《ƘADDARAR RAYUWA》K page 62
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Marubuciyar
*BIBIYATA AKEYI*
* Y'AR FARI*
* YARIMA FAYAD* paid 200
Mahaiafin nabeela ya isa izuwa ga fada bayan sun gama tattaunawa data tarasu mai martaba ya nemi ganinsa a killace,
Mahaifin Nabeelah yanata sake-sake cikin ransa ko meyasa mai martaba keson ganinsa? Ko zancen komawar nabeela zaiyi masa tunda izuwa yanzu ya tabbatarda labarin samun lafiyarta ya iso garesu, amma wannan karon zai roqi alfarma wajan mai martaba kan raba auren yarima da nabeelah kuma cikin ransa yanajin rashin dadin hakan domin shi kansa yasan mai martaba mutum ne, mutum ne gari wanda bbu wanda ba zaiso hada zuri'a dashiba bama ga mulki da Allah yabasu ba, A'a halayensa na gari da tausayin duk wani wanda yake kasansa, Gabaki daya zuri'arsu mai martaba sun kasance mutane nagari masu son takalawansu atarihin kasar kaff sarakunan da sukayi mulki sun kasance masu addini sanin yakamata Allah ya hore musu sani, masana ne na gaskiya gabaki daya illahirin zuri'arsu malamaine, Acikin gabaki daya kaff sarakunan anyi ittifakin bbu wanda yakai mai martaba sarki na yanzu sani da iya gudanar da mulkinsa ta farkin addini,
Cikin y'ay'ansa kaff mahaifin yarima shine yafi kowa wanda ake saka ran zai zama sarki mai adalci kamar mahaifinsa koma fiyeda shi, amma qaddara ta afka masa sai dai yabar baya! Yabar yarima haaliifaa wanda mai martaba ya dauki son duniya ya daura masa sai akaci sa'a yadauko hali irin na mahaifinsa da kakansa,
Yarima ya kasance mutum mai gwarjini fara'a da ilimi da sanin yakamata,
Bayan Abunda yafaru da mahaifinsa sai soyayyar mahaifinsa da mai martaba yake yi masa ya tattaro yadawo dashi akan yariima haliifaa."
Toh in banda lalura a gabaki daya duniya waye bazaizo hada zuri'a da mai martaba ba, waye bazaizo hada tsatso da dasu ba, zuri'a ce wacce ta shahara a gabaki daya duniya, shahara irinta ilimi na addini, mahaifin nabeela yana mai baqin ciki da takaicin wannan al'amari da yazo dashi zuciyarsa tayi nauyi, yanaji kamar bakinsa bazai iya furta neman rabuwa da wannan zuri'a da Allah yabasu daukaka ba, daukaka irin tasu bakowa ke samun irinta ba,
Zaiyi alfahari ace yau jikansa yafito daga wannan tsatso jikansa yazama wanda al'umna zasuyi alfahri dashi, ajiyan zuciya ya sauke yayinda zuciyarsa takeyi masa nauyi."
Gyaran murya mai martaba yayi ya dubi mahaifin nabeelah yace dafarko dai kasance amintacce mutum nagari mai sanin yakamata, a halinda yarima yake ciki ka dauko yarka mai cikeda nagarta da nutsuwa mai ilimi ka aura masa, sannan kuma ka sanyata tayi biyayya ga wannan aure, bazan taba mantawa da wannan halaccin naka gareni ba, kayimin alkahiri kuma shi alkahiri dan aikene in Allah yayarda alkahirinka gareni wata rana zai dawo gareka,
Mahaifiyar yariima ta sameni ta roqi wata alfarma gareni nazauna nayi tunani dakyau, nunfashi mai martaba yaja sannan ya gyara zamansa irinna manyan mutane yace nayi tunani akai sosai al'amarine mai wuyar fassaruwa al'alamarine mai nauyi a fatar baki yayinda zai iya sanyawa zuciya ta kasa samun nutsuwa zai shigarda ruhi damuwa da dimuwa amma duk wannan abune na wani dan lokaci saboda komai mai wucewa ne, shiru mai martaba yayi yayinda ya jefa zuciyar mahaifin nabeela cikin rudani domin yakasa gane yanda ya dosa, mai martaba yaja numfashi yace tasameni da zance akan araba auren yarima da nabeela koda na tambayeta dalili tacemin ita mahaifiya ce akwai lamarin da Uwa kawai zata iya fahimtarsa,
Advertisement
Tabbas zancenta hahkane Uwa itace takeda mahanga dayawa wacce take hango halinda yayanta zasu shiga, tayimin wannan magana ce a matsayinta na mahaifiyar nabeela ba yarima ba,
Na fahimceta kuma nace zan nemeka mu yanke shawara domin mai shawara tasa bata baci, kasa dakai mahaifin nabila yayi duk yaji babu dadi amma tabbas hakan shine abunda yakamata, domin wannan hali data shiga sun razana sosai idan har rabauwarsu shine silar samun lafiyarta, afili kuma yace Allah yasa hakan shine mafi alkahiri ina Adda'u Allah yabata miji nagari shikuma yarima Allah yabashi lafiya, mai martaba ya amsa da amin."
Anraba auren nabeela da yarima batareda son ran kowa ba sai dan babu yanda aka iya al'amarinne yayi wani iri."
Umma da ummi sukaje gidansu nabeelah bayan sun gaisa mahaifiyarta na zaune a gefe itama duk yanda taso raba auren bayan an raba saida taji babu dadi,
Kowannensu yayi shiru dakin yayi tsit yayinda nabeela idanuwanta suke zubda kwalla ganin umma yasake tada mata mikin son mijinta,
Ummi tayi gyaran murya tace toh Alhamdulillah mun gode Allah da kika samu lafiya nabeela muna fata nan gaba Allah ya bawa yarima shima lafiya mungode da halin girma da karramawa hadeda zama da kikayi damu tsakani da Allah hakika ke jarumace nabeela dole a jinjina miki Allah ya miki albarka,
Nabila kanta yana kasa bata iya amsawa ba mahaifiyarta ce ta amsa, dakin haka yaqara zama shiru sai can umma taja dogon numfashi tadubi nabeela tayi murmushi tace nabeela ke kin kasance y'a ce gareni ban daukeki wani abun kasada haka ba, kiyi hakuri na yanke shawara batareda neman izininki ba, mu masu laifi ne agareki dafarko munyi miki aure batareda son ranki ba sannan muka raba auren batareda izininki ba, amma dukda hakan kin kasance mai biyayya agaremu, ni uwace zan iya fahimtar irin halinda kike ciki zan iya jurar ganinki kina bautar aure amma bazan iya jurar ganinki kin cutu ba, bana fata nasake ganinki cikin irin wannan hali da kika kasance watannin baya zuciyata bazata iya daukaba, da wanne zanji? Da cwion da yarima yake ciki? Kokuma da ciwon ganin ki cikin wani yanayi?
Allah yagani banso rabuwa dakeba amma kuma yazama dole shiru umma tayi ta goge hawayenda yake qoqarin zuba mata tacigaba da fadin kiyita addu'a Allah yabawa yarima lafiya har indai da rabon zamanku agaba sai kiga anzauna idan kuma bbu Allah yabaki miji nagari,
Nisawa umma tayi tace bazan kasance mai son kaina ba nabeelah zanje zanci gabada kulada yarima har izuwa ranarda Allah zai bashi lafiyaa, dukansu wajan jikinsu yayi sanyi bakyajin komai sai shasshekan kukan nabeela da yake fitowa a hankali, ummi ne ta katse shirun da fadin ai ba'a rabuba in sha Allahu za'a cigaba da zumunci ai anyi zaman dadi zama akayi na amana nabeela yarinyar kirki ce kwarai da gaske Allah yayi miki zabin alkahiri cikin rayuwarki,
Jikin mahaifiyar nabila tabbas yayi sanyi da badan ace ciwo ba tabbas nabila tayi sa'ar dangi tashiga ahali wanda suka san me ake nufi da mutuntaka, tabbas sunason nafila so na hakika taga hakan cikin kwayar idanuwansu, tabbas taji babu dadi gameda maganganun da ta fadi a kwanakin baya domin kuwa sai yanzu tasan irin karamcin da suke dashi,
A yanda yarima yake tasan dubannin iyaye zasuso su bashi yayansu ya aura koda kuwa wani abun zai samesu, sanin yakamata irinna mahaifiyar yarima ya ratsa zuciyarta matuka,
Advertisement
Su umma sun dade agidan sannan suka tafi cikeda kewar juna,
Hajiya babba burinta yana kan cika yanzu hankalinta ya kwanta kasancewar tasan yanzu yarima shi kadai yake bbu wata wanda zata taimaka masa sai mahaifiyarsa wannan kuma huruminta daban, ciwon yarima nada wasu sharruda wanda zamansa da mace ya kasance hadarine a tattare dasu,
Hajiya babba tayi zurfin tunani sosai sannan ta sanya aka kira mata waziri, bayan waziri yagama kwasar gaisuwa hajiya babba ta dubeshi tace" Gameda wannan yaro haalifaa shin baka tunanin abarshi haka yafi? Batareda aure ba, sanin kanka ne munji kwakwa kafin musamu abubuwan da mukayi su kama jikinsa, yaran yanzu ba abun yarda bane garin neman gira karmu rasa idanuwa saboda yaran yanzu idanuwansu abude yake ba kowacce bace zata ganshi ta barshi haka nan kamar yanda wannan tayi dan nasha matukar mamaki da wannan yarinya (nabeela) ta kasance babu wayo? Yaran yanzu sunada son duniya ni ban yarda da kowa ba bayan mu kar garin neman duniyarsu su bata mana tamu duniyar kuma kasan abunda hakan zai iya janyowa, shin baza'abar haalifaa haka ba?
Waziri yace tabbas kince wani abun Ranki shi dade kina da zurfin tunani cikin kaskantar dakai dason samun wajan zama yace abunda kika hango mu bazamu iya hangoshi ba, kinyi gaskiya." Hajiya babba ta gyada kai tace Yawwa dama maganar kenan sai asan yanda za'ayi atoshe duk wata gaba da zaisa ayi zancen qara yimasa wani auren, waziri yace ki dauka tamkar angama hajiya."
Hajiya suwaiba itama tayi murna jin rabuwar nabeela da yarima da yawan mutane wanda dama suna da wata manufa cikin zuciyarsu sunyi murna yayinda wasu daga ciki suka tausayawa halinda yarima yake ciki, mutane kowa da abunda yake fadi wani suna kallon laifin nabeela da rashin hakuri na rabuwa da mijinta da tayi dan yanada lalura wasu kuma sunga kokarinta matuka dahar ta iya auren yariima kuma tazauna dashi ahaka mutane kenan, su mutane ahaka suke duk kaiwarki da kyautatawarki sai wasu sunga laifinki yayinda duk yanda kika kai da bakin hali wasu sai sun yabeki."
Wajan su umma rayuwa takoma irin ta baya domin andawo da yarima shashinta yabar sha shin mai martaba ita taci gaba da kula dashi ummi da ruma suna taimaka mata,
Jikin yarima wata aga canji wata rana kuma yayi tsanani umma ta tattara komai ta mikawa ubangiji da zubawa sarautarsa idanuwan, amma cikin zuciyarta bata cire ran cewa wata rana yarima zai samu lafiya ba, tanada yaqini akan hakan in sha Allahu."
Nabeela tashiga wani irin yanayi mai wuyar fasaltuwa hausawa sunce sabo turken wawa, nabeela ba wata shakuwa sukayi da yarima ba ba magana suka taba musaya tsakaninsu ba, bakuma kulawa da soyayya ta samu daga gareshi ba hasalima shi da zamanta da rashinsa duk bai saniba amma ta tsinci kanta cikin kewarsa, kullum cikin tunani wani lokacin har takan koka, ganin hakan yasa mahaifinta ya dagata daga garin gabaki ko zata samu ta manta dashi, tadawo da rayuwarta kamar ta kowa."
______________________________
Wajansu sawwama kuwa hamdan da hameeda sai girma sukeyi sun kara wayo sosai sunyi bul-bul abunsu gwanin sha'awa akai-akai dady yake musu aike sammam yana sanya mummy taje dubasu koda ranta bayaso tana zuwa tunda dai tasan koda taqi sawwama bazataqi jinin sadam ba, harda madara sawwama take hadawa yarn domin suna samun karancin nono, mahaifinsu kuwa koda yaushe da zarar yasamu hutu to yana kan wayarsa video call yana kallon matarsa da yaransa a kullum ji yakeyi kamar yayi tsuntsu ya taho ya qosa yaga yaransa yana matukar kewar matarsa, duk da kasancewa anan wajan itama abida tana bashi kulawar daya dace da taimakon mummy da take koya mata abubuwa kala-kala wanda zatayi danta kula dashi kafin su dawo ya kasance ta sace zuciyarsa, ita abida ji takeyi kamar su zauna acan domin zamansu haka su kadai yafi komai yimata dadi bataso sawwama ta qara shigowa rayuwarsu, tafiso tayi nesa dasu dan yanzu tana samun kulawar data dace wajan mijinta, tanada tabbacin idan sawwama tana nan bazata samu kwatankwacin wannan ba,
Abida ta matsawa mahaifinta akan ya sama musu aiki acan ita acan takeson ta zauna,
Ya shawarci mummy, mummy tayi murna sosai dan ita duk wani cigaba tanaso taga yasamu yayanta, kuma gara yatafi yayi nesa da sawwama ko hankalinta zai kwanta, batareda bata lokaci mahaifin abida yafara nema musu aiki acan."
Lokacin da aka deba na karatun su sadam har wuce kullum suna waya kuma bataji yana mata zancen dawowa ba, sawwama tayi kewar mijinta amma haka ta daure ta zubawa sarautar Allah idanuwa mahaifanta dake basusan dama aihini lokacin da aka deba na dawowar sadam ba yasa basu damu ba,
Har yaran sawwama suka fara zama sadam bai taba yimata maganar dawowa ba amma suna waya kuma bbu wani canji data gani agareshi, soyayyar dayake nuna mata bata raguba saima qaruwa da takeyi kullum,
Kwana daya harda wuni sawwama bata samu kira daga sadam ba kuma dama yawanci shi yake nemanta sau dayawa idan ta nemeshi ba samunsa takeba amma hakan cikin damuwa tayita nemansa wayar bata shiga, aranar har mama saida tagane sawwama na cikin damuwa amma tunda bata nemi tasani ba sai ta kyaleta itama bata nemi ta fada mata ba, saboda tasan da tanaso ta sani toh da ta sanar da ita,
Bata sani ba ko sun samu matsala da mijinta ne idan hakane kuma bata bukatar sani domin wani lokacin bai kyautuba a saka iyaye cikin yar qaramar matsalar gidan aure wanda kedashi kun isa ku magange kayanku, dan haka mama taja tayi taja shiru tana addu'a Allah yasa ba wani abun da zai cutar mata da ya bace, har izuwa magrib haka sawwama take sumu-sumu dama gata da sanyin rai sai abun ya hadu tadawo kamar wata marainiya, bayan an idda sallar magrib mama ta sameta a dakinta tazauna bakin gado tadauki hamdan tana fadin dan lukuti kenan wannan yaro yafi karfin goyonki hafsatu, murmushi sawwama tayi tace saina barmiki shi ai mama, itama mama murmushin tayi tace nagode kurike kayanku, a wajan mama ta zauna har bayan isha'i saida taga sawwama tasake kamar bbu wani abunda yake damunta kafin tatafi dakinta lokacin baba yadawo."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial87 Chapters
The Scourged Earth
Derrick is no ones hero. He is barely dealing with his mundane life when all of humanity is forced to confront the extraordinary. Overnight, all across the world, mysterious machines appear. They offer people the chance to purchase almost anything they can think of. Weapons, medicine and even super human abilities are offered, seemingly for free. But following these machines, come the Scourges. The most dangerous creatures, diseases and machines that infest the universe. Ever growing and battling, these empires of horror and hunger will overhelm and devour the Earth and its inhabitants. Unless Derrick and humanity can stand against all the horrors that battle between the stars. +++++++++++++++++++++++++++++++++++++++++++++++++ My first Story, an attempt to turn the standard fantasy litrpg apocalypse into a Sci Fi. Trying for a slower build to power for the MC, so don't expect him to have cheat powers. I delight in helpful crticism so no holding back plz.
8 187 - In Serial38 Chapters
Black Titan
Renya, a veteran of the virtual reality game [Alt Online], is now being threatened by one of the largest Alliances in the game, the [Red Sun Alliance]. They have come to take his city; the city that he put blood, sweat, and tears into. He prepares for battle, summoning his forces, and as he and the [Red Sun Alliance] are about to begin their fight, an emergency maintenance occurs. Finding himself back inside the city, he quickly finds out that things have taken a twist. His city that was once filled with lifeless NPC's is now full of life, and has been brought to a new world. Watch Reyna as he tries to find his way in this new reality he has found himself in, and as he creates his own legend. Synopsis Credit to: Leafyeyes417
8 169 - In Serial13 Chapters
Kitsune in Rockford
Kit is an anomaly. The only male kitsune around. I mean sure there's beastkin with some fox traits around but nothing like him. How does having a power above your class affect your thinking? where do you go if you are the only one who thinks differently? (Some notes: will update irregularly, sugestions welcome, and I appologize now for deplorable grammar. ) Also I have the first two arcs planned in general, but sugestions welcome. (Please be civil about it though) Mature tag considering negative culture traits and ideas. No sex in this series. Light swearing. Violence. picture from: Kouan Kitsune by Claparo-Sans on deviantART
8 133 - In Serial6 Chapters
The Life of an Undercover Conqueror at Specialized High School
2093 ADEarth's natural resources have been depleted. We Humans could survive only just for a few years. We became desperate, we search and search for new resources for us to exploit, but we never found them. Until someone thought of something. "The society of the past even though they had different problems, they must have an answer to their conundrum. Perhaps we can use them too." We continue our research, nights and days have passed, however all of our research only lead to one thing and one thing only the Philosopher's Stone. It could generate energy without having to take any energy. Basically, it broke The Laws of Thermodynamic and Einstein's Law Conservation of Mass Energy, no, all the rule and law that we know of, doesn't apply to the Philosopher's Stone. But how? Where can we found this crimson colored gem? 2094 ADWe the researchers at the Genesis Lab finally found our answer. The Philosopher's Stone is not a Gem or any other precious mineral. It is an Organism, that can replicate itself perpetually. Our greedy minds have already started thinking of various thing especially about 'how can we abuse this poor thing' kind of thought. We can feed them to livestock. Additionally the excrement of those livestock can be used as a fertilizer. Voila! Infinite food and oxygen. But still, we don't know where to find this crimson colored life-form. Spring 2095 ADWE FINALLY DID IT!When we are deciphering some sort of ancient text related to the Mayans, we found out about where it was and how can we obtained it. The method that ancient people used seems to utilize human sacrifice as an offering to Gods. But hey, now we know that Gods exist, and more importantly Their whereabouts. If the ancient people used human sacrifice as the toll to open the portal. Then, we the modern people could simply use some sort of mini-sized black hole with specific coordinate to force this hidden life-form come to this world. Fundamentally, we just needed to mimic the portal that Gods himself open to answer their offering. Allright, let's do this. Summer 2095 ADEverything is progressing as we wanted.Every trivial thing on our side seems to be working in order.We can commence the operation 'Child's Play' early next year.-LB-
8 132 - In Serial26 Chapters
Gifted Eyes
Species War QuintetBook 4: Gifted Eyes In this world where 'Guilds' arise with tremendous magical powers and battle the demons from the defenseless humankind but later on, War broke out between two species. however, no one knew what will happen next. After 500 years the War suddenly stop and no one cannot answer it, therefore, they slowly forgotten and decide to live a peaceful life, but in the shadows, the 'phantoms' carried out the long- struggle blood battle between the 'war veterans' and the demons this war will be named as "Silence of War" no one will ever know this event. still, there is one man will change the whole world and turn the tides of war... John Kennedy was a prodigy and he has a natural talent but he witnessed the death of his family by "demons' when he was 10. he was picked by his one of his relatives in the age of 13, the relatives are fighting over the heritage for their own 'interests'. all of that a sudden 'unknown power' came into John's life and he never knew that the path will be a risky and dangerous one. no one knew that the boy will surely be predicted and see the possibility be in the future, on the other side, the mysterious power is still unknown. he swore to himself that he will avenge and bring Justice to his 'Adopted Family' as he walks right into the top. Follow John Kennedy as he embarks his adventurous on his long and dangerous journey along with his unparalleled-existence the unknown power the 'Gifted Eyes'.
8 184 - In Serial41 Chapters
darling - n.mikaelson
"Nothing is with me now but a sound, A heart's rhythm, a sense of stars"- W. H. Auden, ComplineIn which Charlotte Salvatore wakes after a 145 year slumber and is thrust into a supernatural world before she can cope with the modern one. (THE VAMPIRE DIARIES)(KLAUS X OC)#1 in vampires#1 in thevampirediaries #1 in Originals#1 in NiklausMikaelson#1 in Niklaus#1 in Klaus#1 in tvdfanfic#1 in hybrids#1 in tvd#22 in Mikaelson#69 in VampiresMay 28 2020 - Sept 25 2020 (edited Jan 2022)
8 212

