《ƘADDARAR RAYUWA》K page 48
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
"
Page 48
Zaman nabila a gidansu! mai makon ta samu kwanciyar hankali da nutsuwa kamar yanda take tunani saita samu akasin haka, domin kuwa sam zuciyarta takasa nutsuwa kullum tana cikin tunanin halin databar yarima ko cikekken bacci takasa yi,
Maimakon ta danyi kumari sai kara ramewa data keyi domin tunani dakuma tausayin yarima da kullum yake addabanta cikin zuciyarta,
Abaya tana ganin tana son dariya dayawa amma yanzu data rabu dashi na wani lokaci sannan tagane matukar kaunar tadake masa nabaya ba komai bane,
Duk da kasancewar ko kallon kirki bata samu wajan yarima koda tana waje shi baya zama a wajan amma hakan bai hanata sabawa dashiba kamar yanda hausawa sukace sabo tirken wawa, so sabo da kuma soyayya sun yiwa nabila dabaibayi,
Kwana biyu takara akai ko zata iya cire tunaninsa aranta amma hakan ya faskara maimakon ya ragu sai karuwa yakeyi,
Ita kanta ta tabbata zaman datakeyi a haka a gidansu cutar kanta da zuciyarta takeyi domin sam takasa samun nutsuwa, lokacin tana tareda yarima gani takeyi kamar rayuwarta tana cikin kurkuku, yanzu kuma data rabu dashi sai ta sanya zuciyarta da tunaninta cikin kurkuku,
Addu'a ta dage sosai dayi tasan idan zama da yarima ba alkhairi bane Allah zai canza mata da mafi alkhairi, cikin kwana biyu babu wani takamammen canji a abunda takeji, hakan yasa ta yankewa kanta da zuciyarta shawara dukda kuwa wani gurbi na jikinta da zuciyarta basason wannan hukunci data yanke,
Da yamma likis tasamu mahaifiyarta tana zaune palourn mahaifinsu ta sanya masu aiki su gyaggyara mata ko'ina saboda dawowar mahaifinsu nabila,
Nabila tashiga tazauna cikin nutsuwa, mahaifiyarta ta dubeta cikin tausayawa domin duk tabi ta canja tadawo gida maimakon tasamu sukuni amma sai dada ramewa takeyi,
Kasa nabila tayi dakanta takasa cewa komai domin maganar tayi mata nauyi a baki, mahaifiyarta ta zura mata idanuwa kawai batace komaiba,
Dakyar nabila ta iya bude baki tace mama inason komawa gidan mijinane, dasauri mahaifiyarta ta kalleta tace banganeba wani abun akai miki anan din? Girgiza kai nabila tayi tace babu abunda akayi min kawai dai inason komawane,
Advertisement
Jijjiga kai mahaifiyarta tayi tace babban lamari toh naga keda kanki kikazo kikace kin gaji da zama?
Nabila ta jijjiga kanta tace eh amma yanzu inason komawa saboda koda ina zaune anan dinma hankalina yaki kwanciya hankalina gabaki daya yanacan, ina kwana da tashi da tunanin halinda yake ciki kullum, dama nadawone koda zan samu sukuni amma bansamuba saima abunda yakaru na rashin samun nutsuwar zuciya gara nakoma din kawai ko babu komai nasan ibada nakeyi kuma zan samu lada,
Mahaifiyarta ta jijjiga kai tace ina tausaya mikj sosai saboda halinda kika shiga amma har in dai hakan ne zabin zuciyarki a yanzu bazan hanaki tafiya ba saboda bani nakawo kiba kamar yanda kikazo da kanki kika nemi komawa da kanki bazance komaiba sai Allah yakawo miki sauki cikin lamuranki yabaki ladan ibadan da kikeyi,
Amin thumma amin nabila ta amsa mahaifiyarta tace amma zaki dakata zuwa gobe kafinnan koda mahaifinki bai dawoba nida kaina zan sanya akaiki,
Gyada kai nabila tayi tace nagode mahaifiyarta tace babu komai, Allah ya kawo miki dauki yabashi lpy nabila ta amsa da amin,
Ta mike tatafi mahaifiyarta tabita da kallon tausayawa,
Washe gari mahaifinta bai dawoba dan haka ta sanya aka kai nabila, nabila tasamu kanta da mummunan faduwar gaba a yayinsa takoma gidan, wajan mai martaba tafara isha tabashi hakuri mai martaba yace babu komai na fahimci halinda kike ciki kokadan banji wani abuba Allah yabawa mijinki lpy, kanta kasa ta amsa da amin,
Har umma ma tayi murna da dawowar nabila umma tadanyi mata nasiha hadeda godiya sannan suka maidata sashinta." Wannan kenan!
—————
Kwanan sawwama biyu gidan sadam amman ko sau daya bai taba yimata zancen uwargidansa ba koda kaita wajan uwargidan bai taba yiba balle su gaisa,
Tanason ta tambayeshi amma bataso yaga kamar tanason sany masa ido a rayuwar gidansa kokuma shige masa rayuwar gida,
Dalilin daya hanata tambaya kenan,
Yakan fita lokaci zuwa lokaci sannan taji dawowarsa,
Sai dai idan yafita baya dadewa yake dawowa,
Abida na zaune tacika tayi dam jin zuciyarta takeyi kamar tafashe sakamakon cin karo datayi da video din sadama na ranar da aka kai masa amarya a instagram, ita iya tsawon rayuwarta bata taba kallon angonda ya nuna zumudi akan amaryarsa ba haka kaman sadam, iya zamanta dashi bai taba nuna son wani abuba haka kamar yanda ya nuna akan amaryarsa ba,
Advertisement
Hawayen bakin ciki taji yana zirara akan kumatunta, fuuu tayi daki tadauko gyalenta tadawo tafice tadauki mota tafice a gidan gabaki daya,
Mummy takaiwa video din tagami ai mummy har tafi abida bakin cikin ganin video dinnan har wani huci take zuciyarta zafi take a zafafe tafara neman layin sadam amma mene? Layinsa a kashe diff,
Mummy tadubi abida tace wayarshi a kashe datsu yazo ya gaidani ya koma wallhy danaga video dinnan tun datsu dana ci masa uwa dan iskan yaro, oh yau ni naga ja'iba anya wannan yarinya ba asirceshi tayiba? Sadam nacikin hankalinsa kuwa yake wannan abun?
Anya bai fara tabuwa ba? Abida tace kema dai kya fadi mummy wallhy yanzu ni banma isheshi kalloba yana shigowa gidannan zaiyi wuff yafice ban sake sanyashi a idona,
Mummy tace ih yoh toh ba wannan kanwar ubannasa azabebbiya masifaffiya ta daure masa gindiba? Iyi ai dole yayi abunda ransa yakeso, ai naso akai miki yarinyarnan gidan da kike kici ubanta dakyau, amma ni zaizo ya sameni ina dai-dai dasu gabaki daya,
Abida tace ai mummy ni bansan me yasama aka fasa kawota gidana ba wallhy harda anyi jere aka fasa,
Mummy tace nima ina nasani basa kasani a cikin abunsu shida dadynsu da kanwar ubansa suke shirya komai, daba kin sanar dani ba'a kawota gidan canba aini bazan saniba,
Abida tace mummy dan Allah kiyi wani abu idan ba hakaba muna kallo yarinyarnan zata juyashi yanda ranta yakeso, mummy tace eh ai munanan dake zakiga mai zanyi, tunda nabawa sadam umarni yakibi akan yarinyarnan yasa naji duk na tsaneta duniya banga wanda na tsana fiyeda itaba, abida tayta zuga mummy, mummy tayita zurmawa🙄
Shikam sadam baisan wainar da ake tayawaba wayarshi tana kashe yana can yana shan soyayyarsa da sawwama,
Washe gari kuwa dayazo gaida mummy yasha bala'i kamar zata dakeshi tayita tsinewa sawwama shidai hakuri kawai yake bata,
Bayan tagama yace mata zaiyi tafiya kwana 2 an turashi wani aiki,
Mummy tadan sauka tace yawwa Allah yabada sa'a nace bada wannan yarinya zaka tafi ba? Jijjiga kai sadam yayi saurin yi yace eh mummy aikine ai bazai yiwu natafi da itaba,
Sai lokacin tadan sake ranta tace yawwa sai akula da akwai halima daka tafi da abida,
Sadam ya rusunar dakai yace mummy nima da zanzo hakan saboda ko zata tayani da wnai aiki amma kuma bazai yiwuba,
Mummy tace toh shikenan Allah ya taimaka sadam ya amsa da amin."
Mummy dataji bazai tafi da sawwama ba sai hankalinta yadan kwanta ko babu komai zasu rabu na kwanaki, zata bar mata yaro yadan sarara,
Nikuwa nace anya mummy ba kishi take da sawwama ba? Ba irin iyaye masu kishi da matan yayansu bane?
Sadam yana komawa gida yacewa sawwama tahada kayanta zasuyi tafiya, da mamaki take kallonsa dan batasanda zancen tafiya ba, amma batayi masa gardama ba ta hada kayanta kadan tasaka yazo da kansa yakara dayawa, yace zai fita kafin tadawo tagama shiryawa, zuwa yayi nanma ya shirga abida itama harda murnarta zai tafi at least dai zataji dadi bai tafida kowacce ba a cikinsu, aadam ya gargadi sawwama akan ko family dinta kada ta sanar dasu zancen tafiyarda zasuyi, suna gama shiryawa suka kama hanya sai YANKARI antafi honeymoon🥰."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
💞
Advertisement
- In Serial8 Chapters
The last tales of Arun-Val
In a world where magic is fading, the valley of Arun is one of the last corners where ancient powers still exist. Without wanting to, our protagonists will be involved in different adventures that threaten the survival of magic itself. For the reader The last tales of Arun are four self-concluding short stories of YA high fantasy, based on the mythology of the Pyrenees mountains, Europe. There is no strong language and no sexual content. Violence is mild. Each story is around 8k words, and they will be split into two parts each.
8 174 - In Serial76 Chapters
An ordinary novel but every 10,000 words the audience kills the least interesting character
Season 2 (A straightforward adventure but the audience keeps killing the least interesting hero, ongoing): Six orphans must race across a ruined fantasy world to kill the Locust Queen before YOU vote them dead. Season 1 (An ordinary novel but every 10,000 words the audience kills the least interesting character, complete): That’s right, dear reader. The lives of nine people are now in your hands. They’ve woken up at the top of a tower in the clouds with only one directive: BE INTERESTING, OR DIE.
8 260 - In Serial55 Chapters
Dangerous Love
|Book 1 in Dangerous Mafia Series| Please read this first|A girl who has secrets and thoughts darker than most. A boy who will be the leader of the most powerful Mafia in the world. A past of heartbreak and pain. Brooklyn Lilac Russo grew up learning how two kill a man in hundreds of ways. She never feared death she embraced it. She knows more languages than you can count on your hands. Killing people has never been a problem. But falling in love? That is something she tried but did not work out. Now, will she be able to find love with a man who rivals herself in death and destruction?Mason Enzo Morelli grew up knowing what his role is in the world. Be the greatest Mafia empire known in every town and city. He built his own gang at 14 and at 21 he has to prepare to take over his family's empire built on fear and death. But a young woman who is blessed with the beauty of the gods but rivals the devil comes into his life and messes up his plans. Can they fall for each other while Brooke's past catches up to her? or will the past take the one thing, Mason loves more than life itself?
8 207 - In Serial16 Chapters
A Journey of Chaos and Glory
Chunks of stone forming an armor of earth, blazing orbs of compact fire, riding the wind, tendrils of pure darkness. These are just a few common sights in Jeru's world. Everyone can harness the power of an element to enhance themselves. Jeru however is different. At the age of 12 he is still unable to manipulate nature, this marks him as a simpleton. Jeru's life is further mired in chaos as his Father disappears during a fight with a powerful creature , an Outworlder, a being from another world. Now Jeru must overcome his handicap and become strong if he wishes to find answers to who he is or where his Father has gone.
8 103 - In Serial26 Chapters
Midnight: Dark Horizon
Two hundred fifty years ago, a meteor landed on the war-filled land of Nuria. Shards landed everywhere contaminating the fauna over time and awakening creatures. Now in the present time, something dark is rising up and it's up to a group of five to avenge what has been taken from them and stop the seeds of darkness from blooming. Map of Nuria
8 120 - In Serial235 Chapters
Warrior of Fang
In the darkest times when the world was in ruin, a chosen one gifted with the light to vanquish the darkness is born. A never ending battle with the eternal dragon is fought throughout time, through generation after generation, guided by the talismans of old, an ancient awakening and a forgotten goddess. Alex Fang, a young Feles warrior, the new generation against the darkness has yet to discover his true family linage against the darkness, but it has already set its plans into motion to stop the light from winning His struggles shortly started after he receives his talisman passed down through his family at his sixth birthday, coming in contact with Dumah who carries a dark essence which corrupts those week to its influence. This dark influence slowly changes the kind-hearted king, creating conflict within the lands of Panthera, the darkness seeping into the land. Alex works hard to grow in rank to protect the one who he would give everything to protect from this darkness - princess Tigra. When his true awakening happens, he discovers the world seeped in a deeper darkness than he could have ever imagined, but will he succeed in vanquishing the darkness from his home.
8 105

