《ƘADDARAR RAYUWA》K page 63
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Page 63
Washe gari ma haka sawwama tatashi tun safe take aikin kiran wayar sadam amma yaqi shiga, gashi batada phone number na abida da tana dashi tabbas zata kira taji dalilin dayasa sadam ya kashe wayarsa, har indai taji ba wani abun bane yafaru toh hankalinta zai kwanta,
Sake-sake take tayi acikin ranta abubuwa kala-kala suke zuwar mata da wanda ya kamata da wanda bai kamata ba, sai takeji kamar taje gidan mummy ko zata samu lamarin sadam, amma sanin yanda suke da mummy ya sanya sam batason su hadu, aduk ranarda zata hadu da ita kokuma zasuje wajanta gabanta ya dinga faduwa kenan zuciyarta ta ringa dar-dar kenan, saurin kawarda tunanin zuwa gidan mummy tayi cikin ranta domin tasan koda taje bazata iya fadin dalilin zuwannata ba, idan harko ta iya fadi to sai tasha bakaken maganganu wajan mummy."
zaune suke dukansu cikin gida suna gyaran shinkafa da mama da halima sauran sun tafi makaranta halima kuma tagama makarantar dake tsakaninta da sawwama bbu wani nisa suna aiki suna taba tadi amma sam hankalin sawwama baya garesu kana ganinta zaka fahimci hakan domin kuwa hannunta na cikin shinkafar amma wasa kawai takeyi da ita, tunaninta yana wani waje can na daban, daya hannun kuma riqe yake da waya takasa koda saka ta caji sai faman kiran wayar sadam kawai takeyi dill-dill wayarta ta dauke alamun ba caji dan tun datsu take sanar da ita cajin ciki yazo karewa,
ajiyar zuciya ta sauke wanda yajawo hankalin mama gareta, kallonta mama yayi cikin kwana biyu duk ta canja da dan fadawa fuskarta tayi, hannu mama ta sanya ta dafa hannunta sawwama ta dago ta dubi mama,
Mama cikin kulawa tace lafiya dai hafsatu? Girgiza kai sawwama tayi tace ba komai mama kawai hankalina na wani wajanne,
Mama tana shirin magana bata kaiga furta komai ba suka jiwo karar zubewar abu hankalinsu suka maida wajan karar, hamdan ne ya juye garin tuwo a jikinsa gabaki daya yayi wani butu-butu kamar aljani, mama tace oh ni wannan yaro yanzu dan Allah kiduba yanda yayimin da gari! Toh ku dauke danku kona dakeshi, dasauri halima tatashi ta daukeshi mama tace wannan yaro idan yafara rarrafe ko tafiya kika kuskura kika bar wani abun amfani kusa tass zai baras miki dashi, rawar kaine dashi, ita dai yar uwarsa babu ruwanta shiru abunta amma shi kansa gilgilwa yakeyi, yana zaune yake jaaa yaje yayi ta'adi wannan yaro zaki shafa da ta'adinsa, sai dai Allah ya rufa asiri, mama taci gaba da fadin yayi kamar uwarsa amma bai dauki halinta ba uwarka sam batada kiriniya,
Halima ta turo baki tace mama toh duk me yakawo wannan maganar akan dan garin tuwon daya zubda, mama tace eh yoh kyace dan gari mana tunda ku y'ay'anku basa laifi,
tunda nawane kuwa ai yazama dole na tanka, murmushi kawai sawwama takeyi tana kallonsa,
Mama tacewa halima sai ki masa wanka kafin garin ya shige masa ido ya damemu da rikici, flask halima tadauko na ruwan zafi ta sirka ruwan ta wankeshi ta canja masa kaya suka dawo ta ajiye ta sanya hannu cikin gyaran shinkafar da sukeyi, mama tace kinga tashi ko gyaramin wajanda ya bata sannan ki dagamin shi anan karya sake wata barnar,
Advertisement
Mikewa halima tayi ta kwashe garinda ya zubda dake a sminti ne bbu kasa kuma ashare yake tass sake tankadewa kawai za'ayi sannan ta sanya tsintsiya ta share wajan, ta dauki zanin goyo ta saba hamdan a baya ta goyashi sannan ta nemi waje ta zauna sukaci gaba da aiki suna dan taba hira,
Yarone ya shigo da sallama mama ta amsa! Ya gaida su sannan yace wai sadam yana sallama a waje, mama tadubi sawwama tace kinji yaronnan kaman sadam yakira koh?
Sawwama tace eh nima haka naji mama tace toh dama yana hanya ne kokuwa? Sawwama tace mama bansaniba dan wayarsa bata shiga, mama tacewa yaron kace masa ana zuwa,
Mama tadubi halima tashi kije ki dubo ko shi dinne aiko da mamaki zuwa haka katsam dawowa daga wata kasa sai kace wanda yadawo daga anguwa, sawwama ita dai batace komai ba zuciyarta sai bugawa takeyi da sauri da sauri,
Halima ta dawo tace aiko mama shi dinne wallhy mama tace ikon Allah je maza ki shigo dashi, sawwama kasa motsawa daga wajanda take tayi, jin abun takeyi kamar wani almara,
Sallamar sadam ne ta daki dodon kunnuwan sawwama da sauri ta dago kanta yayinda idanuwanta sukayi arba da fuskar da da dade tana muradin gani batasan lokacin da wani murmushi mai sauti ya subuce akan labbanta ba,
Mama ce dake fitowa a dakinta ta sanyo hijabi amsa sallamarsa da fadin wa'alaikassalam , a dan nesa dasu ya durkusa har kasa ya gaida mama ta amsa da fara'a tanai masa sannu da hanya, sannan tadubi halima tace ki kaishi dakin hafsatu saikizo, mama tana shiga daki ya kai kallonsa izuwa sawwama wacce itama shi din take kallon takasa dauke idanuwanta fuskarta yalwace da annuri, fara'arta takasa boyuwa,
Murmushi ya sakar mata fuskarsa dauke da tsantsan soyayyarta,
halima ce ta ce yaya sadam muje ciki mikewa yayi fuskarsa nakan sawwama yabi halima suka shige ciki,
Sawwama takasa motsawa daga yanda take saida mama tayi mata magana sannan ta miqe ta nufi dakin hannunta dauke da hameedah, itakuma halima tafito bayanta goye da hamdan tashiga dakin mama tabata kudi tace tasiyo lemo da ruwa,
Da sallama sawwama tashiga dakin ya amsa idanuwansa akan kofa, amsa sallamar yayi yana mai cikeda fara'a karasawa kusa dashi tayi kan sallayar itama ya zauna da muryarta mai sayin gaske tace ina wuni yaya sadam?
Lpy sawwamaty ya amsa da sauri, turo baki tayi sannan tayi narai-narai da idanuwanta tace yaya sadam meyasa zakamin haka? Kasan halinda nashiga kuwa?! Tayi magana hawaye ya qarasa gangarowa akan fuskarta cikin zazzakar muryarta mai sanyin gaske tace na kiraka na kira wayarka bata tafiya gashi kuma kai baka kirani ba bana kusa dakai bare nasan halinda kake ciki zuciyata tashiga damuwa,
Ido sadam ya zuba mata a hankali ya sanya hannuwansa ya matso da ita kusada shi ya kamo fuskarta ya sanya harshensa ya dauke hawayen dake kan fuskarta runtse idanuwa sawwama tayi yayinda takejin wani irin yanayi ajikinta saida yagama dauke hawayen fuskarta gabaki daya sannan ya sauko da labbensa izuwa lips nata cikin nutsuwa yafara kissing nata sun dade ahaka saida ya tabbatar zuciyarta tasamu nutsuwa sannan ya saketa a cikin kasalalliyar murya ya rada mata a kunne kiyi hakuri sawwmaty banyi hakan dan na saka zuciyarki cikin wani yananyi ba, naso nayi suprising dinki ban yi zaton abun zai dauki har 3days ba, amma ki yafeni bazan kara ba, ki cire zuciyarki cikin kunci sadam dinki yadawo gareki, hannu ta sanya a hankali ya tsagayeyi ta rungumeshi dakyau ta kwantar da kanta a kirjinsa tanajin bugawar zuciyarsa a hankali take saukar da numfashi, su biyun duka ya hada ya rungume harda hameeda wacce sai kallonsa takeyi a waya tasaba kallonsa yau sai gashi a fili, sallamar halima ce ta katse musu yanayin da suke ciki da sauri sawwama taraba jikinta da nasa taja gefe shikuma, halima tashigo ta ajiye masa lemon dake hannunta da ruwa da cups sanya hannu yayi ya dauki hameeda halima ta kunto hamdan tabashi suka qara gaisawa sannan tafice tabarsu, sawwama ta dauki cup ta bude lemo ta zuba ta miqa masa tace yaya sadam ga lemo, sadam daya zubawa yarnsa idanu yana kallonsu ya dago ya kalleta cikin yanayin zolaye yace nikam nasha lemon daya kamaceni yafadi yana lashe lips dinsa kawarda kai sawwama tayi dan tasan abunda yake nufi ta ajiye lemon gefe ta zuba masa idanu."
Advertisement
Ya maida kallonsa izuwa yaransa yana murmushi har farcen hannunsu da kafafunsu saida yabi ya dudduba, kamannin fuska ne kawai suka dauko na mahaifiyarsu amma dai-dai da gashin kansu irin nasa ne, suma yaran kamar wanda suka san mahaifinsu ne ya dawo bayan tsawon lokaci sai wasa suke ajikinsa suna dariya hameeda da bata cika hayaniya ba kawai ta zuba masa idanu iya kaci tadan kamo hancinsa can ta sake ta kamo gashinsa,
Bayan yagama kare musu kallo ya ajiyesu gefe yajawo sawwama jikinsa, lips dinsa yasake maida wa akan nata yacigaba da kissinga nata hededa wasu abubuwa masu wuyar fassaruwa sawwama bata iya hanashi abunda yake shirin yiba saboda itama tana cikin irin halin da yake ciki na kewarta itama hakan take ciki domin itma tayi kewarsa sosai,
Sanyin da sukajine ya dawo dasu daga duniyar da suka lula da sauri sawwama ta miqe tsaye domin ajike ta jita ga wani sanyi dayake ratsata kallonta takai ga hamdan ya tuntsirarda lemon da ta zubawa sadam, da sauri sadam ya dagashi domin ya bata jikansa shima narai-narainda fuska sawwama tayi kamar wacce zatayi kuka tace yanzu fa! Yanzu fa halima ta canja mai kayan nan ko minti talatin baiyiba amma harya sake batawa, murmushi sadam yayi yace yana taba gagara kenan sawwama tace ba dan kadan ba yanzu ya zubdawa mama gari kar kaso kaga yanda yayi butu-butu dariya sadam yayi yace to ai haka akeso yanzu da bayida walwala sai ace baida lafiya Toh Alhamdulillah gara yayi na wani lokacine, zaro ido sawwama tayi taje gara yayi?? Gara yayi fa kace yaya sadam! Jijjiga kai sadam yayi alamun tabbatar da kalamansa yace eh! Uhmm kawai sawwama tace ya miqa mata shi yace canja masa kaya kada sanyi ya ratsa shi, karbansa tayi ta nufi akwatin yaran ta bude tana fadin akan canja masa kaya sai 3 yayinda hameeda bata bata tun wanda aka saka musu da farko ba, sadam yace dama yaushe zaki hada kiriniyar mace dana miji??
Sawwama ta canja masa kayan sannan ta mikawa sadam ta gyra wajan daya bata ta fitada sallayar ta wanke dai-dai wajan ta shanya ta kawo wata ta shinfid'a sannan suka zauna, hira sosai sadam da sawwama sukeyi har aka kira sallar azahar sadam yafita yaje yayi sallah, yadawo anan ne yayi mata magana akan ta shirya su tafi, noqewa sawwama tayi tace yaya sadam ba yauba kabari muji mai su mama zasuce! Kaga daka sanar dani dawowarka tunda wurine da kafin ka isoma zan koma naje nayi maka shirin dawowa, hade fuska sadam yayi yace toh bagashi nadawo ba mai kuma za'a jira? Kawai nadauki matata mutafi, cikin kwantarda murya tace yaya sadam kayi hakuri ka iya hakurin shekara harda watanni ma bare dan wani kankanin lokaci da zamu kara yanzu? Nima nayi kewarka kuma yanzu banki nabika mutafi ba amma mubi komai a hankali, yanayin yanda take magana ya sanya sadam yayi dariya yace toh shikenan mujira muji abunda zasuce Allah yasa jiran namu bazaiyi yawa ba, sawwama tace in sha Allahu bazaiyiba dadina dakai yaya sadam sauqin kai, komai na rayuwa da sauqi kake daukarsa, murmushi sadam yayi yaja hancinta yace har indai mutum zai zaune da ke mai sanyin hali dole ya zamana mai saukin kai, baki furta kalamai kawai sai kin tantance su baki magana batareda ki aunata a ma'auniba kina da hangen nesa baki yanke hukubci dan son ranki toh mai zai hana bazan zama miki mai saukin kaiba? Nazama miki raqumi da akala ko jani duk yanda kikeso in sha Allahu zan biki, murmushi sawwama tayi ta sumbaci gefen kumatunsa tace inasonka yaya sadam! Girgiza kai sadam yayi yace nima ina sonki amma ni ba'anan nakeso ba, dariya sawwama tayi tace abunda kasamu ya isheka a ranar yau kabari sai kasamu na gobe, iska ba furzar yace shikenan da sannu zaki shigo hannuna,
Murmushi tayi gefen kumatunta ya lotsa tace hmm! Yace fadi abunda yake bakinki tace no babu komai, yace gara dai da kikayi shirun dan duk wani abunda zaki fada zan boyeshi a ma'auni har izuwa ranarda zakiyi bayani,
Kawarda zancen sawwama tayi tace yakamat ka huta yaya sadam saboda gajiya, jijjiga kai sadam yayi yace sauke gajiya aida sauran lokaci, shiru sawwana tayi kamar bataji abunda yace ba,
Sai yamma kafin sadam yabar gidan cikeda kewar matarsa ya yaransa, itama sawwama yabarta da kewarsa."
kai tsaye sadam gidan mummy ya nufa dan saukarsa ma can ya fara sauka ya huta yayita kiran wayar sawwama bai samu ba yafito ya taho wajan sawwama, yacewa mummy yanzu zai dawo, dawowar da ba'ayita ba kenan sai yanzu da yamma liqis."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial472 Chapters
The Last Embrace
In the 20th century…
8 871 - In Serial29 Chapters
Drinker of the Yew: A Necromancer's Tale
Updates Once a Week next update 10/5 Wracked with misfortune, a nameless village along the edge of the Gray Spine rejoiced at the arrival of a paladin. Those celebrations, though, turned to wary tension as the paladin brought an unknown into their midst - his wife Nayinis, who wears the markings of a necromancer. Who is this woman? Why has she come to their village? Nayinis divulges her shadowed past, for she needs the village's trust to defeat the powerful foe that she has been summoned by the divine to face. What to expect: This is a slow-paced, dark, epic-fantasy book written mostly in an archaic first-person style, remniscent of fariy-tale at times. I am expecting the final product to be close to 600-700 pages. The first few chapters introduce a somewhat-steep learning curve of names and mythology of the world that plateaus at aroud chapter 5. The Cover is by youthartwork on Fiverr
8 143 - In Serial12 Chapters
A-Zero
Prisoner 145 is a high-risk criminal kept at the world renowned prison complex Militant Base Prison Zexar aka MBPZ. Due to the numerous, horrendous crimes he had committed before arriving at the prison, it was assumed that Prisoner 145 would be sentenced to death. In the meantime, the King of Zeria, suddenly thought of an ingenious plan to expand Zerian territory without incurring the wrath of surrounding countries. This plan just happened to involve sending the most dangerous of criminals into the world. In a wicked twist of fate Prisoner 145 is released back into the world after ten years of solitary confinement as a part of this plan. How will he adapt to a world he has never seen? Who will still remember him? Does he even remember himself after all this time? I'm completely rewriting it. Cause I'm upping the quality. So uh, yeah. UPDATE: As suggested, old chapters (1-19) have been removed from RRL. If you feel like reading it, then visit my wordpress site: https://aspiringnewbie.wordpress.com/ For more information on this change go to my blog post: https://aspiringnewbie.wordpress.com/2016/03/19/welp-im-sorry-but-im-back/ Updates are super slow. Be Warned.
8 151 - In Serial50 Chapters
Reaper's Game
When Shin Kagerou beat the VR game """"Death Defiance Online"""" he did not expect to end up being the one """"Chosen"""" by the Reaper to be the player in a game between gods. And definitely did not expect to be forced to become a murderer.*Note: First FF and still new to the site, any advice, critique and help would be greatly appreciated.
8 161 - In Serial16 Chapters
Nightfall
Where they came from or what they even are is a complete mystery. What they want, however, isn't. There is only one thing that seems to keep them going: their endless hunger. Feeding is the only goal of these seemingly unstoppable nocturnal beasts. One of the few survivors, Markus, must journey across the United States in search of somewhere safe - to find others who are desperately trying to survive like him.
8 149 - In Serial62 Chapters
BadBoy Tutor
Samantha Walker is an 18 year old senior who plans to just spend the rest of her high school life hanging with her two best friends and staying single after being cheated on by her ex-boyfriend with the girl that she despises. When Sam is failing maths, she is forced to be tutored by the one and only Reece Parker.Reece is arrogant, cocky, annoying, a deliquient, but most of all the most attractive in school.Her and Reece already hate eachother but what happens when they are forced to spend time with each other and actually get to know each other. The two quickly become friends, and feelings may begin to develop.
8 149

