《ƘADDARAR RAYUWA》K Page 59
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
"
_Rayuwannan tadawo abun tsoro😢 Allah ya karemu da sharrin mutum da aljan, dole sai mun tashi mun riki addu'a hannu bibbiyu Allah yakawo mana dauki, Allah yashiga tsakanin nagari da mugu, ya Allah muna rokonka ka kare bayinka a duk yanda suke, addu'a tana da kyau sosai kuma makamice_ idan muka riqi addu'a sai Allah ya dubemu yajikanmu samnan kuma ya karemu."
*(Hasbiyallahu la'ilaha illah huwa alaihi tawakkaltu ahuwa rabbil arshir azim)* wannan addu'a tana da kyau yakamata mu riketa mu koyawa kannenmu da yayanmu, safe rana dare duka muringa Karantata kafa bakwai Allah ya karemu."
Page 59
Saida sawwama tayi 2weeks da haihuwa sannan akayi suna, lokacin jikinta ya dad'a warwarewa,
Idan ka ganta ma bazakace CS bane saboda
tana samun kulawa yanda yakamata daga wajan mahaifanta, duk wani abunda zasu bukata daga mai jegom har jariran dady ya tanadar musu dashi, suma mahaifanta suna iya nasu qoqarin dai-dai karfinsu dan ganin sun fidda diyar tasu,
Yara sunci sunan daddy da mummy wanda mummy ce ta bukaci hakan, kokadan ran mahaifan sawwama bai baci ba tunda dama sunsan sukeda iko da yara,
Kuma sunada ikon zabar musu sunanda yadace asaka musu, ko inkiyar da za'a ringa fadawa yaran ma mummy ce ta aiko da wadanda takeso hamdan da hameeda,
Duk wani iko da gadara da mummy ke nunawa babu wanda ya tanka mata mahaifan sawwama sun kauda kansu kawai dan zaman lpy, fun fiso ayi komai arabu lpy cikin mutumci da aminci,
Har akayi suna aka gama yan uwan sawwama ne da tsirarrun wasu daga cikin yan uwansa mummy bata yarda ta sanarwa yan uwa da abokan arziki da yawa ba sai iyakacin wanda tasan idan basu saniba za'a iya samun sabani, cewarta idan abida ta haihu zata sanar musu,
Sadam ma har lokacin bai saniba saboda bata fada masa ba bata kuma bada damar fada masa ba, dukda kullum sukayi waya da mummu yana tambayarta lpyrs sawwaman,
Yakan tambayane kawai amma yasan ba lallai idan tana zuwa dubasu ba, yadai lura kwana biyu akai-akai mummy ke kiransa awaya duk kuwa da yanda samunsa ke wahala,
Mummy koh tana kiransa ne tanaso taji ko sawwama ta bijirewa umarninta ta sanar masa daga nan sai tasan matakin da zata dauka akanta,
Halima da tasan wainar da ake toyawa cewa mummy ce tahana sawwama fadawa sadam zancen haihuwar ranta yabaci sosai, haushin sawwama ma taji na biyewa mummy datayi kuma tanaji kusan kullum sai sadam yakira waya sun gaisa ko wani lokacin yakan tambayi jikinnta dasauki kawai take amsa amsa,
Yakance har yanzu shiru? Kin wuce EDD dinki sawwama takance eh kawai saita canja zancen, dake bawani jimawa sukeyi suna hira ba wani lokacinma ita kece masa tanajin bacci,
Advertisement
Idan suka fara wayar halima ficewa takeyi daga dakin dan acewarta takaicine yake cikata bataga dalilin sawwama nabiye mummy a wannan shirmenba duk kuwa da tasan mummyn ba sonta takeyiba kuma bawai tayi hakanne da wani dalili ba sai dalilin kiyayyar da take mata,
Halima cikin jin haushin sanyin hali irinna sawwama da dubeta tace dan Allah yanzu haka zakuci gaba da zama?
Kinsan ranarda yagane cewa boye masa kikeyi zaku samu matsala?
Ina fata kinsan hakan?
Ita mahaifiyarsa ce tanada hanyoyi da zata kare kanta dayawa kuma dole yayi hakuri,
Sanyayyen murmushi sawwama tayi da muryarta mai sanyi tace in sha Allahu zai fahimta kuma
Mummy tayi hakanne dan kada yanar karatunsa dinsa yace zai dawo dan suna gabar fara exam na fahimceta,
Cikin takaici halima ta gyada kanta tace ya kamata daga nan bata sake cewa komai ba,
Dady zaune suke da mmmmy a daki phone dinsa tafara ruri yakai dubansa kan wayar no din sadam yagani, hannu yakai yadauka yana fadin kwana biyu munata dafka sabani a tsakani,
Amsawa yayi yakai wayar kunnensa hade dayin sallama sadam ya amsa hadeda gaisheda dady,
Dady ya amsa gaisuwa yana fadin kwana biyu munata sabani ko shekaran jiya daga kira muna meeting na fito kuma na nemeka ban sameka ba, kasan yanayin samun layinku nacan nada wahala ba kamar yanda ku kuke iya riskomu a saukake ba, shiyasa ma wani lokacin idan na tadda takira bana bi,
Dady yace ko shekaran jiyanma danayi trying akan sunan da kacewa mummynku asakawa yaranne sai naga rashin dacewar hakan amma tunda tace kai kayi insisting kuma nakiraka ban samuba ga lokaci yana kurewa shiyasa, amma alokacin dana sameka dako ni sai ahakura da sunana asaka na mahaifinta hakan shine adalci, tunda dai haihuwa kam in sha Allahu yanzu aka farata idan ba'a saka yanzu ba za'a saka wani lokacin,
Cikin rashin fahimtar zancen da dady yakeyi sadam yace dady yaro! Yaron waye kuma?
Dady yace ungo naka sadam yaronnaka kake tambaya wane yaro?
Mummy dake jiyosu a gefe saita fara share gumi ita batajin na sadam dadynsu batasan yanda zai dauki lamarinba, sake-sake tafarayi a cikin ranta na abunda zata fada masa kafin yagama wayar,
Muryar dady tajiyo yana fadin bani minute saika sake kira zamuyi magana da mummynka, gabantane yayi mugun fadi amma tadake,
Dady yajuya ya kalleta yace nasan baki bukatar karin bayani dan kinji me muka tattauna dashi, yakamata kiyimin karin bayani ina saurarenki? Menene dalilinki nayin haka?
Shiru mummy tayi dady yacigaba da fadin meyasa bakya kama girmanki? Kina shiga hakkin yarinyarnan dayawa, kina tunanin Allah bazai tambayeki bane akanta, kokuwa kawai danta auri danki saita zama abun musgunawa?
Mummy da wtaa idea da fado mata tayi wani narai-narai da fuska tace kayi hakuri da nasan abunnan zai bata maka rai har haka toh daban biyewa yarinyar nan ba,
Advertisement
Daddy yace wace yarinya? Mummy ta kara kasa da muryarta tace ita matar sadam din lokacin tana asibiti ita ta rokeni kan cewa bataso na fadawa sadam saboda yana gab da fara exam kuma ysha fada mata cewa tana haihuwa zai baro can kasar yadawo,
Toh nima dai da ban aminceba sai naduba naga zancenta yana kan manya yanzu idan yataho yabar karatunsa ai kaga ansamu matsala,
Daddy yace subhanallahi kaji wani rashin wayo shidin yana shirun jarabawar zai taho dan akansa aka fara haihuwa?
Mummy tace wai hakafa inji matarsa haka ya gaya mata, dady yace toh duk dai da hakan da kun fadamin ni kukayimin bayani nasan yanda zanyi dashi bai isa ya taho ba, kiran sadam ne yasake shigowa dan yamatsu dady yadaga yayi masa bayani, yace yo ai kaine ka sanya suka boye maka ai bazakce zakabar karatunka ka taho ba amma dukda hakanma naga rashin wayonsu da sun fadamin ni nasan yanda zanyi dakai,
Sadam shidai baice komai ba Allah-Allah yake suyi sallama da dady yakira sawwama,
Ransa yabaci kam da abunda sukayi masa amma kuma farin cikin dayake ciki dole ya take bacin ransa,
Mummy tacewa daddy idan kun gama banishi nan Zamuyi magana dady yace barshi yanzu yakira matarsa idan yaso idan sunyi waya saiya kiraki, mummy ta hade rai amma batace komai na dady yana nufin waya da matarsa yafi waya da ita muhimmanci kenan, miqewa tayi ta fita a dakin dan sam abunda dady yayi baiyi mata dadi ba,
Sau biyu sadam na kiran wayar sawwama ba'ayi picking ba sawwama kuwa lokacin tana wanka, yaran kuma suna wajan mama,
Ganin batayi picking ba ya sanya yakira mummy,
Mummy da shigarta daki taji wayarta tafara ruri, ganin sadam ya sanya ta saki murmushi saboda tasan wannan tsakanin lokacin bai isa ace har yayi waya da sawwama ba yazo kuma ya kirata,
Mummy tayi picking bayan sun gaisa sannan tace dama hakuri nakeso na baka, sadam yace hakuri kuma mummy? Mummy tace eh mana sadam matarka ta haihu amma munkasa fada maka, sadam yace bbu komai mummy yanzu gashi ai nasani,
Mummy tace toh ai babu dadi ne dan koni da farko data kawo shawarar banyi na'am da itaba amma data cemin zaka taso ka dawo to shine na amince kasanni sam banason wasa da karatu, bana daukan sakaci akan karatu,
Shiyasa kaga kwanakinnan na dage da kiranka wani lokacin haka naketa kira bai shiga ba amma dake abun yana raina inaso na fada maka shiyasa nake nacewa har saina sameka amma kuma saina kasa fadar,
Sadam yace mummy karki damu kanki bbu komai, mummy yaya abidar take?
Lpynya qlau tana dakinta sadam yabata amsa mummy tasake cewa kakira matar taka ne?
Kai tsaye sadam yace mata A'a,
Dadi taji a ranta, tace toh kakirata mana sadam; saida yadanyi jimm sannan ya amsa da toh atakaice dagajin yanda ya amsa maganar kasan ba har cikin ransa ba, ba karamin dady mummy tajiba dan tasan ko babu komai sai sun sami sabani tsakaninsa da sawwama,
Sallama yayi mata ya kashe,
Bayan sadam ya kashe ya ringa tunanin wani lokacine ya fadawa sawwama haka dahar zata sanarwa iyayensa tasan iyeynsa bbu abunda sukeso samada karatu kuma rashin maida hankali da zaiyi akan karatunsa zaisa su iya samun sabani, yadauka koda ya fada mata haka ita mai boye wane karta sanarwa mahaifansa dan kada suga kaman yana musu wasa da hankali kokuma ya fifitata akan muradinsu,
Tunane-tunane kawai sadam yakeyi bai sake daga waya yakira sawwama ba yana cikin tunanin abida wacce mummy tatura text akan taje wajan sadam ta dauke masa hankali ta shigo dakin, tayi nasarar dauke masa hankalin kuwa gabaki daya yanda bai sake bi takan wayarsa bama balle kiran sawwama,
Itako data dawo daga wanka batabi takan wayarta ba dan bakowa ke kiranta ba sai sadam shikuma bai saba kiranta a dai-dai wannan lokacin ba, yawanci lokaci daya tsayayye wanda yake kiranta,
Har dare bai kiraba bata dauki hakan a matsayin wani abunba ta kwanta tayi baccinta kawai,
Washe gari ma harta cire rai da kiransa sai kuma gashi yakira,
Murmushi sawwama tayi alokacinda taga sunan sadam daukan wyaar tayi a hannunta tayi picking ta kara a kunnenta da sanyayyar muryarta tace Amincin Allah ya tabbata agareka."
Kwanaki da yawa babu posting wasunku daga ciki sunsan cewa banda lpy yayinda wasunku basusan hakanba, amma duk da haka ina mai baku hakuri akan rashin samun update, Allah yakara mana lpy Amin."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial720 Chapters
Realm of Myths and Legends
Jin, a hardcore gamer who still lives with his mom at the age of 24. He could never hold down a steady job since graduating, his girlfriend since high school dumped him for his best friend and he’s constantly getting beat up by a group of local gang members. His dad left him and his mom when he became rich from the lottery and got a new family, one free of debt and burdens as he called it. His mom works 3 jobs to keep everything from falling apart, except for herself slowly. One day on his way home with the very first and new fully immersive VRMMORPG called Realm of Myths and Legends or RML for short, he died from a hit and run car accident. RML was advertised as the worlds first fully immersive VRMMORPG, allowing for players with skill sets in the real world, like sword training, martial arts, archery or reaction time, to benefit in the game itself! Though Jin died and at that moment a soul from another world crossed over into his body and inherited his memories. The man known as Izroth once hailed as the greatest cultivator in the seven realms, soul reincarnates into the modern world year 20xx in the body of Jin.
8 369 - In Serial12 Chapters
Ascension of Shura
When Lin Shen logged in to Asgurd for the first time he never thought his curse would awake as a skill. This is his journey to be the strongest.
8 322 - In Serial51 Chapters
The Coach's Daughter
In a town where the high school football team rules the school, Amelia is just another face in the crowd. Sure, her dad is the football coach but Amelia's idea of "Friday night lights" revolves around studying until lights are out. Trying to impress her father who only knows football and her mother's high expectations, Amelia puts her head down and tries her best to satisfy them. After accidentally ending up at a party one night (without her mother's permission of course), Amelia finds herself thrown into the world of the infuriatingly gorgeous yet arrogant Zack Darrington.Zack was never part of a crowd. He's king of the city: the best running back in the state- if not the entire country. Flirtatious, cocky, and a skilled player in all senses, Amelia is not the type of girl he typically surrounds himself with.Everyone knows Zack Darrington. No one knows Amelia Hayes. Football is his world while she wishes it wasn't a part of hers. At first glance, these two couldn't be more different but deep down, they may be more similar than they think.Highest Rankings:#1 in Fiction #10 in Teen Fiction#3 in Sports#10 in DramaBook 1 in THE COACH'S DAUGHTER trilogyCan be read as a standaloneBook 2 OUT NOW
8 88 - In Serial18 Chapters
I am Stellar
A future where entertainment is mainstream. Thousands and millions of virtual planet hub are chained together, forming a net — forming what's known as the Quantum Network. Every second, millions of traffic happen within the Global Hub, the forefront front of the Quantum Network, while serving as the entertainment source for the public. Hao Xu, a periodic user of the Global Hub, found himself cast away into the far-reaching corner of the web — or so he believe. Is it truly the truth? Or is it simply his Psychotic mind at work, as he found himself awake, greeted with a white-ring of light. ———— I'm posting this draft here as of now — work in progress. Noticeable changes will appear daily. Status Update: Hiatus
8 153 - In Serial11 Chapters
New chance
A bleach rosario crossover staring the 4 espada ulquiorra as he is given a second chance at life to find his heart. this fiction is starting back up dont mind the hiatus tag
8 179 - In Serial14 Chapters
Roommates
Y/n is the daughter of Tony Stark. You all live together at Avengers Tower. But when all of them have an important mission to go on, you have to go and live with the schools nerd, Peter Parker. Unbeknown to y/n, Peter is Spider-Man.
8 90

