《ƘADDARAR RAYUWA》K page 49
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
"
Page 49
Kwanan su sadam biyu da tafiya mummy tafara tunanin raina mata hankali kawai sadam yayi bbu aiki kawai yadauki matarsa ne sunbar gari,
Kokuma suna gari suna wani waje daban,
Alokacin dayazo mata da zancen tarasa mai ya cushe a kwakwalwarta harta yarda da tatsunuyarsa nacewa aiki aka turashi domin kowa yaji zancen yasan akwai wata a kasa,
Mummy tayi bincike a wajan aikinsu ta tabbatar babu wani aikin da aka turashi hasalima hutu ya dauka,
Wani irin tsanar sawwama yakara sauka a cikin ranta danta datake kallo mai hankali da nustuwa yau dayi mata biyayya shine ya bijire umarninta akan sawwama yau har takaiga yayi mata karya ya rena mata hankali,
Duk yanda takaiga son samunsa a waya amma sam wyarsa taki shiga switchoff, mummy kullum da dacin wannan abunda sadam yayi mata take kwana tana tashi har,
Sadam a nasa wajan kamar yasan cewa mummy zatayi bincike ta gano gaskiya hakan yasa duk wata hanyar da zata saddashi da mutannen gida ya datseta zai dauki duk wani hukuncinta dazai biyo baya tunda yasamu farin ciki a tafiyarsa sam bazai damu da kalamanta da maganganunta ba,
Saida su sadam sukayi 2weeks a yankari sannan suka dawo gida, sunyi isowar dare hakan yasa bai sanarwa da kowa dawowarsa ba sai washe gari yashirya yatafi wajan abida,
Fuska a daure yasameta saboda itama jikinta yabata sadam ya raina musu hankaline kawai,
Gashi cikin 2weeks dayayi sau daya sukayi waya,
Sadam shi kansa yasan bai kyautawa abida ba hakan yasanya ya shiga da fuskar tausayi, ganin yanayinta saita bashi tausayi, yasan dole da hakkinta akansa kuma bai dace ace yayi 2weeks bai kira yaji lafiyarta ba,
Zama sadam yayi yaringa lallashinta da kalamai masu dadi wanda harya sanyata ta sauka daga fushinta, sadam bai samu fita a gidanba har rana domin abida ta narke masa gabaki daya ta hanashi motsawa nan da can, saida aka kira sallar azahar sannan yasamu yayi mata wayo yafita hakanma cewa tayi sai dai yayi sallah agida, bai yarda ba dai yayi tayi mata dadin baki dacewa yanzu zai dawo hakan yasa tabarshi yafice.
Advertisement
Gabansa yanata dukan uku-uku a yayinda yanufi gidansu dan baisan mai zaije ya taras wajan mummy ba,
Yasamu dawowarta daga office kenan tana zaune tana hutawa yashiga da sallama mummy ta amsa sallamar ciki-ciki yanda bazai jiyotaba ta kauda kanta gefe sadam ya iso gabanta ya tsugunna cikin dar-dar yace sannu da gida mummy ina wuni ya aiki? Ya jera masa gaisuwa cikin taraddadin mai zai biyo baya,
Mummy tayi banza dashi ta debeshi ta watsar sadam yakara maimaitawa amma yacce kasan babu mutum a wajan zaman wani lokaci sukayi babu wanda yasake cewa komai,
Sadam ganin fuskar mummy babu alamun koda wasane ya sanya duk gabobin jikinsa sukayi sanyi, domin mummy tasha murr sosai kamar ba mummynsa ba,
Yankewa kansa kawai yayi ya dauki laifinsa yafara bata hakuri domin yasan halin mahaufiyarsa zata gano gaskiya yasan yanzu haka tagani gaskiya,
Sun kuyarda kansa kasa yayi yace mummy dan Allah kiyi hakuri ki gafarceni nasan nayi miki laifi amma in sha Allahu bazan sake kwatanta hakaba,
Harara mummy ta watsa masa kusan 5minute kamar bazatace komaiba sai kuma tace sadam ni zaka nemawa hankali? Ni sa'arkace? Ashe har kayi wayon da zaka iya yimin karya? Akan wata shashashar matarka? Yaushema aka haifekane sadam nawa kake? Dahar zakayi tunanin yimin wayo batareda nagane ba,
Nawa kake sadam? Yaushe aka haifeka?
Sadam yayi kasa dakai yace mummy kiyi hakuri nasan nayi laifi amma Mummy bawai na raina miki hankali bane, mummy duk wanda zai raina miki hankaki a duniyar nan ni bazan taba jituwa dashiba balle har ace ni dakaina na raina miki hankali,
Mummy tace nanawa kuma sadam? Nanawa? Gashinann matarka ta zugaka ka yimin karya, ga gujeni, sadam yace wallhy mummy ba laifinta bane itama batasanda tafiyarba,
Salati mummy tayi ta sanrwa ubangiji tace sadam! Nashiga uku kana cikin hankalinka kuwa? oh kareta kakeyi? Gani uwar banza nayi mata karya koh? Saurin girgiza kai sadam yayi yace A'a ba haka nake nufiba mummy kiyi hakuri, in sha Allah haka bazata sake faruwaba,
Mummy tace shikenan ai tunda haka kace karka kuma sadam dan zaka hadu da fushina,
Sadam yace nagode in sha Allahu mummy bazan sakeba,
Allah yayarda mummy tafadi sadam yamike yayi mata sallama yatafi yana tunanin wannan sawa kai ijaba irinna mummy."
Advertisement
Sadam yakanyi kwana daya gidan wannan sannan yayi kwana daya gidan wancan ko sau daya bai taba hadasu waje dayaba,
Babu wacce tataba ganin wata acikinsu,
Sau daya yataba kaita ta gaida mummy basu samu tarban arzikiba kallon kirki basu isheta ba, har turmin zani tadauka a cikin na lefenta mai kyau da tsada da turare da man shafawa dasu sabulu takai mawa mummy su hassana da hussaina kuma yan kananun kaya ta deba musu, ko kallon arziki mummy batabi kayan dashiba, sawwama kuwa ko ajikinta bata dauki hakan a komaiba dan bai dameta ba, haka tatashi tayiwa mummy kaf aikin gidan komai da komai dake a weekend sukace, ba sannu babu madallah haka tagama aikin, harta da abinci ita tayi da mummy tashiga kitchen tabita ta karba sai tafice tabar mata kitchen din tayi tagama takai dining, tadawo ta zauna,
A sace mummy take kallonta ko zataga wata makusa a tattare da ita amma bata ganiba, gata karamar yarinya su hassana da hussainama zasu girmeta ko suzo sa'oi, aranta tana tunanin idan yartace bbu abunda zaisa tayi mata aure kamar haka,
Zuciyar mummy nason sauka akan taanar sawwama datakeyi saboda kyawawan halayanta datayi noticing amma mummy kyam haka tahana zuciyarta jin komai gameda ita, sai kara cusawa ranta takeyi cewa danta yaki bin umarninta akanta, ta mallake mata da aikuwa nan da nan taji wata sabuwar tsanarta tadawo cikin zuciyarta,
Koda zasu tafi mummy ta make adaki kin fitowa tayi suyi sallama sadam da kansa yashiga yace mata zasu tafi tace Allah raka taki gona, yafito yacewa sawwama su tafi amma fir haka taki tafiya wai saitayiwa mummy sallama, kofar dakin mummy yanuna mata taja yatsaya cikin ransa yana zullumin abunda zata taras, dankoda yakawota baiso barinta tawuniba alokacin yaso su tafi amma haka taki tafiya wai ita wuni zatayi haka yatafi yanata tunaninta, akai-akai yake dawowa gidan dubata, hakan kuwa ba karamin karawa mummmy haushin sawwama ba yayi aranta dan tasan dan ita yake wannan ziryan, shiyasa da zasu tafi taki fitowa,
A zaune bakin gado sawwama ta sameta tashiga da sallama mummy ta amsa ciki-ciki, har kasa ta tsugunna tacewa mummy, zamu tafi sai anjima, mummy kanta yana gefe tace mujima dakyau, sawwama ta mike tafita, mummy tabi bayanta da kallo,
Ita kanta acikin zuciyarta tasan sawwama tafi abida kirki, kyautatawar da sawwama tayi mata a yau kadai abida bata taba gwada makamancin hakaba."
Tafito tasamu sadam tace muje yaya sadam fuskarta yakebi da kallo ko zaiga wani yanayi amma sam baiga komaiba ajiyar zuciya yasauke yana tunanin ko mummy tafara saukowane toh? Dan yasan kyawawan halin sawwama dole idan ka zauna da ita kasota,"
Su hassana kuwa har mota suka rakata da murna kowannenssu a fuska ga dukkan alamu sun saba da ita adan zamansu na yau, suna cemata sai sunzo, itama da murmushi a fuskarta tace inajira sai kunzo."
Kwanansu sawwama biyu zuwa gidansu mummy tafara laulayi babu kama kafa gashi laulayin yazo mata da zafi,
Koda da yakaita asibiti aka auna 2month cikin dai-dai da lokacin aurensu, sadam bai bari kowa yaji labarin cikinba shine yake jinyarta akai-akai yake zuwa gidanta ranar dayake gidan idan yadawo a aiki baya motsawa ko ina,
Ganin idan baya gidan tana shan wahala yasanya ya dauko mata halima kanwarta dan sam bayaso tamotsa ko nan da can dan bakaramin soyayya yake nunawa cikin ba,"
Ana cikin wannan halin mummy tayi masa waya tanason ganinsa shida sawwama da abida duka suzo gobe, sadam baisan excuse din dazai bawa mummy amma sawwama kam sam batajin dadi yana ganin zaijene kawai batareda itaba."
Ih toh nace yauma dai banyi editing ba😀😀
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- End179 Chapters
Dimensional Sovereign
One day, I was given the mysterious power of Hwanmong. If I killed a monster in the dream then my level would rise in reality. My home in reality became a base in the dream. A dimensional strategy RPG where reality and dreams are linked! Earn money and become stronger! Now I will dominate the world.
8 1118 - In Serial192 Chapters
Minecrafts Reality
Follow Aeternum, an unlucky soul, through a world some would consider a blessing and some a curse. Robbed of his rightful afterlife, how will he make the best of his second life? On his adventure, he will struggle against and fight the world’s monstrous denizens. He is trying to survive using creativity and what little know-how he has while trying to enjoy life a little. Maybe, with enough effort, he will be able to escape his fate as the toy of a bored God. -----Author----- Thank you for checking out my light novel. I am a hobbyist writer who is still learning. I would appreciate any corrections people can make as well as constructive criticism. I hope that you enjoy the story! I personally made the cover art with photo editing. *edit* This story is the grinder I use to sharpen my writing skills further. Of course, I care for the story and wish to see it flourish. But, please understand that I have a long way to go to become a great author. Current schedule: 12am, UK standard time. 9pm, central standard time. Once per week! (Temp) V3 courtesy of Skye
8 140 - In Serial16 Chapters
Teenage Badass
Finn is a Helfwir, a monster hunter born. At the age of 8, Finn was capable of destroying a vampire with a plastic spoon. By the time she was 10, Finn knew a hundred ways of killing pretty much everything that went bump in the night. On her 14th birthday, Finn decides she wants to try living a normal life. She leaves home for Orsonville and enrolls in its high school. There, Finn will have to learn to deal with petty bullies, tenuous friendships , the hardships of teenage love and a werewolf cult that's hell-bent on world domination, all without revealing her true identity. This is shaping up to be a hell of a school year.
8 87 - In Serial8 Chapters
Whispers from the dark
During the dark times, the humans and elves decided to work together to defeat the Fiend. A high king among the humans was chosen, together with his archmage he defeated the Fiend. A few years of peace, until the high king lost it. He was convinced that the mages would steal the crown and take over his world. Scared as he was, he decided to hunt down everyone with magical abilities. Elves retreated to the safety of their forests and mountains, forever remaining a mystery to the humans. Many non-magical humans agreed to this plan of their lord, for they were also afraid that the mages would take advantage of their weaknesses. The mages tried to survive. The archmage, who was the former counsellor of the last king and protector of the royal family, protested. He wanted to solve this problem through politics. But nothing helped, and the archmage fled. The king got two sons, one was born a mage, and the other human. The king despised his mage son and banished him. His younger brother became the heir of the throne. Anger grew in the mage prince. He thought war was the only solution to this problem. Consumed by the will to gain power, he searched for followers who would fight the humans in order to stop the hunt on mages. The archmage tried to stop this evil plan of the prince. But the mages split in two groups. The necromancers, followers of the evil prince, who studied the crafts of the dark magic to terrorise their enemies and gain back the throne. And the sorcerers, followers of the archmage, who tried to peacefully restore the trust between humans and mages. But nobody knew the danger that was gaining back his power in the underground world. The archmage disappeared and a darkness swept over the world. Human, elves, mages, every creature awaited in fear the day the darkness would take back his control. Faelwen, a young woman, was put in the middle of this chaos. Even though her only priority was to survive. Hunted down by humans and evil beasts, who can she trust? And what whispers from the dark will reveal the secrets from the archmage?
8 142 - In Serial37 Chapters
After Dark
Eliza is a young, black jazz singer in 1920s New York City. Despite growing up sheltered, she begins to work at at Speakeasy during the prohibition era. Her life changes when she meets an Irish gangster by the name of William McGill. When they begin a heated affair, Eliza questions if she will ever become accustomed to his lifestyle.When * appears, it means that there are sexual themes in that chapter. Warning: Sexual content, alcohol, other adult themes
8 128 - In Serial133 Chapters
Avneil - being with you
Started: December 18, 2017Ended: August 13, 2019Status: Completed Editing: In process Description:Based on Avni and Neil's married life.....this story is a Fan Fiction of Avneil from the show Naamkaran.....this story continues from the point when Dayavanti is captured by the police......This story will be about the ups and downs of avneil through their beautiful journey of marriage....Do check it out if ur a Avneil fan...
8 539

