《ƘADDARAR RAYUWA》K page 53
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
"
Muna saida kaya, material, laces, atampha, shadda, takalma kayan kitchen da sauransu akan farashi mai sauki siya daya ko sari,
Alarabee's hair cream is available pcs, cotton, half cotton, yana gyara gashi, cire dandruff, hana karyewar gashi, yana softening gashi, yana saka bakin gashi yana saka cika da tswon gashi🥰 masu bukatar kaya ko hair cream ku tuntubu wannan lambar 08161146563
Page 53
Sadam baije kiran dady ba sai da ya tabbatar ya zauna yagama tsara abunda zai fada idan yaje can, har rubutawa yayi a paper yanata mai-maitawa kamar karatu🤔 yanda idan yaje bazai manta koda kalma daya ba,
Saida ya tabbatar ya shirya kalamanda hankalinsu dady da mummy zai dauka sannna ya nufi gida,
Wata irin nutsuwa sadam ya tattaro yashiga gidansu da ita wacce kana ganinsa kaga salihin bawa,
Yasamu mummy tacika tayi fam kadan yarage ta fashe sai huci take jiransa kawai takeyi ga abida kusada ita tayi wani luff kamar mras lafiya,
A nutse sadam yashiga har cikin dakin mummy ya tsugunna har kasa ya gaidata yayi kamar baisan duk wani abunda yake faruwa ba,
Dakyar mummy ta amsa gaisuwarsa kansa yana kasa yace mummy dady yadawone? Yakirani datsu wai yana nemana, harara mummy ta watsa masa tace eh ai kayi abunda za'a nemeka ne ai dan kaniya, sadam yayi magana cikin wata innocent voice yace me yafaru mummy? Dan kwalo tayi masa tace haka kaji maras kunya au bakamasan abunda kayiba?
Sadam ya sunkuyarda kai mummy tace tashi muje wajan dadynku hana jiranka kema abida taso nan mutafi,
Cikin drama sadam ya zaro ido yace abida! Mai kuma yakawoki? Ban fada miki kidaina fita bada izinina ba?
Mummy tace eh ai dole kafadi haka ka jibgeta bakaso tazo tafada ba, sadam yace nikuma? Mummy tace A'a ni! Shiru sadam yayi yafice daga dakin zuwa shashin dady, durkufe abida da mummy sukazo duka sameshi gaban dady bayan sun shigo dady yafara magana da fadin sadam kabani makaki i am disappointed 😔 sadam harka sanya ahnnu ka doki mace? Eyeh sadam? Bakada hankaline? Kataba kallon ko zungiro nayiwa mummynku? Sadam macen auranka itace abin duka a wajanka, kaban mamaki banji dadiba sam da abunda ka aikata, Allah yagani sadam Allah ne shaida inabin bayanka a komai amma bazan goyi bayanka adukan yar mutane ba,
Advertisement
Mummy tace ai wallhy dabadan dadynku ya hananiba sadam yau da saina sharara maka mari abunda ban taba yimaka shiba iya tsawon zamana dakai da yau saina yimaka, saboda abunda kayi kaban mamaki kanuna banda girma akan idonka ka dubi abida ka daketa akan wata kaskantacciyar matarka?
Dady yace sadam baka kyautaba gaskiya a yanda ta nuna min kana nuna banbamci atsakaninsu kuma bata isa yin maganaba saika hauta da fada kamar zata daketa jiya kuwa saida ka dakeba,
Sadam baice komaiba saida ya tabbatar sun gama sannan yace Dady ka gafarceni amma ni bansan me kuke magana akai ba, ita abidar ce tace na duketa?
Mummy tayi salati ta sanarwa ubangiji tace kaji yaro karya kenann akaia maka?
Sadam ya girgiza kai cikin iya kwarrwa a drama yace ni banceba mummy saboda banida masaniya akan abunda tazo tafada muku, amma data fadi abunda tazo tafada danima anjirani anji abunda yafaru kafin ayankr hukunci,
Dady ya jijjiga kai yace hakane dama idan anji ta daya bangare ajira aji na daya bangaren saboda maslaha akeso baza'a taba fahimta ba idanba an tsaya anji tabakin kowaba amma dukda haka sadam bazan goyi bayanka a duka ba, wannan ba dabi'ar mijin kwarai bace koda kaine mai gaskiya zan hukuntaka a hakan dakayi, dan ba dalili bane dukan mace, sadam ya girgiza kai yace sam dady ni ban dakeba ba, sai dai idan sharri taso hadawa shine zatace na duketa, dady ai idan akazo akace maka zan iya dukan mata zaka karyata danni koda gigin wasa ban taba tunanin saka hannu jikin matata da duketaba, kuma itama abida ban duketaba, dady yace toh wannan abu da daure kai yake kuma tacemin baka dawowa sai karfe dayan dare idan kadawo asubahi kake ficewa menene amfanin hakan,
Inna lillahi sadam tafadi sannan yadubi abida da mamaki yace abida kifadi tsakaninki da Allah nine bana dawowa gida sai shadaya? Abida zatayi magana yayi saurin katseta yace dady duk rintsi bana wuce 10:00pm awaje kuma dalilin dayasa nake kaiwa haka saboda sawwama da batada lpy ne,
Advertisement
Kuma maganar fita asubahi kuma dady idan ta kwanta bacci yanda kasan kasa bata tashi har lokacin fita aikina sai dai na shirya kaina mostly awaje nakecin abinci ta dalilin haka har ulcer nakamu dashi nafada mata taki gyarawa shine kawai nake wucewa gidan sawwama naci abinci daganan na wuce dady kaga laipina a wannan lamarin?
Girgiza kai dady yayi yace A'a abida kuwa tasake baki kawai tanajin sharrinda sadam yakeyi mata,
Sadam yacigaba da fadin dady ko jiyan datake cewa na duketa ban duketaba nadawo tana fadamin bakaken maganganu duk wata maganar datazo bakinta ta tsaremin hanya ta hanani wucewa shine kawai na tureta na wuce hakanma bai isheta ba har kofar dakina tabi tana bubbugawa tana fadin maganganun da sukazo ranta ban kulataba saida nafito sallar asubahi nasameta kwance a kofar dakina tana jira nafito tayi bala'i nikuma dana fice yasa ban dawoba gudun rikici amma dady kaga hakan danayi mata bai isheta ba har saida tabiyo nan ta hadani da sharri,
Jijjiga kai kawai dady yakeyi mummy kuwa sai salati tana bin abida da harara mummy tace aikuwa idan hakane abida baki samu saraba wallhy gara ki canja hali tun wuri kuka abida tasaka ganin batada kalaman da zata wanke kanta ta rufza da ita, mummy tace kinsan kece maras gaskiya amma kika saka inata bala'i inata bala'i da wani wajene nan da kinsakani jin kunya,
Dady ya girgiza kai yace abida baki kyautaba idan kika yiwa mijinki kazafi ribar mai zakici?
Karki sake yin haka koda wasa ko banan ba, yanzu da wajan abbanki kika kai wannan zancen kinsan zai dauki zancen da zafi saboda bbu mahaifin da zaiji an duka masa ya yakyale, haka bbu kyau karki sake, abida tanason yin magana amma kuka ya hanata tanata fadin Allah dady,,, Allah dady,,, mummy tace rufamin baki ki tashi mutafi, tatashi taja hannunta suka fice, sadam zuciyarsa tayi sanyi amma abida tadan bashi tausayi,
Sai bayan yagama shirya drmarsa sannan hankalinsa yadawo kan sawwama a gaugauce yayiwa dady sallama yafita dady yace toh adaici gaba da hakuri kasan lamarin mata sai hakuri koda shekarunku daya da mace to sai kayi hakurin zama da ita saboda hankali bazaizo dayaba,
Sadam yace bbu komai dady,
Sadam yayiwa mummy sallama yatafi duk da dantane amma saida tadanji kunyarsa na zakewar datayi,
Mummy adaki fada take yiwa abida tana fadin ahakan abida kikeso mijinki yasoki ya kaunace ki? Ashe dama ke shashahsha ce? Bakisan yanda zaki tarairayi miki ba ki kula dashi? Sokuwa kai, tun wuri ki farka daga mafarkin da kikeyi kina jina? Koh wallhy abida kisan mai yake miki ciwo ki nemi hanya tun dare baiyi mikiba, daga masifa kuma sai mummy tadawo yimata nasiha, har abida taji zuciyarta tayi sanyi amma dai ranta cike yake fall da tunanin zancenda sadam ya shirya dama gaskiyar hausawa da sukace idan baka iya kama barawoba shi barawo zai kamaka,
Har dare abida takai agidan mummy sannan tatafi kafin tatafi sanda mumy tace mata kada tasake ji idan takoma karta sake dago da maganar."
————————————————
Nabila-Yarima
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial6 Chapters
Weapons Don't Have Names
Replicants. Dogs of war, their leash held by greedy corporations. Living weapons with serial numbers instead of names. Genetically perfect soldiers, created for one purpose and one purpose only - to complete the mission at any cost. But what are they to do when the battlefield is far away, commanding officers are gone and they are on a peaceful planet that belongs to the enemy? Two replicants must not only escape the enemy territory, but also deliver two civilians to the HQ. However, their charges are doing everything they can to sabotage the mission and the orders are clear - they can't be left behind or killed.
8 162 - In Serial15 Chapters
My Hero Academia: Hero's Horizon
A young man after being killed gets a second chance at life and not only that but in a world he loves and knows will help prove to himself that he deserves this second chance. Follow him through UA High as he makes friends, allies and enemies alike. (Also posted on Fanfiction.net, Archive of our own, Wattpad.com and quotev.com)
8 179 - In Serial6 Chapters
Rebound of Lost Souls
On the final day of Summer Break, Seth and four of his closest friends set out to explore an abandoned building before school is back in session. But his plans are ruined when they're unexpectedly murdered. Waking up in an open prairie, devoid of any civilization, Seth must figure out what to do next. Updates are usually on Sundays.
8 161 - In Serial8 Chapters
The God Complex
Alon wishes to be remembered—to stamp his existence on this cruel world, to engrave the fact that "he was here" into the very Earth. This is his sole purpose; To be important. For what greater reason is there to exist if not to be remembered? People are special. People aren’t... Your actions in this life define how those left behind remember you. Once you die, you’re reborn and live on, if only for a time; The grander the actions in this life, the longer your second one becomes. Alon knows this better than anyone, and he will live in the minds and hearts of everyone in Krestelen longer than anyone that has come before. Krestelen is a place long forgotten by those outside its walls; known by most as the Cursed City of The Dead, with the Lower Tier of the City being abandoned by the Upper Tiers after an inexplicable Fog blanketed the entire sector thirty-four years ago. This Fog adds those unfortunate enough to be caught within it into the legions of Vacant roaming the empty streets of the city: A creature that has seemingly lost all reasoning and sanity, to wander around the streets crying into the palms of their hands as they beg for help, to be freed from their condition. This is the place that Alon, and the Gang led by his mentor Casian, shall steal the very source of what gives those in power—the rightfully ruling family, the Deramore's—their ability to live in luxury as those below in the Lower Tier struggles to survive. They will forever be cast into the annals of the history of this cursed place—for better, or for worse.
8 160 - In Serial15 Chapters
The Leeches Loom
A young girl struggles with her newfound magic.Two women seek vengeance for two very different reasons.A pair of hunters explore their supernatural bond. Strangers cross paths after the sudden and mysterious destruction of a major city, plunging into turmoil a nation still in its infancy. Together, they find themselves embarking on a quest to uncover the sinister plot wreaking havoc across the empire. It is a story of perseverance, revenge and found family. Updated every Wednesday at midnight PST over at leechesloom.com, but I'll be crossposting it over to RoyalRoad for ease of reading!
8 121 - In Serial5 Chapters
°•♡Always♡•° 《Rosilla oneshots》
Bunch of Rosilla oneshots that i have probably written in 2am!Feel free to suggest some things!☆Hope you like it!Lots of love,Me😁
8 182

