《ƘADDARAR RAYUWA》K Page 61
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa
#Follow me on
"
Page 61
Da sauri tafarka daga baccin datake ganin rana tafito ya sanyata sakin salati domin ko sallar asubahi batayi ba a gaggauce tashiga toilet tafito daure da alwala tagabatar sallah sannan ta kishingida a jikin sallayar domin wani baccine a idanuwanta bata samu bacci dawuriba ba jiya da daddare tazauna tanata tunani kamar yanda tasaba tana tunanin daya zame mata jiki yazama aikin yinta a kullum, bayan baccin ya dauketa kuma saita yi wani mafarki, mafarkine mai dadin gaske wanda bata taba koda kwatanta irinsaba hakan ya sanyata makara sallar asubahi,
bata dade da kishingida ba wani baccin yasake daukarta irin mafarkin datsu taci gaba dayi gata gakuma yarima cikin hankalinsa suna zaune suna hira cikeda nishadi afuskokin kowannensu,
Suna zaune a wani waje mai yalwar furanni hadeda bishiyoyi, kana ganinsu zaka hango tsantsar farin cikin dasuke ciki a cikin mafarkin take karasawa kusa dasu, tazo daff dasu cikeda murnar ganin kanta tareda yarima a wannan yanayin, farin cikin dayake fuskartace ya gushe, annashuwan fuskarta ta canja izuwa tashin hankali sakamakon ganin fuskarta tana canjawa wani kamanni hankalintane yatashi ayayinda ta ga gabaki daya kamanninta ya canja izuwa kamannnin wata yarinya wacce bata taba ganin fuskartaba shikuma yarima ko ajikinsa kamarma baisan da canjawar fuskarba saima wani farin ciki daya karu akan fuskarsa a firgice nabila tafarka daga baccin data keyi mafarkin datayi datsu ya sanyata farin ciki amma na yanzu yabata tsoro, me mafarkin datayi yake nufi kenan? Fuskarta ta canjawa zuwa wata fuskar? Wacece wannan wacce tagani amafarkinta?
Wannan sune tambayoyin da batada amsarsu batada kuma wanda zai amsa mata, jiki a mace tatashi tashiga tayi wanka tukunna ta shirya tafara yan gyare-gyare,
Saida nabila tagama duk wani abunda zatayi na gyaran gida izuwa breakfast sannan tanufi dakin yarima dan ganin yanda yakwana, murda hannun kofan tayi tashiga da sallama duk da tasan cewa bazai amsataba, akwance ta hangoshi a katafaren gadonsa har yanzu bacci yake bai farkaba da sauri ta karasa gaban gadon tadan rankwafo tataba fuskarsa jikinsa bbu zafi ajiyar zuciya tasauke sannan a hankali tafara taba kafarsa tana fadin yarima! Yarima! motsawa yayi a hankali sannan yabude idonsa ya zubesu akanta gabantane yayi mummunan fadi sakamkon yanayin data ganshi irin yanayine mai kamada wanda taganshi ranar, kallo ne yakeyi mata kamar wanda yakeson gano wani abun tattare da ita, cikin faduwar gaba nabila tajuya dasauri niyyarta takoma dakinta tadauki waya takira umma tazo taga yanayin da yake ciki,
Caraf taci ya cafko hannunta a tsorace tajuya ta dubeshi batayi auneba taji sautin muryarsa ta daki dodom kunnuwanta,
Am sorry!
shine abunda yake kokarin ambata, dukda abunda yake fadi bai fito radauba domin harshensa kamar a harde yake amma nabila ta fahimta abunda yake shirin fada, sandarewa nabila tayi a tsaye takasa aikata komai cikin tsoro sai tsaro idanuwanta take koda sau daya bata tabaji ya ambaci wata kalma ba sai yau,
Advertisement
Saurin saketa yayi ya rike kansa,
Atake kansa yafara jujjuya masa kamar wanda ake hajijiya dashi haka yaji kawai ya sake wani irin kara a tsorace nabila tafita bbu mayafi tashi sashin mai martaba bata sameshi anan ba a firgice tayi hanyar fita sukayi kicibus da umma, umma wacce ganin nabila ahaka ya sanya itama ta rikice ta rikota tana tambaya nabila mai yasamu haaliifan? A firgice tace umma yarima yayi magana yanzu kuma ihu yakeyi umma tayi saurin sakin abunda yake hannunta tayi cikin sashinsu da gudu a haka taje ta tarasda yarima rikeda kansa yanata kuwwa,
Karasawa tayi tasaka kuka ta rikeshi gam ajikinta sai kokarin kwacewa yakeyi nabilace tayi aika akaje aka gayawa mai martaba yana faada yataso yazo yasamu abunda yake faruwa, mai martaba bai dade yana masa addu'a ba abun ya lafa ba kamar daba da sai yakusan kwana akansa ana abu daya,
Bayan yasamu baccine nabila take basu labarin abunda yafaru umma tana kuka tana fadin in sha Allahu komai yakusan zuwa karshe yarima kakusa samun lpy,
Mai martaba yace lamarin kam akwai cigaba domin ko yanzu a kankanin lokaci komai ya lafa saba'anin abaya da ake kwana ana abu daya,
Zamuci gaba da addu'a in sha Allhu komai zaizo karshe da yardar ubangiji,
Ranar umma anan takwana wajan yarima, shikuwa yarima bacci yawuni yakwana yanayi danko farkawa baiyiba."
Wazirinr gaban hajiya babba a zaune ya gurfana kamar mai shirin yimata sujjada,
Kana ganin hajiya babba kasan a kufule take ranta yana bace sosai,
Hajiya tadubi waziri cikin takaicin dake cinta arai tace waziri kanason 6atamin aikina, kanason cusamun bakin ciki, yaushe har kayi saken da har akakai wannan matakin?
Ashe idan bana saka idanuwa akan lamuran nan shikenan zaku barsu su tabar bare?
Ashe ni ban kai ku tsayamin akan abuba kenna kuyimin abubuwanda suka kamata ba?
Jiya nayi kwanan bakin ciki!
Naji bakin ciki da sako ya isoni wai haalifa yafara magana! Saida ta jaa numfashi mai cikeda huci da zafi tace nadade arayuwata banji bakin irin najiya ba,
Inaso kayimin bayani yaya aka samu akasi haka tafaru?
Waziri yayi kasa da kansa yana fadin Allah ya hyci zuciyarki ranki shi dade Allah yaja zamaninki yaja kwananki da girman kujerraki, bbu ke bhu faduwa har abada, bbu ke bbu kara shiga bakin ciki irinna wanna karon har abada, hajiya tace ba wannan nakeson jiba yaya akayi haka tafaru?
Lokacin sabunta aiki yayi ka sabunta ko baka sabunta ba?
Waziri yafara kame-kame yana fadin ayimin afuwa ranki shi dade tabbas lokacin sabunta aiki yayi amma bansan mai ya sha'afar daniba,
Hajiya babba tace ka sha'afa?
Me hakan yake nufi kenan? Aikin da ake yinsa shekara da shekaru dimun da'iman shine yanzu ya sha'afar dakai?
Advertisement
Waziri ya kwantarda kansa yana fadin Allah yahuci zuciyarki Ayimin rai, hakan bazata sake faruwaba gobe-gobe zan sauka a wajan aikinann,
Hajiya cikin fushi tace yau basai gobeba idan aka sake samun matsala irin haka zanyi maka horonmak bala'in tsanani ,
Waziri yayi kasa dakai yace makamancin haka bazata sake faruwaba ranki shi dade,
Hajiya babba tace da dai yafi, kuma ka taimaki kanka,
Hajiya tace dalilin dayasa banaso na hada maka aiki biyu lokaci daya kenan saboda ka maida hankali akansa kada asamu matsala, daya aikin da mukayi magana dakai ranar asamu wanda zaija ragamarsa amma ba kaiba dan banason sake samu akasi duk karancin ko yaya yake banaso,
Waziri yace yanda kikace hakan za'ayi,
Ran hajiya babba yabaci sosai da sosai batayi zaton wannan sakacin daga wajan waziri ba saboda yafi kowa maida hankali akan aiki,
Waziri yatashi yatafi aranar yayi shirin barin kasar dan sabunta aiki."
Hajiya suwaiba itama anataa wajan hankalinta ba karamin rashi yayiba da labarinnan ya isota, aranar ta nemi yaya hadiza tace mata duk yanda za'ayi ayi kuma duk yanda zata fita tafita taje ta nemi musu wanda zai share musu hawayensu dan wancan yayi sake har yabar yarima yafara magana, aikuwa hakan akayi aranar yaya hadiza tayita yawon nema musu wajanda zasuje a aranar tasamu amma sai dai ba'a gari bane kuma wajan da nisa, tana fadawa hajiya suwaiba washe gari suka kama hanya."
Cikin kwanaki kadan jikin yarima yasake rikicewa jikinsa yayi tsanani dayafi na baya sosai,
Murnar su Umma takoma ciki yayinda labarin rikicewar jikinsa ta isa izuwa ga hajiya babba sai alokacin hankalinta ya kwanta,
Itama hajiya suwaiba anata wajan zatonta nata aikinne yaci har ya dawo da yarima haka,
Waziri ne gurfane gaban hajiya babba kamar wanda yake shirin yimata sujjada, cikin kaskantar da kai dakuma girmamawa yace Allah yaja zamaninki Ranki shi dade, hannu kawai hajiya ta dagawa waziri nufinta ba haka takeson jiba,
Waziri ya fahimci yanda hajiya babba ta dosa cikin son ya birgeta yafara fadin Hajiya anje an sabunta aiki wannan karon aikine akayishi na hakikanin gaske matsalar da muka samu wancan karon baza'a sake samun makamanciyar hakanba,
Hajiya babba ta gyada kai cikin gamsuwa da zancen waziri domin kuwa labari ya iso gareta irin yanda jikin yarima ya koma,
Waziri ne ya katse mata tunaninta da fadin wani hanzari ba gudu ba hajiya wannan yarinya matar sa izuwa yanzu yakamata ace mun san yanda mukayi da ita, tunda har tatafi tadawo hakan yana nufin itama zai iya samun wani taimakon daga gareta toh amma idan muka kawarda dagabaki daya daga gareshi, zamu samu daya daga cikin iyalanmu tashiga a matsayin mata gareshi aikinmu zaifi tafiya yanda mukeso komai zai tafi a yanayin tsaronmu zai kasance babu wata fargaba a tattare damu duk wani abunda muke bukata zamu sameshi cikin sauki, nunfashi hajiya babba taja sannan tace"
Nabar komai a hannunka duk wani abunda yakamata ayi toh ayishi, cikin girmamawa waziri yafice daga wajan hajiya babba."
Umma zaune bakin gadon da yarima haliifaa yake kwance idanuwanta cike da hawaye tana kallonsa cikin ranta sake-sake takeyi tunanin bbu irin wanda baizo cikin ranta ba,
Daga hannuwanta biyu tayi sama tace Allah Allah abunda ta iya fadi kennan kuka yayi kokarin kwace mata saurin toshe bakinta tayi da hannunta a hankali taci gabada rera kukanta gwanin tausayi wannan al'amari na yarima izuwa yanzu yaci ace idanda sabo ta saba toh amma ta yaya?
Ta yaya uwa zata saba da ganin d'anda ta haifa acikinta cikin wahala? Wannan abune wanda bazai taba yiwuwa ba koda idanuwanta sun saba da ganinsa cikin wannan halin zuciyarta bazata iya sabo da ganinsa ahaka ba,
Akoda yaushe idan ta kalli yarima haliifaa cikin wannan hali rayuwarsa ta baya ke sake fad'o mata yarima haliifaa ya kasance saurayi mai cikeda gwarjini , birgewa, shiga rai uwa uba addini da sanin ya kamata, iya kacin wadannan halayensa tayi sabo dasu amma ba wannan halin da take kallonsa aciki ba yanzu,
Jin motsinda tayi ya sanyata saurin hadiye kukanta ta sanya hannuwanta ta share hawayen dake kan fuskarta, da sallama nabila tashigo dakin, umma ta amsa sannan tasaki wani murmushi mai cikeda zallan damuwa, nabila ma ta maida mata murmushin da qaraso tace umma kije ki huta saina zauna a wajansa, rankwafar da kai umma tayi cikin sigar tausayi tace kayya nabila babu wani hutun da zan iya cikin wannan hali ke kije ki kwanta koda baki samu bacci ba kidan huta jiya haka muka kwana ido biyu cikinmu babu wanda ya runtsa,
Sunkuyarda kai nabila tayi kwallar tausayin kansu ya cika mata idanuwa, dukansu sun dawo abun tausayi itada umman da yariiman gabaki daya wani lokacin ma harda shi kanshi mai martaba gashi girma ya kamashi ga wannan al'amari mai tsoratarwa da rikitarwa dake faruwa da magajinsa hawayenda suka cika idanuwata suka sauko akan kumatunta, hawaye sun kuyarda kanta kasa tayi saboda bataso umma taga halinda take ciki amma saida umma ta fahimci yanayinda tashiga
A fili umma tace kiyi hakuri nabila kiyi hakuri bazan gaji da tausarki da baki hakuri ba, hakika wannan itace *
*
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial1492 Chapters
Dragon Prince Yuan
The heavens and earth are furnaces, every living things are charcoal, and the Yin and Yang are fuel. The battle for destiny, fate, and luck between the Serpent and Sacred Saint Dragon arises. When all is said and done, will the Serpent emerge victorious or will the Sacred Saint Dragon rise up above all sentient beings?
8 430 - In Serial22 Chapters
The Simulacrum of Dread
The entities known as the Beings of Old have long since staked claims to most of that gem-shaped manifold which is existence. Their alien, furtive, and impenetrably distant politicking has ebbed and flowed throughout past ages, beyond the awareness of most thinking creatures… and recently, it has begun to accelerate. For Sebastio Artaxerxes - and many civilians outside reality’s facets, especially in the transcendent city of Rhaagm - interest in such matters becomes far more pressing after a madman decides to claim a relic of one of the Olds. Sebastio’s demons tell him that fighting the man he once called friend will only end in tears. His soul tells him that tears are only shed by the living, and that the living at least may overcome regrets with time and effort.
8 137 - In Serial8 Chapters
Heavy Metal: A Cyberpunk Novelette
A soldier meets his favorite rockstar, partakes in mind uploading, and faces the reality of the war he's fighting. Ian finally has a night off, just in time to see his favorite band and the rockstar he worships. But then the doors are blown in, and a special ops team storms the place with guns blazing. When the smoke clears, his hero is dead. When the captain tells him to keep quiet, Ian can't help but talk to his hero one last time. What the rockstar says turns his reality upside down, that he might be the one inflicting terror on his people. Now Ian has to figure out what his captain is hiding, before he's forced to destroy the mind of his hero. If you love cyberpunk that makes you think, then you'll enjoy Ian's war within himself, and his plight against the military system pushing him to murder.
8 120 - In Serial39 Chapters
Epistula Amoris // SeokSoo
"Wag kang mag seselos ha? ikaw lang talaga pramis hihi muah" -Seokmin Lee, Writing for his future someone. [Love Letter series 1]
8 179 - In Serial23 Chapters
Zodiac Signs (Anime Version)
All in the title
8 155 - In Serial22 Chapters
Easy (Complete) | WinRina
This story is slightly (?) a next part of "It all started on Twitter". So Taeyeon and Jessica just had their first child who looks exactly just like them. The newborn parents are just doing so great taking care of their child.This is mainly WinRina so yeah. The generation moved on to the Next Generation.| Highest Rank |✨ 1. Taengsic✨ 2. Aetzy✨ 6. Taeyeon✨ 7. TaengSic✨ 7. Jiminjeong✨ 14. Snsd✨ 17. Girls Generation
8 94

