lallen yazo kanta ma halima aka fara yiwa sannan bayan an gama gyara mata kai itama akazo kanta, Sadam yakirata hakai sau uku duka tana ce masa basu gama ba, tun lokacin sai qunquni kawai yakeyi yana fadin wannan ko wani irin lalle ne haka? Shi yaranma yafiji akan manyan yasan dole zasu galabaita."
Lallen Sawwama yayi matukar kyau sosai kamar na amare haka mai lallen ta zauna da zane mata shi yanda kasan inji ne yayi, ita kanta sawwaman ganin lallen takeyi cikeda sha'awa, duk mutanen da suke wajan saita suka tofa albarkacin bakinsu gameda lallen Sawwama wata ciki har tana fadin itama irinsa za'ayi mata, abunda duka kasa gamewa shine Sawwama ita tayiwa lallen kyau ba shi ya mata kyau ba."
Sun gama ana daff da za'ayi magrib hakan yasa Sawwama tacewa halima su wuce kawai basai sun kirashi suna tafiya izuwa bakin titi sukaji halima na goye da hameeda yayinda ita Sawwama ta goyi Hamdan horn din mota akeyi a bayansu alamun anaso su tsaya, Sawwama ta juya a zatonta Sadam ne sai taga bashiba hadeda rai tayi ta juya taci gaba da tafiya adai dai lokacin mai adaidaita yazo wucewa suka tsara suka tafi, tana lurada wannan motar har lokacin bata bar binsu a baya ba da sauri suka sallami mai adaidaita suka shige gida."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial14 Chapters
Kill the Joker: Survival Game
Redemption is a fickle thing. Nine detectives and nine serial killers find themselves playing a dangerous survival game of deductions, pretending, and - murder. With your life and alias on the line, what would you give up for a shot at redemption? ... The main premise and kick of KtJ is that it is a guessing game of sorts. 18 high school students of various ages and backgrounds come together and are given aliases, such as "King", "Killer", or as the protagonist is aptly named - "Protagonist". They do not know each others' identities, and what's more - 9 of them are anonymous detectives, and 9 of them are serial killers. The cast is given a list of their names, and a list of the identities of the serial killers and detectives they are being held hostage with, and are forced to interact to guess the identities. The people who are able to connect all identities will get "a special advantage" in the killing game, but it isn't specified what. Alongside this, each cast member is given three secrets they are able to reveal at any point for an advantage in the killing game as well. However, one of these secrets is their name, and revealing that secret will result in a minor "punishment" as well. [COVER ART DONE BY RILIE @kisikils] [Illustrated]
8 185 - In Serial18 Chapters
The Fated Saviour
A young boy lived his life in boredom. Living alone in his home while his parents were out there in the vast world. He thought it would never change, but that was until he met something that would change his life forever. Another boy lived his life in the slums outside of the walls of a richer city. He thought he would continue living the same as always; always being at the mercy at those with power, but he too would soon discover a supernatural power.They were given a chance to change their situations, but this world is not as simple as that. One can not hope to achieve change without hardships and risks.
8 175 - In Serial39 Chapters
Tales of the Rebirth Apocalypse Emperor (BL)
Have you ever wondered how your life might have turned out differently had you made different choices or decisions along the way? Sometimes, life does give you a second chance. However, it is you who decide whether that second opportunity counts… This novel revolves around our main character, Chen Murong, who can accidentally go back in time even before the apocalypse period begins to change everything humankind has done. We will follow our MC and see how he and his family react to this second chance to ensure their family and the human race's survival. --------------------------------------------------------------------------------- Current release schedule: 1 Chapter/week on Saturday + extra if I have more time on the weekday If you like my writing, please consider tipping/supporting me on: PayPal: paypal.me/AmateurAuthorPen Patreon: patreon.com/singlehamster I plan to have advanced chapters on Patreon in the future for you to read as well. However, as of now, there is no early access chapter. It is only a tip jar at the moment. That being said, your generous support will help me a lot and will stabilize the flow of chapters coming. This is just the start of my journey, and I hope to progress more with your help. I am also in the process of setting up my discord. Feel free to hop over to chat with me. 😊 I will give any notice, poll, artwork about my novel there in the future too! Discord: https://discord.gg/eMaxDuHvRP That's all. I hope to see you guys there! --------------------------------------------------------------------------------- Full background: The story situates in a universe called Gondola, where countless races from numerous worlds and realities are poured in. Our MC's original world, Blue planet (similar to Earth), went through an apocalypse period for ten years and has been pulled through this universe by mysterious force as one of the human race worlds. Unfortunately, the human race is one of the weakest and most feeble races of all Gondola races. However, their sheer number and several allies have helped them escape extinction so far. Regrettably, even though there are many ants, given a sufficient amount of time, the elephant will eventually be able to destroy them all. After 50 years of pointless struggle, almost all of the last remaining humans have been hunted down by some of the strongest undead races of the Gondola, the Skeletons, the Vampires, the Werewolves, and the Demons. The few remaining humans have been found and eradicated. Our MC, Chen Murong, a member of the last humanity group, can escape the hunt from undead races for fifty years. He finally dies under the claw of Lucifer, one of the emperor-rank demons from the undead race. However, he activates one of his time magic spells with his most precious space gemstone at the moment of his last breath. Through the spell, he wakes up alive, back in his home world, and returns to the year before the apocalypse period began.
8 168 - In Serial20 Chapters
System Outcast
Ray just wanted his new job. He was bored of his old one but things never work out the way you want.When the world ends and Ray dies, he wakes up in a completely new one. It turns out the system wasn't ready for him to die yet, but why?
8 198 - In Serial20 Chapters
Sir Grace Wachinga, Order of the Hatchet
Grace Howard, a tough street girl in Virginia could become a knight -- if she survives her education. She learns to fight and be a refined lady. She finds good friends, vicious enemies, and finally love and family. The Knight Riding School produces young knights capable of protecting victims the FBI and other agencies cannot. Police policies do not bind them. Carrying swords, knives, and other medieval weapons, they wear bulletproof vests, and use their horses and wolves as fighting and survival partners. I post a chapter about every two weeks, not for the writing part but for editing but because the editing process is so demanding. I give great thanks to those who have helped me learn the art and craft of writing a story, so easily told but written in blood.
8 194 - In Serial10 Chapters
Affair With JXDN
1st #jxdnsmutt1st #jadenhosslerdirty1st #jadenhosslersmutt1st #secretaffair**ADULT THEMES**Working on his film and photography crew, meant slowly falling for a talented young man. no matter how much I tried i learnt I couldn't deny him.Leave me comments or votes if I should even continue this. I'm not getting many reads so some feedback would be appreciated. Thanks and much love.
8 345

