《ƘADDARAR RAYUWA》K page 49
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
"
Page 49
Kwanan su sadam biyu da tafiya mummy tafara tunanin raina mata hankali kawai sadam yayi bbu aiki kawai yadauki matarsa ne sunbar gari,
Kokuma suna gari suna wani waje daban,
Alokacin dayazo mata da zancen tarasa mai ya cushe a kwakwalwarta harta yarda da tatsunuyarsa nacewa aiki aka turashi domin kowa yaji zancen yasan akwai wata a kasa,
Mummy tayi bincike a wajan aikinsu ta tabbatar babu wani aikin da aka turashi hasalima hutu ya dauka,
Wani irin tsanar sawwama yakara sauka a cikin ranta danta datake kallo mai hankali da nustuwa yau dayi mata biyayya shine ya bijire umarninta akan sawwama yau har takaiga yayi mata karya ya rena mata hankali,
Duk yanda takaiga son samunsa a waya amma sam wyarsa taki shiga switchoff, mummy kullum da dacin wannan abunda sadam yayi mata take kwana tana tashi har,
Sadam a nasa wajan kamar yasan cewa mummy zatayi bincike ta gano gaskiya hakan yasa duk wata hanyar da zata saddashi da mutannen gida ya datseta zai dauki duk wani hukuncinta dazai biyo baya tunda yasamu farin ciki a tafiyarsa sam bazai damu da kalamanta da maganganunta ba,
Saida su sadam sukayi 2weeks a yankari sannan suka dawo gida, sunyi isowar dare hakan yasa bai sanarwa da kowa dawowarsa ba sai washe gari yashirya yatafi wajan abida,
Fuska a daure yasameta saboda itama jikinta yabata sadam ya raina musu hankaline kawai,
Gashi cikin 2weeks dayayi sau daya sukayi waya,
Sadam shi kansa yasan bai kyautawa abida ba hakan yasanya ya shiga da fuskar tausayi, ganin yanayinta saita bashi tausayi, yasan dole da hakkinta akansa kuma bai dace ace yayi 2weeks bai kira yaji lafiyarta ba,
Zama sadam yayi yaringa lallashinta da kalamai masu dadi wanda harya sanyata ta sauka daga fushinta, sadam bai samu fita a gidanba har rana domin abida ta narke masa gabaki daya ta hanashi motsawa nan da can, saida aka kira sallar azahar sannan yasamu yayi mata wayo yafita hakanma cewa tayi sai dai yayi sallah agida, bai yarda ba dai yayi tayi mata dadin baki dacewa yanzu zai dawo hakan yasa tabarshi yafice.
Advertisement
Gabansa yanata dukan uku-uku a yayinda yanufi gidansu dan baisan mai zaije ya taras wajan mummy ba,
Yasamu dawowarta daga office kenan tana zaune tana hutawa yashiga da sallama mummy ta amsa sallamar ciki-ciki yanda bazai jiyotaba ta kauda kanta gefe sadam ya iso gabanta ya tsugunna cikin dar-dar yace sannu da gida mummy ina wuni ya aiki? Ya jera masa gaisuwa cikin taraddadin mai zai biyo baya,
Mummy tayi banza dashi ta debeshi ta watsar sadam yakara maimaitawa amma yacce kasan babu mutum a wajan zaman wani lokaci sukayi babu wanda yasake cewa komai,
Sadam ganin fuskar mummy babu alamun koda wasane ya sanya duk gabobin jikinsa sukayi sanyi, domin mummy tasha murr sosai kamar ba mummynsa ba,
Yankewa kansa kawai yayi ya dauki laifinsa yafara bata hakuri domin yasan halin mahaufiyarsa zata gano gaskiya yasan yanzu haka tagani gaskiya,
Sun kuyarda kansa kasa yayi yace mummy dan Allah kiyi hakuri ki gafarceni nasan nayi miki laifi amma in sha Allahu bazan sake kwatanta hakaba,
Harara mummy ta watsa masa kusan 5minute kamar bazatace komaiba sai kuma tace sadam ni zaka nemawa hankali? Ni sa'arkace? Ashe har kayi wayon da zaka iya yimin karya? Akan wata shashashar matarka? Yaushema aka haifekane sadam nawa kake? Dahar zakayi tunanin yimin wayo batareda nagane ba,
Nawa kake sadam? Yaushe aka haifeka?
Sadam yayi kasa dakai yace mummy kiyi hakuri nasan nayi laifi amma Mummy bawai na raina miki hankali bane, mummy duk wanda zai raina miki hankaki a duniyar nan ni bazan taba jituwa dashiba balle har ace ni dakaina na raina miki hankali,
Mummy tace nanawa kuma sadam? Nanawa? Gashinann matarka ta zugaka ka yimin karya, ga gujeni, sadam yace wallhy mummy ba laifinta bane itama batasanda tafiyarba,
Salati mummy tayi ta sanrwa ubangiji tace sadam! Nashiga uku kana cikin hankalinka kuwa? oh kareta kakeyi? Gani uwar banza nayi mata karya koh? Saurin girgiza kai sadam yayi yace A'a ba haka nake nufiba mummy kiyi hakuri, in sha Allah haka bazata sake faruwaba,
Mummy tace shikenan ai tunda haka kace karka kuma sadam dan zaka hadu da fushina,
Sadam yace nagode in sha Allahu mummy bazan sakeba,
Allah yayarda mummy tafadi sadam yamike yayi mata sallama yatafi yana tunanin wannan sawa kai ijaba irinna mummy."
Advertisement
Sadam yakanyi kwana daya gidan wannan sannan yayi kwana daya gidan wancan ko sau daya bai taba hadasu waje dayaba,
Babu wacce tataba ganin wata acikinsu,
Sau daya yataba kaita ta gaida mummy basu samu tarban arzikiba kallon kirki basu isheta ba, har turmin zani tadauka a cikin na lefenta mai kyau da tsada da turare da man shafawa dasu sabulu takai mawa mummy su hassana da hussaina kuma yan kananun kaya ta deba musu, ko kallon arziki mummy batabi kayan dashiba, sawwama kuwa ko ajikinta bata dauki hakan a komaiba dan bai dameta ba, haka tatashi tayiwa mummy kaf aikin gidan komai da komai dake a weekend sukace, ba sannu babu madallah haka tagama aikin, harta da abinci ita tayi da mummy tashiga kitchen tabita ta karba sai tafice tabar mata kitchen din tayi tagama takai dining, tadawo ta zauna,
A sace mummy take kallonta ko zataga wata makusa a tattare da ita amma bata ganiba, gata karamar yarinya su hassana da hussainama zasu girmeta ko suzo sa'oi, aranta tana tunanin idan yartace bbu abunda zaisa tayi mata aure kamar haka,
Zuciyar mummy nason sauka akan taanar sawwama datakeyi saboda kyawawan halayanta datayi noticing amma mummy kyam haka tahana zuciyarta jin komai gameda ita, sai kara cusawa ranta takeyi cewa danta yaki bin umarninta akanta, ta mallake mata da aikuwa nan da nan taji wata sabuwar tsanarta tadawo cikin zuciyarta,
Koda zasu tafi mummy ta make adaki kin fitowa tayi suyi sallama sadam da kansa yashiga yace mata zasu tafi tace Allah raka taki gona, yafito yacewa sawwama su tafi amma fir haka taki tafiya wai saitayiwa mummy sallama, kofar dakin mummy yanuna mata taja yatsaya cikin ransa yana zullumin abunda zata taras, dankoda yakawota baiso barinta tawuniba alokacin yaso su tafi amma haka taki tafiya wai ita wuni zatayi haka yatafi yanata tunaninta, akai-akai yake dawowa gidan dubata, hakan kuwa ba karamin karawa mummmy haushin sawwama ba yayi aranta dan tasan dan ita yake wannan ziryan, shiyasa da zasu tafi taki fitowa,
A zaune bakin gado sawwama ta sameta tashiga da sallama mummy ta amsa ciki-ciki, har kasa ta tsugunna tacewa mummy, zamu tafi sai anjima, mummy kanta yana gefe tace mujima dakyau, sawwama ta mike tafita, mummy tabi bayanta da kallo,
Ita kanta acikin zuciyarta tasan sawwama tafi abida kirki, kyautatawar da sawwama tayi mata a yau kadai abida bata taba gwada makamancin hakaba."
Tafito tasamu sadam tace muje yaya sadam fuskarta yakebi da kallo ko zaiga wani yanayi amma sam baiga komaiba ajiyar zuciya yasauke yana tunanin ko mummy tafara saukowane toh? Dan yasan kyawawan halin sawwama dole idan ka zauna da ita kasota,"
Su hassana kuwa har mota suka rakata da murna kowannenssu a fuska ga dukkan alamu sun saba da ita adan zamansu na yau, suna cemata sai sunzo, itama da murmushi a fuskarta tace inajira sai kunzo."
Kwanansu sawwama biyu zuwa gidansu mummy tafara laulayi babu kama kafa gashi laulayin yazo mata da zafi,
Koda da yakaita asibiti aka auna 2month cikin dai-dai da lokacin aurensu, sadam bai bari kowa yaji labarin cikinba shine yake jinyarta akai-akai yake zuwa gidanta ranar dayake gidan idan yadawo a aiki baya motsawa ko ina,
Ganin idan baya gidan tana shan wahala yasanya ya dauko mata halima kanwarta dan sam bayaso tamotsa ko nan da can dan bakaramin soyayya yake nunawa cikin ba,"
Ana cikin wannan halin mummy tayi masa waya tanason ganinsa shida sawwama da abida duka suzo gobe, sadam baisan excuse din dazai bawa mummy amma sawwama kam sam batajin dadi yana ganin zaijene kawai batareda itaba."
Ih toh nace yauma dai banyi editing ba😀😀
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial36 Chapters
The Death God's Daily Troubles
"Starting from today, I'm gonna have a carefree life in the capital." Is what I'd like to say, but reality is cruel and the bills are even crueler. There are only two certain things in this world, death and taxes, and honestly, I'd rather die right now. Ugh. Welp, looks like I gotta get a job... And I just got out of prison too! Hmm, so what's the easiest job with the most freetime I could get that still pays well... Ah, I got it. I'll become a professor at the royal academy! Audiobook by Isekai Audio Tales: The Death God's Daily Troubles
8 105 - In Serial74 Chapters
Art of Mortality
New Synopsis after chapter 56: Long long ago, there was a mortal who despised the gods and envied the immortals. Why do the mortals have to die when the gods wish them to? Why do worlds have to perish when the gods say so? Why do only immortals get to live forever, why not mortals like him? As his family, friends, and his loved one died, he lamented. He wailed, he cried. He cursed the immortals, blasphemed the gods, spat at the heavens. But he was just a mere mortal. His curses were pointless, his blasphemous words were useless, and his spits only returned back to fall on his face. At last, he thought, enough was enough, he would definitely do something about it. He decided that it was time for the multiverse to know what a mortal can do. He was the first mortal to cultivate. Eventually, after a long struggle, he killed the Immortals, enslaved the Gods, and shattered the heavens. He reshaped the multiverse and rewrote his fate. In the end, he reincarnated as he decided upon a grand scheme, a scheme to rule 'All and Always'. He came up with the concept of what is known today as 'Paragon'. And with this, all of reality, 'All and Always', was finally reforming, according to a Mortal's Wish. Synopsis (Old): In the vast and complex multiverse, what can a mortal accomplish? In the grand scheme of things, what can a mortal change? In truth, what is a mortal, and what is mortality? Being mortal is being ordinary, the same as being trash, or so says The World. "No, mortality is an art, and a true mortal is a grand artist. Being the root of all, a mortal can become anything.", says a young mortal boy. Meet Edward Alexander, a mortal boy walking the path against gods and immortals, fighting to the end to rewrite his destiny, and change the grand scheme of things. Can he really change the grand scheme of things? Or maybe he himself is the Grand Schemer? To know the answer, follow Edward Alexnder on his journey to demonstrate the Art of Mortality.*******
8 162 - In Serial13 Chapters
Cosmic Spirits
(This is coming, I'm just trying to upload my little ideas of fiction, I didn't think of a short description yet)
8 133 - In Serial8 Chapters
When Machines Break
Leo Valdez. A man with a lot to say, but not many people willing to listen. Everyone on the Argo II know about his tendencies to forget eating or overworking himself. But clearly, there are some things they don't know. And when they find out, they'll do their best to help.
8 149 - In Serial21 Chapters
Mistakes (school 2015 fanfic)
Eunbi choose Han Yian over Gong Taekwang in the end. Han Yian makes her happy, comforted her, make her feel comfortable, and protected her, that's why she choose him. As time goes by, she realized that Han Yian is still in love with her sister. Gong Taekwang on the other side met his childhood friend, Kim Hajin, after a long time. Eunbi had a hard time with her sister abroad, she cannot understand her heart. Until she realize that, she's making a mistake.
8 239 - In Serial10 Chapters
My Love Made in the 90's
Di dalam buana yang belantara ini, pria dan wanita lebih menyayangkan untuk menjalani sebuah hubungan dengan seseorang yang usianya lebih dekat dari mereka.Meskipun, tidak sedikit juga di dunia ini yang memiliki pasangan yang berbeda usia terpaut jauh. Tentu saja akan mempengaruhi keduanya, bersamaan pola pikir yang jauh berlainan.Hal begitu wajar jika pria memilih wanita yang lebih muda darinya, karena memang sebuah hubungan ideal itu sudah sepatutnya sang laki-lakilah yang lebih tua.Inilah yang dialami seorang Bae Ga Eun yang tersemu 'kutukan' dirinya sendiri karena harus menjalani kisah cintanya oleh beberapa pria yang lebih belia darinya.Namun pada suatu hari, takdir mempertemukannya kepada seseorang yang begitu berlainan diantara laki-laki yang mencoba mendekatinya dan seluruh pria yang pernah ia jumpai.Bagaimana seorang Bae Ga Eun dapat melewati masa-masa yang di hadapinya?Ingin tau kelanjutan kisah ini?Look forward to the story, stay tuned eggies & everybody! 🥚❤️Cerita ini hanya fiktif belaka, jika ada kesamaan tokoh/tempat/kejadian/karakter/dsb itu sebuah kebetulan semata dan tidak ada unsur kesengajaan.Author menciptakan tulisan orisinil bersama khayalan sendiri. Dilarang keras untuk copy paste ataupun memplagiat karangan.Hargai sesuatu karya orang lain dalam bentuk pujian atau bahkan kritikan keras yang membangun, bukan menyalinnya 😊Terimakasih, aku cinta kalian readers! ❤️ [Author Fika]
8 93

