《ƘADDARAR RAYUWA》K page 50
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
"
Eh toh yauma dai nace banyi editing ba🙃
Page 50
Sadam bai sanarwa sawwama cewa harda ita mummy ke nema ba yadai cemata kawai mummy nemansa dan haka zaije baisan menene ba amma bazai dadeba zai dawo,
Sawwama najin haka tace masa itama zataje ta gaida mummy yanzu rabonsu da gidan 1month kenan tun farkon fara rashin lafiyarta, Sadam yace bazata jeba dan batada lafiya, haka badan tasoba ta hakura tayi masa addu'a tace yagaida mummy, yafita zuciyarsa cike da tsantsan kaunar sawwama, addu'arta agareshi kullum tana kara soyayyarta gareshi yakanji dadi da sanyi cikin zuciyarsa idan tanayi masa addu'a,
Bai dauki lokaci ba ya'is gidan mummy baibi wajan abida ba yadaukota dan idan mummy tatashi banbanmi sai yabata excuse dakyau tubda zataga abidarma bai zoda itaba, amma mene sadam yana isa yasamu abuda tarigashi isa,
Da wani irin kallo sadam yake jidan abida dan bada izininsa tafitoba, ita kuwa ko ajikinta batamasan laifin datayiba kallon dayake matana bata daukeshi dawani nufiba, sadam batareda ya gaida mummy ba yadubi abida yace ke waya baki izinin fitowa? Kin tambayeni ne kika fito?
Bata rai abida tayi tace naga mummyce takirani tanason ganina shine nataso nataho,
Harara ya balla mata yace shikenan dan mummy ta kiraki tanason ganinki saiki taso kizo? Batareda kin tambayeniba ke kike auran kanki?
Cikin fada yace karki sake min haka idan kika sake fita bada izinina ba ni nasan matakin dazan dauka,
Mummy dake zaune tana jinsu ta dakatar da sadam tace kai kaga ya'isa haka haba tsabar masifa na azalazalarka ko gaisuwa bakaiba kafara bala'i,
Sadam yakara hade rai yace amma mummy yakamata tafito bada izinina ba? Mummy tace toh naji ke abida karki sake fita bada izininsaba kinji? Ko'ina zaki kira ki sanar masa tukunna,
Abida cikin rashin kuwa tafara fadin toh fisabilillahi mummy kawai sai yaso yahau kaina da masifa, Dan yana aurena shine akace ya cikamin kai da masifa, mummy baifa wani girmeniba amma kiji yanda yake yimin fada,
Dankwalo mummy tayiwa abida tace hungo nan naki gidanku mijinnaki kike fadawa haka? Kinci gidanku, tura baki abida tayi mummy ta bata rai tace maza bashi hakuri inajinki tun kafin na bata miki rai,
Abida ta tura baki kamar zai taba kofa tace kayi hakuri,,,,,,,..
Sadam yayi kamar bai jiba mummy tace kai sadam ba magana ake dakaiba bakajin tana baka hakuri! Uhum sadam yace mummy tace banjibafa mai kace,
Advertisement
Adakile yace naji,
Mummy tace kaji yara daga zuwanku kuna neman hargitsamin gida, sannan tajuya wajan abida tafara yinata fada mai kamada nasiha tana fadin shi miji babu ruwansa da girma ko shekaru, har indai Allah yabashi girmansa na miji yaci sunan miji toh agirmamashi ayi masa biyayya, mummy taringa zuba zance tashare sadam karma wanda ta manta dashi a wajan, shima sadam danna wayarsa yakeyi amma hankalinsa yana garesu mummy zagewa tayi tana koyarwa abida yanda ake zama da miji,
tanayi tana fadin idan ke kika gaza sai karamar yarinyar nan tazo tayi masa tunda kinganta karamar yarinya amma Allah ya zuba mata kinibibi da riya,
Mummy takama haba tace ohh ni naga ya ranar daya kawota da ladabin karya, yarinya kamar ta sabeni ta goyani araina ina fadin idanma ke mayyace kyaci kanki kuma badai ki shiga rainaba komai zakiyi, mummy tace aiko abincin data girka ban yarda naciba, sadam yana jinsu amma tausayin sawwama yakeji aransa dan ita tanayin abune zuciyarta daya bawai dan asota kokuma ta gwada bajinta da riyaba, takanyinr da kyautatawa amma hakanma ba'a ganiba baisan mai sawwama tatareda mummy ba baisan kuma bai yasa tayi mata irin wannan tsnaarba, baisan yaushe mummy zata saukar da zuciyarta tafara son sawwama ba kodan kyawawan halayanta,
Sun dauki tsawon lokaci suna tadai sai daga bisani mummy tajuya ga sadam tace ina ita yar gwal(gold) din? Anbarta a gida kenan tafi karfin zuwa idan na kirata ban isada itaba kenan? Sadam yace ba haka bane mummy, mummy tace yayane toh idanba hakaba sadam! Kai da na'isa dakai bagashi nakiraka kazo ba? Abida dana isa da ita bagashi na kirata tazoba? Amma ita ai kaga yar gwal ce kai kanka baka isa da itaba bareni, yar gidan isassu ita kesa doka abi badai ita asaka mata tabiba,
Sadam yace mummy danaji kiranne urgent dake ba'a gida nakeba shine kawai nawuco idan naga komai lafiya sai nabi nadauko ita sawwama da abida duka sai muzo tare dan hankalina yatashi nadauka wani abun yafaru dake, tabe baki mummy tayi tace aida nadauka ishasshiyar bazata iya zuwa bane, girgiza kai sadam yayi, mummy tace maganace dakuma albishir danakeson yimuku dukda abun kaida abida kadai yashafa amma yakamata ace itama tana wajan dan haka kaje ka daukota ayi komai agabanta tagani,
Bbu musu sadam yamike yace toh mummy barinaje yanzu zan dawo mummy tace yawwa gara kam karka dade kadawo, sadam tun yana mota yakira sawwama yace halima tataimaka mata tashirya yanzu yana zuwa zasu taho gidan mummy,
Advertisement
Shi kadai a cikin mota yana tunanin wani irin abun albishir ne haka daya shafi shi kadai da abida banda sawwama? Ahalin yanzu yasan duk wani abunda yashafeshi yakamata itama ya shafeta amma abida kadai yashafa?
Haka yaketa saka da warwara cikin zuciyarsa yasaka wannan ya kulla wancan harya isa yasamu su. Shirya dan haka kai tsaya suka fito har bakin mota halima tarakata sannan takoma ciki shikuma sadam yaja mota suka tafi, ko'a mota sawwama kwantar dakai kawai tayi jikin seat dan sam jikinta babu karfi kokadan, a hankali sadam yake tuki har suka isa, koda suka isama yadan dade cikin motan dan sawwama bacci tafara bayaso yatasheta saida ita kanta taji mota bata tafiya tana bude ido kuwa taga sun iso,
Dasuari ta kalleshi ya zuba mata idanuwan ita kawai yake kallo tana baccinta, idanuwansu yana haduwa waje daya ya sakar mata murmushi itama ta maida masa nata sanyayyan murmushin tashafi fuskarsa tace yaya sadam mun iso shine baka tasheniba kabarni inata bacci?
Shafan fuskanta yayi a hankali sannan yadanja hancinta yace banason abunda zai tabamun baby bane shiyasa gara kiyi baccinki ko awa nawane ni zan jiraki ahaka, murmushi tayi tayi brushing lips dinta akan nasa dake motan tinted ne bbu mai hangen ciki, lumshe idanuwa yayi hadeda saukarda ajiyar zuciya yace Alhamdulillah da samun mata kamarki, yar garamar dariyar jin dadi tayi itama tace Alhamdulillah da samun nagartaccen miji kamarka, lumshe idanuwansa yayi ya tura mata lips din, a hankali takai lips dinta kan nasa saida tabari yagama sakewa akan abunda tafara yimasa tayi bitten din lips dinsa a hankali amma yadanji zafi tayi saurin sakewa tasaka dariya tabude motan tafita shima yafita yabita abaya, yana fadin tarage saurin datakeyi saboda ba lafiya gareta ba,
Harta shiga gidan bai cimmataba, ya girgiza kai kawai ya dai-daita tafiyarsa tabita abaya, da sallama tashiga cikin palourn mummy da abida su duka suka juya suna kallonta, sai ayau abida tataba sanyata a idanuwanta, zagin muryarta yasanya abida juyawa dafarko abida bata iya cewa komaiba tabita da kallo kawai da mamakin karancin yarinyar gata kyakkyawace gaskiya amma tayi karama dayawa, har takaraso abida batabar kallontaba, gaban kujerar da suke zaune itada mummy ta isa tazauna a kasa sai lokacin sadam ya karaso, cikin nutsuwa da ladabi sawwama ta gaisar da mummy, ciki-ciki mummy ta amsa, sannan tagaida abida, abida ko kulata bataiba hakan yasa sawwama dagowa caraf idanuwanta yasauka a cikin na abida tana wirga mata uwar harara, ko ba'a fadawa sawwamaba tasan wannance abidar uwargidanta, dan haka ta sake mata murmushi wanda yakara fitto da kyawunta, kulolun bakin ciki ya turnuke abida jitayi kamar tatashi tashake sawwama, akaro na biyu sawwama tasake gaidata bata amsaba takara wurga mata harara, sadam ya hasala yace kr bakiji ana gaidake bane?
Abida kamar zata fashe da kuka dan yanda zuciyarta ke kuna tace idan naji saime? Banyi niyyar amsawaba tarike kayanta, sadam yace abida ni kike fadawa haka? Abida tace anfadan ai ba'a dole, banason gaisuwarta, kallonta yayi kawai da bakin ciki rashin kunya dazatayi masa?
Zaki maimaita kalamanki yafadi afili,
Mummy tace kunga ya isheni ni bance kuyimin hayaniya ba kai sadam haka akeyi agabansu kana nuna kafison daya, ai gaskiya tafada ana dolene a gaisuwar? tunda bataso ai shikenan,
Jijjiga kai sadam yayi baice komaiba sawwama takara sadda kanta kasa,
Mummy tace yanzu muyi abunda yataramu anan ba wannanba dadynku ma nakirashi yacemin wani aiki zai karasa zai shigo idan yagama sai ayi murna taredashi,
Wata takarda tadauko ta mikawa sadam,
Tadauko wata ta mikawa abida tace kubude kugani kowa idonsa ya gaya masa,
Sadam ya bude takardab a hankali yanabi yana karantawa harya gama yadago yana yiwa mummy kallon rashin fahimta yana neman karin bayani,
Abida nagama karanta tatashi da muran ta daka tsalle tafada kan mummy."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial7 Chapters
Code Name: GLITCH
Major Xiomar Haydn is a damn good soldier, and an even better mechanic, although he does have a tendency to get himself thrown into the stockades for getting on the general's bad side. To keep him busy and out of trouble, Xiomar is assigned the task of repairing an old Mech that hasn't been touched in fifteen years. He knows he can fix it--he's Chief Mechanic. What he doesn't know, however, is that GLITCH has a mind of its own. Literally. In the midst of a war between two countries, Xiomar and his newly-repaired Mech are caught in the middle. The enemy is trying to obtain GLITCH's technology... the power to give their own Mechs sentience and dominate the world. Xiomar finds himself pondering the morality of forcing a sentient being to fight on his behalf, and what that means for him as a dutiful soldier. With the future filled with uncertainty, Xiomar and GLITCH are certain of one thing--no one's going down without a fight.
8 209 - In Serial21 Chapters
Just Another Isekai
Daniel, a moody college kid hates his boring mundane life. He hates his stupid family and his stupid world preferring the fantasy worlds in video games and books instead. Luckily for him Daniel has been summoned to the forgotten world of Utradem. Finally he will get to live his isekai dream! Utradem is a forgotten world for a reason though, and his summoners have there own plans for Daniel. This is my first time writing and I am mostly just doing this to pass the time. Expect lots of mistakes and wierd/ improper formatting. My uploads will likely be inconsistent at best (going to try and update on wednesdays and fridays). The chapters may also be edited as I go along. That said I hope you enjoy and any feedback is welcome. Cover Image does not belong to me it can be found here; https://www.freeimages.com/photo/harnas-1480681
8 185 - In Serial6 Chapters
The Landvaettir
Varen Ashtar, a Junior Archivist with an unhappy past, is sent to investigate the truth of a prophecy he uncovers. It will send him far south into the Unknown Territories, where Vaettir roam without number. Will he succeed in his task? Or will his time run out before the Cataclysm cleanses the world?
8 151 - In Serial23 Chapters
You Found Me [ Kim Seokjin × Ahn Heeyeon ] (BTS & EXID / Hani × Jin)
"Then you found me,you didn't buy the front that I was showing everybody.You found me,you saw the scared boy inside of me that knew nothing.You found me, my flaws you found perfect, you loved me."A Kim Seokjin (BTS' Jin) and Ahn Heeyeon (EXID's Hani) Alternate universe!Rated teen fan-fictional story.BTS & EXID Fanfiction.I do not own all the names stated on the story.If you happen to read a story that is similar to this, it's just purely coincidental!Lastly, inspired by David Choi's song "You Found Me".
8 148 - In Serial56 Chapters
||Falling From The Sky||Black Clover x Reader||COMPLETED||
SATUS: COMPLETED (✔)(Y/n), Yuno and Asta aim to become the Magic Emperor, but in this world magic means everything. (Y/n) learns the true meaning that peasants are weak and that the powerful are selfish. Instead of losing hope, she gains hope to get stronger and become the Magic Emperor to rid of laws of social classes.In her new squad, (Y/n) starts to grow stronger and develop bonds with the people around her, some start falling in love with her cockiness and childish behaviour, while others might be filled to brim with jealousy, may it be in power or beauty. Will these bonds grow stronger and turn in something more? Or will they drip with poison of hatred and jealousy? Follow her as a new adventure begins, a new twist of fate when she is bestowed with a heavenly grimoire, now her fates are connected with God."I'd rather them take me than my family. I'd rather them hurt me, then the ones I care about.I'd rather die then have them taken, I'd take the pain to stop seeing them cry. I would...."-(Y/n)HIGHEST RANKINGS#1-Clover#4-Leopold#2-Yuno#1-Asta#1-Blackclover#1-Marx#2-Yami#4-Licht#1-Silva#3-Nozel#4-Fuegoleon#1-Vermillion#1-Blackcloverxreader#1-MagicKnights#3-Luck#213-Klaus#2-Mars#1-Blackcloverfanfiction#6-leo
8 192 - In Serial16 Chapters
Those Eyes (Ayato X Laito)
Yaoi WarningLaito always dreamt about his mother. His dreams always bothered him and he would always see Cordelia's faces everywhere. He hated her but at the same time he misses her. He mostly hangs out with Ayato just so he could stare at his eyes, those same emerald green eyes just like Cordelia. Laito started giving Ayato affection and little by little until Ayato fell in love with Laito. But will this work out for them, read to find out.
8 181

