《ƘADDARAR RAYUWA》K page 49
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
"
Page 49
Kwanan su sadam biyu da tafiya mummy tafara tunanin raina mata hankali kawai sadam yayi bbu aiki kawai yadauki matarsa ne sunbar gari,
Kokuma suna gari suna wani waje daban,
Alokacin dayazo mata da zancen tarasa mai ya cushe a kwakwalwarta harta yarda da tatsunuyarsa nacewa aiki aka turashi domin kowa yaji zancen yasan akwai wata a kasa,
Mummy tayi bincike a wajan aikinsu ta tabbatar babu wani aikin da aka turashi hasalima hutu ya dauka,
Wani irin tsanar sawwama yakara sauka a cikin ranta danta datake kallo mai hankali da nustuwa yau dayi mata biyayya shine ya bijire umarninta akan sawwama yau har takaiga yayi mata karya ya rena mata hankali,
Duk yanda takaiga son samunsa a waya amma sam wyarsa taki shiga switchoff, mummy kullum da dacin wannan abunda sadam yayi mata take kwana tana tashi har,
Sadam a nasa wajan kamar yasan cewa mummy zatayi bincike ta gano gaskiya hakan yasa duk wata hanyar da zata saddashi da mutannen gida ya datseta zai dauki duk wani hukuncinta dazai biyo baya tunda yasamu farin ciki a tafiyarsa sam bazai damu da kalamanta da maganganunta ba,
Saida su sadam sukayi 2weeks a yankari sannan suka dawo gida, sunyi isowar dare hakan yasa bai sanarwa da kowa dawowarsa ba sai washe gari yashirya yatafi wajan abida,
Fuska a daure yasameta saboda itama jikinta yabata sadam ya raina musu hankaline kawai,
Gashi cikin 2weeks dayayi sau daya sukayi waya,
Sadam shi kansa yasan bai kyautawa abida ba hakan yasanya ya shiga da fuskar tausayi, ganin yanayinta saita bashi tausayi, yasan dole da hakkinta akansa kuma bai dace ace yayi 2weeks bai kira yaji lafiyarta ba,
Zama sadam yayi yaringa lallashinta da kalamai masu dadi wanda harya sanyata ta sauka daga fushinta, sadam bai samu fita a gidanba har rana domin abida ta narke masa gabaki daya ta hanashi motsawa nan da can, saida aka kira sallar azahar sannan yasamu yayi mata wayo yafita hakanma cewa tayi sai dai yayi sallah agida, bai yarda ba dai yayi tayi mata dadin baki dacewa yanzu zai dawo hakan yasa tabarshi yafice.
Advertisement
Gabansa yanata dukan uku-uku a yayinda yanufi gidansu dan baisan mai zaije ya taras wajan mummy ba,
Yasamu dawowarta daga office kenan tana zaune tana hutawa yashiga da sallama mummy ta amsa sallamar ciki-ciki yanda bazai jiyotaba ta kauda kanta gefe sadam ya iso gabanta ya tsugunna cikin dar-dar yace sannu da gida mummy ina wuni ya aiki? Ya jera masa gaisuwa cikin taraddadin mai zai biyo baya,
Mummy tayi banza dashi ta debeshi ta watsar sadam yakara maimaitawa amma yacce kasan babu mutum a wajan zaman wani lokaci sukayi babu wanda yasake cewa komai,
Sadam ganin fuskar mummy babu alamun koda wasane ya sanya duk gabobin jikinsa sukayi sanyi, domin mummy tasha murr sosai kamar ba mummynsa ba,
Yankewa kansa kawai yayi ya dauki laifinsa yafara bata hakuri domin yasan halin mahaufiyarsa zata gano gaskiya yasan yanzu haka tagani gaskiya,
Sun kuyarda kansa kasa yayi yace mummy dan Allah kiyi hakuri ki gafarceni nasan nayi miki laifi amma in sha Allahu bazan sake kwatanta hakaba,
Harara mummy ta watsa masa kusan 5minute kamar bazatace komaiba sai kuma tace sadam ni zaka nemawa hankali? Ni sa'arkace? Ashe har kayi wayon da zaka iya yimin karya? Akan wata shashashar matarka? Yaushema aka haifekane sadam nawa kake? Dahar zakayi tunanin yimin wayo batareda nagane ba,
Nawa kake sadam? Yaushe aka haifeka?
Sadam yayi kasa dakai yace mummy kiyi hakuri nasan nayi laifi amma Mummy bawai na raina miki hankali bane, mummy duk wanda zai raina miki hankaki a duniyar nan ni bazan taba jituwa dashiba balle har ace ni dakaina na raina miki hankali,
Mummy tace nanawa kuma sadam? Nanawa? Gashinann matarka ta zugaka ka yimin karya, ga gujeni, sadam yace wallhy mummy ba laifinta bane itama batasanda tafiyarba,
Salati mummy tayi ta sanrwa ubangiji tace sadam! Nashiga uku kana cikin hankalinka kuwa? oh kareta kakeyi? Gani uwar banza nayi mata karya koh? Saurin girgiza kai sadam yayi yace A'a ba haka nake nufiba mummy kiyi hakuri, in sha Allah haka bazata sake faruwaba,
Mummy tace shikenan ai tunda haka kace karka kuma sadam dan zaka hadu da fushina,
Sadam yace nagode in sha Allahu mummy bazan sakeba,
Allah yayarda mummy tafadi sadam yamike yayi mata sallama yatafi yana tunanin wannan sawa kai ijaba irinna mummy."
Advertisement
Sadam yakanyi kwana daya gidan wannan sannan yayi kwana daya gidan wancan ko sau daya bai taba hadasu waje dayaba,
Babu wacce tataba ganin wata acikinsu,
Sau daya yataba kaita ta gaida mummy basu samu tarban arzikiba kallon kirki basu isheta ba, har turmin zani tadauka a cikin na lefenta mai kyau da tsada da turare da man shafawa dasu sabulu takai mawa mummy su hassana da hussaina kuma yan kananun kaya ta deba musu, ko kallon arziki mummy batabi kayan dashiba, sawwama kuwa ko ajikinta bata dauki hakan a komaiba dan bai dameta ba, haka tatashi tayiwa mummy kaf aikin gidan komai da komai dake a weekend sukace, ba sannu babu madallah haka tagama aikin, harta da abinci ita tayi da mummy tashiga kitchen tabita ta karba sai tafice tabar mata kitchen din tayi tagama takai dining, tadawo ta zauna,
A sace mummy take kallonta ko zataga wata makusa a tattare da ita amma bata ganiba, gata karamar yarinya su hassana da hussainama zasu girmeta ko suzo sa'oi, aranta tana tunanin idan yartace bbu abunda zaisa tayi mata aure kamar haka,
Zuciyar mummy nason sauka akan taanar sawwama datakeyi saboda kyawawan halayanta datayi noticing amma mummy kyam haka tahana zuciyarta jin komai gameda ita, sai kara cusawa ranta takeyi cewa danta yaki bin umarninta akanta, ta mallake mata da aikuwa nan da nan taji wata sabuwar tsanarta tadawo cikin zuciyarta,
Koda zasu tafi mummy ta make adaki kin fitowa tayi suyi sallama sadam da kansa yashiga yace mata zasu tafi tace Allah raka taki gona, yafito yacewa sawwama su tafi amma fir haka taki tafiya wai saitayiwa mummy sallama, kofar dakin mummy yanuna mata taja yatsaya cikin ransa yana zullumin abunda zata taras, dankoda yakawota baiso barinta tawuniba alokacin yaso su tafi amma haka taki tafiya wai ita wuni zatayi haka yatafi yanata tunaninta, akai-akai yake dawowa gidan dubata, hakan kuwa ba karamin karawa mummmy haushin sawwama ba yayi aranta dan tasan dan ita yake wannan ziryan, shiyasa da zasu tafi taki fitowa,
A zaune bakin gado sawwama ta sameta tashiga da sallama mummy ta amsa ciki-ciki, har kasa ta tsugunna tacewa mummy, zamu tafi sai anjima, mummy kanta yana gefe tace mujima dakyau, sawwama ta mike tafita, mummy tabi bayanta da kallo,
Ita kanta acikin zuciyarta tasan sawwama tafi abida kirki, kyautatawar da sawwama tayi mata a yau kadai abida bata taba gwada makamancin hakaba."
Tafito tasamu sadam tace muje yaya sadam fuskarta yakebi da kallo ko zaiga wani yanayi amma sam baiga komaiba ajiyar zuciya yasauke yana tunanin ko mummy tafara saukowane toh? Dan yasan kyawawan halin sawwama dole idan ka zauna da ita kasota,"
Su hassana kuwa har mota suka rakata da murna kowannenssu a fuska ga dukkan alamu sun saba da ita adan zamansu na yau, suna cemata sai sunzo, itama da murmushi a fuskarta tace inajira sai kunzo."
Kwanansu sawwama biyu zuwa gidansu mummy tafara laulayi babu kama kafa gashi laulayin yazo mata da zafi,
Koda da yakaita asibiti aka auna 2month cikin dai-dai da lokacin aurensu, sadam bai bari kowa yaji labarin cikinba shine yake jinyarta akai-akai yake zuwa gidanta ranar dayake gidan idan yadawo a aiki baya motsawa ko ina,
Ganin idan baya gidan tana shan wahala yasanya ya dauko mata halima kanwarta dan sam bayaso tamotsa ko nan da can dan bakaramin soyayya yake nunawa cikin ba,"
Ana cikin wannan halin mummy tayi masa waya tanason ganinsa shida sawwama da abida duka suzo gobe, sadam baisan excuse din dazai bawa mummy amma sawwama kam sam batajin dadi yana ganin zaijene kawai batareda itaba."
Ih toh nace yauma dai banyi editing ba😀😀
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial42 Chapters
Slightly Contradictory
I did not expect to die, but for the same outcome I would die once more. I did not expect to wake up again, but as soon as I did I was told to die. I did not expect anything from this new life, which has since given so much. I still do not know what the future holds, but there is one thing I am certain of; I will fight to get there if I have to, and I will fight twice as hard for my family!
8 165 - In Serial93 Chapters
Smith-Knight
In a world where kings rule over the land, knights live and die by way of the sword and monsters roam the land, sea, and sky. A young blacksmith will have his chance to make a name for himself! Along with the allies he makes on the way, from Humans, Demons, Elves, and more! Will he be able to live through it and gain greatness beyond his hopes and dreams? Find out by reading! (Updates Every Sunday At 12 p.m AST)
8 115 - In Serial13 Chapters
Fracture: Tales of the Broken Lands [Re]
Eternity's march wears down even those destined to see its end. He was one of them, one of the first and last. But... nothing went as it should have. The enemy came and its legions consumed the worlds and all those who rose to defend the cosmos. Everyone except him. Despite all, he survived, fighting until he had nothing left, yet even as he welcomed it, the end never came. Jack was given another chance. His fate brought him to a plane called Fracture, a nexus of the cosmos, where broken things go to find new purpose. Will he find his purpose? Or will the machinations of those who rule the Broken Lands lead him to ruin? *** This is a rewrite of my first story. It is a litrpg with elements of cultivation in a setting filled with fantasy and scifi trappings. For old readers returning, the story will be significantly different, but core components of the characters will remain the same. I hope you enjoy it.
8 141 - In Serial9 Chapters
Soy una mazmorra, pero ¿realmente es un mundo de fantasía? (Spanish)
Sinopsis: El protagonista despierta en un lugar extraño, sin poder moverse, hablar o hacer algo al respecto ... o eso creia. Resulta que es una "Mazmorra" y tendra que afrontar su nueva vida, en un mundo desconocido con un futuro incierto, y si falla, consecuencias que le prometen mucho sufrimiento. Pero al menos puede crear lo que imagine. Longitud de cada capitulo: Aproximadamente 3900- 5000 palabras. Trato de que cada capitulo sea largo. Que espero como Autor: Si te ha gustado la historia o hay partes que no te gustan o no comprendes, comenta. Me ayudaria a saber como mejorar. Las criticas constructivas son muy bien recibidas y los animo a hacerlo. Esta obra la realizo yo, no es un fanfic. Derechos de Autor: Licencia Creative Commons Attribution-NonCommercial-ShareAlike 4.0 DESCARGO DE RESPONSABILIDAD SOBRE LA IMAGEN: La foto de portada no me pertenece. Si el autor de la imagen desea que la retire, lo hare sin ningun problema. Eventualmente la cambiare por una que se adapte mejor
8 152 - In Serial51 Chapters
Earth II: Starting From Zero
This story begins far in Earth’s future. The once-beloved planet is dying from decades of pollution and poor management. Accepting nothing could be done to prevent it, the world’s scientists come together to create a new Earth. Fearing human incompetence, they create an Artificial Intelligence (Ai) to create the new Earth in the image of the old one. However, things do not go as planned, and the Ai creates the new planet in the image of a fantasy game. Now humanity must rebuild in a whole new world full of dangers and mysteries: Starting from zero. This novel follows the young male protagonist “Artie.” After a series of tragic events, he vows to destroy the cruel new planet and return to Earth. Through his journey, he raises armies, advances civilization, and attempts to restore technology to its former capacity.
8 198 - In Serial4 Chapters
first love.. (Child tord X reader) Part 1/3 (discontinued)
(discontinued) I'm no good with descriptions... but the Title says it all.This is a child reader x child Tord.⋘ 𝑙𝑜𝑎𝑑𝑖𝑛𝑔 𝑑𝑎𝑡𝑎... ⋙1/3 books𝐖𝐚𝐫𝐧𝐢𝐧𝐠fighting (gasp.)Minor cussing.𝕯𝖎𝖘𝖈𝖑𝖆𝖎𝖒𝖊𝖗I do not own any of the eddsworld charactersall eddsworld themed rightfully owned by eddsworldcredits to the person who owns the art on the cover.I do not own any of the art in the story credits to the owner.
8 149

