《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 38
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 38
Har shi kansa sadam ido ya zuba mata yaji wani sharaɗine wannan a ransa yana faɗin ita dai mummy bata rasa hanyar bijirowa,
Mummy taci gabada faɗin zan barka kayi aure amma sai dai ka auri abida ƴar gidan yaya, gaban sadam yayi wani dam wai me mummy take nufi dashine haka? Aurenma bazata barshi y aauri wacce yakeso ba sai an haɗashi da wata shi bai kai ya zaɓi macenda yakeso ba kennan? Shi abidanma bai wani sandata ba koda ya santa sam bata burgeshi a ya aureta ba, sun kuyarda kansa yayi kasa yakasa cewa komai,
Dady ya miƙe ya kallo mummy yace biyoni ɗakina muyi magana, yawuce ɗaki mummy tabi bayansa,
Dady yace ke wai meyake damunki ne? Ikonki yayimun yawa akan yaronnan kinsan nafiki iko dashi koh' amma ke kinfi nuna iko akansa nabarki saboda ke mhaifiya, nabaki damarki na mahaifiya akan neman aurensa amma kin zubda damarki wayace miki kinada hurimin zaɓa masa mata? Toh bari kiji sadam yanada wacce yakeso kuma gobennan zanje nema masa auranta da kiso dakuma karkiso kina jina koh? Shi namiji ana yimasa auren dole ne? Ni ko mace a ƴaƴana bazan yiwa auren dole ba, bare sadam wanda ke kanki kin sani naƙi ɓacin ransa,
Mummy tace amma dadyn sadam bawai kai tsaye na zaɓa masa aurenba, tun shekarun baya da suka wuce yaya yayimin magana akan yanason haɗa auren sadam da abida lokacin sadam yana karatu shiyasa nace ya dakata tukunna, idan yagama karatu zamuyi magana, kuma ko jiya dana tura masa result ɗin sadam sanda ya sake maganar, kuma ya shaidamun bazai bawa yarsa akowaba idan bashi sadam ɗinba,
Kallonta yakeyi harta gama magana sannan dady yace kin sanda haka tsawon lokaci baki sanar dani ba sai yanzu?
Mummy tace alokacin ina tsoron kada kace zaka yimasa aurene, saboda nasan yanda kake ɗaukan yaya da muhimmanci, tsaki dady yaja yace nikam yanzu basan abunda zanyiba, idan naƙi auren alhaji zai ɗaukeni da wata manufa sannan kuma abunda nakeso kisani shine auren sadam da wancan yarinyar babu fashi idan kikaga ba'ayiba sadam ko iyayenta sukace basuso,
Advertisement
Toh yanzu yaya zanyi da yaya? Mummy ta tambaya, dady yace ki sanar dashi kiji mai zaice,
Mummy ta ɗauki waya ta kira yaya jiki bbu kwari ta sanar dashi abunda ake ciki, amma da mamakinta bai wani damuba yace toh shikenan sai in sama masa aaiki sai y aauresu duka biyu, dan ita kanta abidan ta shaidamin irin sonda takeyi masa idanba shiba bazatayi aureba har nayi mamaki domin bansan yanda har suka saba hakaba, toh kinga shima baza'a tauye masa hakkinsa ba sai ya auresu duka biyun ni wajena ba komai bane ita kanta abida nasan bazata ƙiba ai,
Ita dai mummy jiki babu karfi har sukayi sallama mace ɗayama da yaya akayi ta yarda zai aura bare biyu?
Dady yana kallonta batareda yace komai ba, cikin damuwa mummy tace yanzu yaya za'ayi? dadyn sadam kajifa abunda yace, Dady yace gashi ya faɗa miki yanda za'ayi kuwa aurensu su duka biyun zaiyi, mummy tace amma yaushe sadam zai iya riƙe mata biyu?
Dady yace toh shikenan sai ita abida ɗin ta hakura, da sauri mummy tace A'a yaya za'ayi haka? Itacefa ƴar uwarsa, dady yace nasan baki buƙatar ƙarin bayani akan abunda na faɗa miki ɗazu koh?
Jikin mummy yayi sanyi dady yace kiyi addu'a shi sadam ɗinma ya amince mana tukunna,
Mummy tace amma dadyn sadam nawa sadam ɗin yake da za'ace zai auri mata biyu? Aduba lamarinnan itafa abidan shekaran baya fa akayi maganarta wannan ɗin da sai ahaƙura da ita,
Dady yace itama wannan shekarunsu nawa? Ai ba yanzu yace yafara nemanta ba, dady ya bata amsa sannna yace tashi ki Kirawom shi naji ta bakinsa tun kafin na canja ra'ayi, mummy ranta baiso ba tatashi takirawo sadam ɗin, dady yayiwa sadam bayanin komai, sadam yace dady ni fa banna wani santa ba yaya za'ace na aureta kuma mata biyu?
Dady idamma na santa wannan tayi sa'anafa,
Nisawa dady yayi yace sadam nasan wannan zance zaiyi maka nauyin ɗauka amma inaso kasani mummynka zta iya ɓullowa da wata hanya idan baka amince ba garaka amince kawai yafi, kayi addu'a kawai Allah ya sanya alkhairi, sadam yace shikenan Allah yasa hakan shi yafi alhairi,
Advertisement
Dady ya amsa da amin sannan yace zaka iya tafiya amma ka sanar musu da zuwanmu gobe kada muje batareda mun sanar ba toh sadam y amsa sannan ya fita,
Aranar suna waya da sawwama ya sanarda ita zuwan magabatans- aamma bai yarda ya faɗa mata cewa su biyu zai aura ba."
Washe gari su dady da abokansa suka shirya suka tafi nemawa sadam auren sawwama, gidan mahaifin baba sukaje wato malam sa'adu, baba yayi musu bayanin cewa mata biyu zai aura, sam bbu wanda ya nuna rashin jin dadinsa a zancen saima faɗi da sukayi Allah yasa hakan shine mafi alkahiri, sawwama tayi sa'ar gidan arziki,
Alokacin su dady suka bada sadaki 200k da goro da minti na tambaya, aka tsaida lokacin biki idan tayi waec dan watanni ya rage mata, dady ya bada 200k ne kawai saboda su sayawa ɗiyarsu abun buƙata dashi saboda ya lura basuda komai sai rufin asiri, shine ya bada 200k matsayin sadaki, haka sukayi zamansu cikkn mutumci suka ƙare, yayinda suka rabu suna yabon halin kirkin juna,
Ita kuwa mama taji rashin ɗadi sosai cewa wai su biyu sadam zai aura dan tayita faɗa har take cewa baba da an fasa aiba kai sukeyi da ɗiyarsu ba da za'a bada aurenta su biyu, jijji ga kai baba yayi sai yanzu yake ƙara tabbatarwa da mata ba kasafai suka cika hangen nesa ba, sannan kuma ai idan akayi la'akari sadam ya rufa musu asirine ya rufawa sawwama asiri amma ita mama bata fahimci hakanba,
Ita kanta sawwama jin zancen su biyu zai aura baiyi mata daɗi ba, amma kuma hakan bazaisa taji tana son fasa aurensa ba."
Washe gari suka je gidansu abida abokin dady ne yabada 100k sadaki yayinda sukayi duk wani abunda ya kamata aka sanya biki wata ɗaya mai zuwa,
Sakonda ya isa sadam ji yayi kamar yayi kuka tayaya za'ace ya fara auran abida bayan ga wacce yakeso, ji yayi kamar ya samu dady ya ce masa kawai ahaɗa dana sawwama idan yaso sai tayi exam ɗin a gidansa,
Duk wannna abunda akeyi mummy bata san cewa sadam ƴar talakawa zai aura maka karancin karatun boko ba, saboda yanzu duk ta ta'allaƙa hankalinta ta maida akan auransa da abida, idanba tuna mata akayiba takan manta cewa mata biyu zai aura."
* FITATTU BIYAR NA KUD'INE.*
*FEEDOHM - SILAR WAYE?*
*ZAINAB BAWA- YARIMA FAYAD.*
*ZEE YABOUR - DR MUHRIX.*
*HAJJA CE - ANNURIN ZUCIYA.*
*NANA DISO - GIMBIYA SUHAYMA.*
LITTAFI BIYAR AKAN___500,
IDAN HUDU KIKE SO___450,
IDAN KUMA UKU NE___400,
IDAN BIYU KIKE SO___350,
IDAN KUMA D'AYA KIKE SO 200.!
TURA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT D'IN.
3126584401 FIDDAUSI MUSA FIRST BANK TARE DA SHAIDAR BIYA A 08036953516
KO KUMA.
ACCOUNT NUMBER:- 0003075326 ZAINAB M BAWA
Jaiz bank SHAIDAR BIYA TA 08161146563.
*KO KATIN MTN TA WANNAN LAMBAR 07065283730 TARE DA SHAIDAR BIYA.*
*SANNAN MUYI ADDING D'INKI A FITATTU GROUP🌹...*
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial76 Chapters
Dreams of Sabers and Spirits
With all his alternatives cut down and facing the disdain of his family, Aiden goes in a travel in search for a method to recover his lost spirit. Accompanied by a mysterious saber and a beautiful maid, look how Aiden gives his best to fight against his fate and reach someday to the peak of the world. ______________________________________________________________ English is not my native tongue, so I hope you can correct any mistake you find.
8 181 - In Serial21 Chapters
Madness with a touch of sanity
A story from the point of view of madman, although they seem perfectly sane, the world will burn around them and only they will remain, and maybe some others too. This is one of my first published stories, hate it if you want, I probably will, but any advice will always be appreciated, if I can improve my writing I will be happy. Cover is temporary, royalty-free image, until I either create or commision someone to create a new one
8 195 - In Serial12 Chapters
Sylvaria Online Book 1: Split
A married couple who love gaming soon find their reality shaken when their family is drawn into a game; Sylvaria. Relationships are tested when they discover this game isn't like other games. Death is final and the only thing keeping them alive is their wit and willingness to trust one another through anything this new reality has to throw at them.
8 166 - In Serial6 Chapters
The Gate of Wills
Crow and thousands of other gamers are drawn into a new world where more is at stake than what they can imagine. Of course, he is happily unaware of the dangers that lurk around him and is mostly just peeved over why he can't choose an avatar or log out of this new mmorpg. He is about to have a rude awakening.
8 88 - In Serial15 Chapters
UnKnown
One hated for having a villains quirk other loved for having a hero's quirk, both unknown to the people around them, only having each other until one day they broke.
8 80 - In Serial11 Chapters
Steel fangs
Screw the legendary sword whats so good about that only one person can wield a sword at a time. human are born without fangs, claws, or scales. So we made our own of steel. and we called them swords, daggers, and armor. Myka's parents died saving people yet never known as heros But everyone bowed for the summoned heros who did nothing but be blessed with power. The man has a dream to destroy the legendary sword and make his people stand on their own two feet.instead of false heroes
8 139

