《ƘADDARAR RAYUWA》K page 62
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Mahaiafin nabeela ya isa izuwa ga fada bayan sun gama tattaunawa data tarasu mai martaba ya nemi ganinsa a killace,
Mahaifin Nabeelah yanata sake-sake cikin ransa ko meyasa mai martaba keson ganinsa? Ko zancen komawar nabeela zaiyi masa tunda izuwa yanzu ya tabbatarda labarin samun lafiyarta ya iso garesu, amma wannan karon zai roqi alfarma wajan mai martaba kan raba auren yarima da nabeelah kuma cikin ransa yanajin rashin dadin hakan domin shi kansa yasan mai martaba mutum ne, mutum ne gari wanda bbu wanda ba zaiso hada zuri'a dashiba bama ga mulki da Allah yabasu ba, A'a halayensa na gari da tausayin duk wani wanda yake kasansa, Gabaki daya zuri'arsu mai martaba sun kasance mutane nagari masu son takalawansu atarihin kasar kaff sarakunan da sukayi mulki sun kasance masu addini sanin yakamata Allah ya hore musu sani, masana ne na gaskiya gabaki daya illahirin zuri'arsu malamaine, Acikin gabaki daya kaff sarakunan anyi ittifakin bbu wanda yakai mai martaba sarki na yanzu sani da iya gudanar da mulkinsa ta farkin addini,
Cikin y'ay'ansa kaff mahaifin yarima shine yafi kowa wanda ake saka ran zai zama sarki mai adalci kamar mahaifinsa koma fiyeda shi, amma qaddara ta afka masa sai dai yabar baya! Yabar yarima haaliifaa wanda mai martaba ya dauki son duniya ya daura masa sai akaci sa'a yadauko hali irin na mahaifinsa da kakansa,
Yarima ya kasance mutum mai gwarjini fara'a da ilimi da sanin yakamata,
Bayan Abunda yafaru da mahaifinsa sai soyayyar mahaifinsa da mai martaba yake yi masa ya tattaro yadawo dashi akan yariima haliifaa."
Toh in banda lalura a gabaki daya duniya waye bazaizo hada zuri'a da mai martaba ba, waye bazaizo hada tsatso da dasu ba, zuri'a ce wacce ta shahara a gabaki daya duniya, shahara irinta ilimi na addini, mahaifin nabeela yana mai baqin ciki da takaicin wannan al'amari da yazo dashi zuciyarsa tayi nauyi, yanaji kamar bakinsa bazai iya furta neman rabuwa da wannan zuri'a da Allah yabasu daukaka ba, daukaka irin tasu bakowa ke samun irinta ba,
Zaiyi alfahari ace yau jikansa yafito daga wannan tsatso jikansa yazama wanda al'umna zasuyi alfahri dashi, ajiyan zuciya ya sauke yayinda zuciyarsa takeyi masa nauyi."
Gyaran murya mai martaba yayi ya dubi mahaifin nabeelah yace dafarko dai kasance amintacce mutum nagari mai sanin yakamata, a halinda yarima yake ciki ka dauko yarka mai cikeda nagarta da nutsuwa mai ilimi ka aura masa, sannan kuma ka sanyata tayi biyayya ga wannan aure, bazan taba mantawa da wannan halaccin naka gareni ba, kayimin alkahiri kuma shi alkahiri dan aikene in Allah yayarda alkahirinka gareni wata rana zai dawo gareka,
Mahaifiyar yariima ta sameni ta roqi wata alfarma gareni nazauna nayi tunani dakyau, nunfashi mai martaba yaja sannan ya gyara zamansa irinna manyan mutane yace nayi tunani akai sosai al'amarine mai wuyar fassaruwa al'alamarine mai nauyi a fatar baki yayinda zai iya sanyawa zuciya ta kasa samun nutsuwa zai shigarda ruhi damuwa da dimuwa amma duk wannan abune na wani dan lokaci saboda komai mai wucewa ne, shiru mai martaba yayi yayinda ya jefa zuciyar mahaifin nabeela cikin rudani domin yakasa gane yanda ya dosa, mai martaba yaja numfashi yace tasameni da zance akan araba auren yarima da nabeela koda na tambayeta dalili tacemin ita mahaifiya ce akwai lamarin da Uwa kawai zata iya fahimtarsa,
Advertisement
Tabbas zancenta hahkane Uwa itace takeda mahanga dayawa wacce take hango halinda yayanta zasu shiga, tayimin wannan magana ce a matsayinta na mahaifiyar nabeela ba yarima ba,
Na fahimceta kuma nace zan nemeka mu yanke shawara domin mai shawara tasa bata baci, kasa dakai mahaifin nabila yayi duk yaji babu dadi amma tabbas hakan shine abunda yakamata, domin wannan hali data shiga sun razana sosai idan har rabauwarsu shine silar samun lafiyarta, afili kuma yace Allah yasa hakan shine mafi alkahiri ina Adda'u Allah yabata miji nagari shikuma yarima Allah yabashi lafiya, mai martaba ya amsa da amin."
Anraba auren nabeela da yarima batareda son ran kowa ba sai dan babu yanda aka iya al'amarinne yayi wani iri."
Umma da ummi sukaje gidansu nabeelah bayan sun gaisa mahaifiyarta na zaune a gefe itama duk yanda taso raba auren bayan an raba saida taji babu dadi,
Kowannensu yayi shiru dakin yayi tsit yayinda nabeela idanuwanta suke zubda kwalla ganin umma yasake tada mata mikin son mijinta,
Ummi tayi gyaran murya tace toh Alhamdulillah mun gode Allah da kika samu lafiya nabeela muna fata nan gaba Allah ya bawa yarima shima lafiya mungode da halin girma da karramawa hadeda zama da kikayi damu tsakani da Allah hakika ke jarumace nabeela dole a jinjina miki Allah ya miki albarka,
Nabila kanta yana kasa bata iya amsawa ba mahaifiyarta ce ta amsa, dakin haka yaqara zama shiru sai can umma taja dogon numfashi tadubi nabeela tayi murmushi tace nabeela ke kin kasance y'a ce gareni ban daukeki wani abun kasada haka ba, kiyi hakuri na yanke shawara batareda neman izininki ba, mu masu laifi ne agareki dafarko munyi miki aure batareda son ranki ba sannan muka raba auren batareda izininki ba, amma dukda hakan kin kasance mai biyayya agaremu, ni uwace zan iya fahimtar irin halinda kike ciki zan iya jurar ganinki kina bautar aure amma bazan iya jurar ganinki kin cutu ba, bana fata nasake ganinki cikin irin wannan hali da kika kasance watannin baya zuciyata bazata iya daukaba, da wanne zanji? Da cwion da yarima yake ciki? Kokuma da ciwon ganin ki cikin wani yanayi?
Allah yagani banso rabuwa dakeba amma kuma yazama dole shiru umma tayi ta goge hawayenda yake qoqarin zuba mata tacigaba da fadin kiyita addu'a Allah yabawa yarima lafiya har indai da rabon zamanku agaba sai kiga anzauna idan kuma bbu Allah yabaki miji nagari,
Nisawa umma tayi tace bazan kasance mai son kaina ba nabeelah zanje zanci gabada kulada yarima har izuwa ranarda Allah zai bashi lafiyaa, dukansu wajan jikinsu yayi sanyi bakyajin komai sai shasshekan kukan nabeela da yake fitowa a hankali, ummi ne ta katse shirun da fadin ai ba'a rabuba in sha Allahu za'a cigaba da zumunci ai anyi zaman dadi zama akayi na amana nabeela yarinyar kirki ce kwarai da gaske Allah yayi miki zabin alkahiri cikin rayuwarki,
Jikin mahaifiyar nabila tabbas yayi sanyi da badan ace ciwo ba tabbas nabila tayi sa'ar dangi tashiga ahali wanda suka san me ake nufi da mutuntaka, tabbas sunason nafila so na hakika taga hakan cikin kwayar idanuwansu, tabbas taji babu dadi gameda maganganun da ta fadi a kwanakin baya domin kuwa sai yanzu tasan irin karamcin da suke dashi,
A yanda yarima yake tasan dubannin iyaye zasuso su bashi yayansu ya aura koda kuwa wani abun zai samesu, sanin yakamata irinna mahaifiyar yarima ya ratsa zuciyarta matuka,
Advertisement
Su umma sun dade agidan sannan suka tafi cikeda kewar juna,
Hajiya babba burinta yana kan cika yanzu hankalinta ya kwanta kasancewar tasan yanzu yarima shi kadai yake bbu wata wanda zata taimaka masa sai mahaifiyarsa wannan kuma huruminta daban, ciwon yarima nada wasu sharruda wanda zamansa da mace ya kasance hadarine a tattare dasu,
Hajiya babba tayi zurfin tunani sosai sannan ta sanya aka kira mata waziri, bayan waziri yagama kwasar gaisuwa hajiya babba ta dubeshi tace" Gameda wannan yaro haalifaa shin baka tunanin abarshi haka yafi? Batareda aure ba, sanin kanka ne munji kwakwa kafin musamu abubuwan da mukayi su kama jikinsa, yaran yanzu ba abun yarda bane garin neman gira karmu rasa idanuwa saboda yaran yanzu idanuwansu abude yake ba kowacce bace zata ganshi ta barshi haka nan kamar yanda wannan tayi dan nasha matukar mamaki da wannan yarinya (nabeela) ta kasance babu wayo? Yaran yanzu sunada son duniya ni ban yarda da kowa ba bayan mu kar garin neman duniyarsu su bata mana tamu duniyar kuma kasan abunda hakan zai iya janyowa, shin baza'abar haalifaa haka ba?
Waziri yace tabbas kince wani abun Ranki shi dade kina da zurfin tunani cikin kaskantar dakai dason samun wajan zama yace abunda kika hango mu bazamu iya hangoshi ba, kinyi gaskiya." Hajiya babba ta gyada kai tace Yawwa dama maganar kenan sai asan yanda za'ayi atoshe duk wata gaba da zaisa ayi zancen qara yimasa wani auren, waziri yace ki dauka tamkar angama hajiya."
Hajiya suwaiba itama tayi murna jin rabuwar nabeela da yarima da yawan mutane wanda dama suna da wata manufa cikin zuciyarsu sunyi murna yayinda wasu daga ciki suka tausayawa halinda yarima yake ciki, mutane kowa da abunda yake fadi wani suna kallon laifin nabeela da rashin hakuri na rabuwa da mijinta da tayi dan yanada lalura wasu kuma sunga kokarinta matuka dahar ta iya auren yariima kuma tazauna dashi ahaka mutane kenan, su mutane ahaka suke duk kaiwarki da kyautatawarki sai wasu sunga laifinki yayinda duk yanda kika kai da bakin hali wasu sai sun yabeki."
Wajan su umma rayuwa takoma irin ta baya domin andawo da yarima shashinta yabar sha shin mai martaba ita taci gaba da kula dashi ummi da ruma suna taimaka mata,
Jikin yarima wata aga canji wata rana kuma yayi tsanani umma ta tattara komai ta mikawa ubangiji da zubawa sarautarsa idanuwan, amma cikin zuciyarta bata cire ran cewa wata rana yarima zai samu lafiya ba, tanada yaqini akan hakan in sha Allahu."
Nabeela tashiga wani irin yanayi mai wuyar fasaltuwa hausawa sunce sabo turken wawa, nabeela ba wata shakuwa sukayi da yarima ba ba magana suka taba musaya tsakaninsu ba, bakuma kulawa da soyayya ta samu daga gareshi ba hasalima shi da zamanta da rashinsa duk bai saniba amma ta tsinci kanta cikin kewarsa, kullum cikin tunani wani lokacin har takan koka, ganin hakan yasa mahaifinta ya dagata daga garin gabaki ko zata samu ta manta dashi, tadawo da rayuwarta kamar ta kowa."
______________________________
Wajansu sawwama kuwa hamdan da hameeda sai girma sukeyi sun kara wayo sosai sunyi bul-bul abunsu gwanin sha'awa akai-akai dady yake musu aike sammam yana sanya mummy taje dubasu koda ranta bayaso tana zuwa tunda dai tasan koda taqi sawwama bazataqi jinin sadam ba, harda madara sawwama take hadawa yarn domin suna samun karancin nono, mahaifinsu kuwa koda yaushe da zarar yasamu hutu to yana kan wayarsa video call yana kallon matarsa da yaransa a kullum ji yakeyi kamar yayi tsuntsu ya taho ya qosa yaga yaransa yana matukar kewar matarsa, duk da kasancewa anan wajan itama abida tana bashi kulawar daya dace da taimakon mummy da take koya mata abubuwa kala-kala wanda zatayi danta kula dashi kafin su dawo ya kasance ta sace zuciyarsa, ita abida ji takeyi kamar su zauna acan domin zamansu haka su kadai yafi komai yimata dadi bataso sawwama ta qara shigowa rayuwarsu, tafiso tayi nesa dasu dan yanzu tana samun kulawar data dace wajan mijinta, tanada tabbacin idan sawwama tana nan bazata samu kwatankwacin wannan ba,
Abida ta matsawa mahaifinta akan ya sama musu aiki acan ita acan takeson ta zauna,
Ya shawarci mummy, mummy tayi murna sosai dan ita duk wani cigaba tanaso taga yasamu yayanta, kuma gara yatafi yayi nesa da sawwama ko hankalinta zai kwanta, batareda bata lokaci mahaifin abida yafara nema musu aiki acan."
Lokacin da aka deba na karatun su sadam har wuce kullum suna waya kuma bataji yana mata zancen dawowa ba, sawwama tayi kewar mijinta amma haka ta daure ta zubawa sarautar Allah idanuwa mahaifanta dake basusan dama aihini lokacin da aka deba na dawowar sadam ba yasa basu damu ba,
Har yaran sawwama suka fara zama sadam bai taba yimata maganar dawowa ba amma suna waya kuma bbu wani canji data gani agareshi, soyayyar dayake nuna mata bata raguba saima qaruwa da takeyi kullum,
Kwana daya harda wuni sawwama bata samu kira daga sadam ba kuma dama yawanci shi yake nemanta sau dayawa idan ta nemeshi ba samunsa takeba amma hakan cikin damuwa tayita nemansa wayar bata shiga, aranar har mama saida tagane sawwama na cikin damuwa amma tunda bata nemi tasani ba sai ta kyaleta itama bata nemi ta fada mata ba, saboda tasan da tanaso ta sani toh da ta sanar da ita,
Bata sani ba ko sun samu matsala da mijinta ne idan hakane kuma bata bukatar sani domin wani lokacin bai kyautuba a saka iyaye cikin yar qaramar matsalar gidan aure wanda kedashi kun isa ku magange kayanku, dan haka mama taja tayi taja shiru tana addu'a Allah yasa ba wani abun da zai cutar mata da ya bace, har izuwa magrib haka sawwama take sumu-sumu dama gata da sanyin rai sai abun ya hadu tadawo kamar wata marainiya, bayan an idda sallar magrib mama ta sameta a dakinta tazauna bakin gado tadauki hamdan tana fadin dan lukuti kenan wannan yaro yafi karfin goyonki hafsatu, murmushi sawwama tayi tace saina barmiki shi ai mama, itama mama murmushin tayi tace nagode kurike kayanku, a wajan mama ta zauna har bayan isha'i saida taga sawwama tasake kamar bbu wani abunda yake damunta kafin tatafi dakinta lokacin baba yadawo."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial1327 Chapters
Chrysalis
Anthony has been reborn! Placed into the remarkable game-like world of Pangera.However, something seems a little off. What's with these skills? Bite? Dig?Wait....I've been reborn as a WHAT?!Follow Anthony as he attempts to adjust to his new life, to survive and grow in his new Dungeon home! Join us on Discord! https://discord.gg/BFEfytf
8 2576 - In Serial6 Chapters
Vast Asleep
The story of Kingard the Binder in the aftermath of Broken This short story is the epilogue of Broken, the second book of the Chronicles of Mother's Gate series. It’s a great follow-up to the novel, a bonus story that adds extra layers but is set apart from the full-length narrative. Vast Asleep follows the story of Kingard, who finds himself caught in a world called Mother's realm, bathed in glowing light but strangely stuck in place. He encounters his greatson Varyan there, and learns that his experiences are likely dreams. As he grows more accustomed to the loving realm around him, Kingard remembers fear and trepidation about the face of the world, and he loses contact with his companion. This story answers the question, Is Kingard really dead? with a tentative no, and new mysteries brewing. It also raises the question, What's happening while he's awake? and includes an excerpt from the sister story Ride Awake, about Kingard's situation with the Colkh'rak. Praise for Tales of the Known World Bookends: Loved it. The difference between the two stories is great! The difference between the epilogue and prologue is astounding. So much light and love in the first story. You feel safe reading it. Healing. The second, so much darkness, pain and despair. The choice of vocabulary is awesome and makes an impact. And this set of short stories ties the two books together so well. -- Dana V. of Texas ★★★★★
8 167 - In Serial11 Chapters
Torn Asunder
Demons and devils are only myths... until they're not. An outcast detective, criticized for his crazy ideas, stumbles upon a case that could prove his wild theories true. Mysteries abound as a disturbed man struggles with his inner demons, wreaking havoc upon the physical world. Both hold pieces of an ancient puzzle that could plunge the world spiraling into chaos. Will their paths lead to salvation? Or will it tear the world asunder?
8 209 - In Serial33 Chapters
Multiple people, multiple ways
Sometimes things get harder, when people know their feelings TOO well. Which often results in (especially for teenagers) a very confusing time. If you pair that up with many many many personal crisis'... life becomes much harder than one might expect.~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~~WE ARE BACK TO BASICS! If someone knows me from a long time ago, they'll know I used to make ALL my covers via very bad editing because I didn't have anything better. Well, I have nothing better anymore, so, the cover is going to be that until I get it changed somehow. This'll be POLYAMORY. I will say it at the start, I absolutely hate, when things get stupidly complicated because people can't decide in fanfics, unless it's done well.Welcome to the adventure of me making a story absolutely nobody asked for.
8 70 - In Serial19 Chapters
The Beasts Under Your Bed
The Beasts From Beyond, an ever-present threat of elderich abominations appearing in the world through some unknown means, for unknown reasons. All that is known is that they will come, and they will kill. Living in fear of this, was not the way of the people of Alatara. To the North, they built mighty machines and bred mighty people. To the west, they developed an order of great warriors. To the east, they undertook surptitious and unseemly strides towards peace. To the South, flaming Demons and Devils crush the creatures that threaten them. And in the center, the largest mass of land and the largest concentration of both Beasts and man, they embraced unity. The Otherworld Defence Department oversaw all the needs of the different branches, the most famous of this being the Supernatural Incursion Response. A Mailed Fist, aimed at the creatures that would disturb the peace and threaten the people. Aided in this endevour, there were the Quasi-Humans. Beings of transformative properties, with powers and capabilities allowing them aid the Humans in pushing back the beasts. It is in this, that Kiko is born. Though nobody could foresee it, she will bring about the doom of the planet. The only question, is how?
8 102 - In Serial34 Chapters
Alpha Cravings
6000 years ago, the royal family of the werewolf race got wiped out by vampires, or did they? It is said they possessed great powers that have never been seen before not even witches have powers so great.Today there are no traces of vampires or royal members, or anyone that possesses great powers or is there?Meet Phoebe an ordinary girl that was born a white wolf with ordinary white wolf powers. She will be the next Beta for the Black Wolf Pack.Meet Damon he is the next Alpha for the Black Wolf Pack. After being gone for 4 years for Alpha Training he finally comes home with extra baggage in tow.What happens when these two find out they are mates? What will happen when everyone discovers one of them are more then just an ordinary werewolf?Contains mature content and violence.
8 248

