《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 35
Advertisement
*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 35
Sawwama kwana biyu tana son ganin sadam amma babu yanda ta iya haka ta haƙura batareda ta nuna masa tanason ganinsa ba saboda tasan idan shi yana son ganinta tasan tabbas zaizo,
Haka baba ya lurada yanda sadam ya ɗauke ƙafarsa a gidan amma bai sanya abun a ransa ba balle yadameshi, suna zaune baba ya kira sawwama bayan tazo baba yake tambayarta ko sadam yana zuwa kwana biyu, baya zuwa sawaama tabashi amsa,
Jijjiga kai baba yayi yace toh shikenan bamusan mai yake nufi ba amma Allah ya zaɓarda mafi alkhairi, cikin rashin fahimta sawwama ta kalli baba sai kuma ta sunkuyarda kanta, mama tace badai tunda kukayi maganarba shine bai dawoba, baba yace eh shine amma bamusan mai yake nufiba zai iya kasancewa wani abun ya tsarrmeshi mai muhummanci dan haka zamu jira na wani lokaci mu gani, shiyasa banyi gaggawar bawa yaya zakari amsa ba saboda gudun hakan, gaban sawwama sai faɗuwa yakeyi dan haka tatashi ta wuce ɗaki, tana shiga taji wani gumi yana tsattsafo mata wani zance baba sukayi da sadam kenan har ya sanyashi ya daina zuwa wajanta? gabanta yaci gabada faɗuwa ga zancensa da yayi na cewa shiyasa bai bawa yaya zakari amsaba, mai hakan take nufi kenan? Menene haɗin ya neman auranta da sadam da yaya zakari kuma?
Tambayiyine dayawa fall cikin ranta amma batada wanda zai bata amsa dan haka ta yanke shawarar idan sunyi waya da sadam zata tambayeshi."
cikin sanyin jiki sadam yace dady nagode yana faɗin haka ya tashi ya fita dady ya bishi da kallon tausayi cikin ransa yana kissima abubuwa dayawa,
A ƙofar ɗakin mummy sadam ya tsaya yace mummy dady yana kiranki, da wani kallo ta bishi ganin yanda jikinsa yayi sanyi sai tace me kuma kacewa dadynka nayi?
Baby kawai yana son magana dake ne, miƙewa tayi tana masa kallon tuhuma ta yi ɗakin dady shikuma sadam ya wuce nasa ɗakin yayinda gabansa yake tsananta faɗuwa saboda yana taraddadin yanda zata kaya tsakanin dady da mummy yasan bawani da daɗi zata kaya musu ba,
Advertisement
Mummy zaune gaban dady tayi shiru kawai tana jira taji yafara magana,
Gyaran murya dady yayi sannan yace mummyn sadam dama magana nakeso muyi dake gameda abunda sadam yanzu yazo ya sameni akai,
Kafin na faɗa miki zancen inaso ki yiwa zancen kyakkyawan fahimta ki sanyashi a ma'auni ki auna zancen a matsayinki ke kanki matsayinki ma mahaifiya, inaso idan kika tashi yanke hukunci ki cire son zuciya aciki kiyi masa adalci iya yanda zai iya dauka,
Ni ban tilasta miki ba amma inaso kisani sadam dai ɗanki ne kuma Allah zai tambayeki idan kika musgunawa rayuwarsa duk da kasancewarki matsayin mahaifiyarsa,
Cikin ƙaguwa mummy tace dadyn sadam nikam ka faɗamim mai yake faruwa,
.Dady yace toh shi dai sadam yazo ya sameni da magana man cewa shi aure yakeso,
Zaro ido mummy tayi tace aure? Koba aureba? Shi sadam ɗin yafaɗi haka? nawa yake? Shi yaushe aka haifeshi da har zai fara maganar aure? Yaushema yafara karatu tukunna da zaiyi zancen aure?
Wallhy ban yardaba ban amince sadam yayi auren ba bada yawuna ba kwata-kwata nawa sadam ɗinyake? har yaushe aka haifeshi da zaiyi magaanr aure? wani mataki yakai a karatu? Yaushe ma yafara karatun da zai bijiromin da maganar aure? Idan wannan maganar nema gaskiya ni kada ka matsani saina amince dan banjin zan iya amincewa,
Jijjiga kai dady yayi yace ni ni bance can takuraki dole sai kin amince ba ai ɗanki nefa kinada hakki akansa, nidai abunda nakeso kisani har in dai yaro zai fito ya dubi iyayensa yace ayi masa aure to zancen abun dubawa ne lallai idan anason a zauna lafiya, saboda yafaɗi hakanne dan gudun faɗawa halaka, idan kuma anƙi to yaro zai iya faɗawa wani hali alokacin ɓarna zata yaɗu, sannan kuma kafin asamu hanyarda zata ɗinke wannan ɓaraka sai anyi da gaske, kuma har in dai ya faɗa halaka bashi kaɗai keda laifi ba mu kansa mahaifansa akwai namu gudumawar, sannan Allah zai tambayemu, wallhy ko sau ɗaya banason Allah ya tambayeni akan nakasa bawa yarana tarbiyarda tadace kokuma wani gazawa akan yarana, to ke idan kika hanashi aure meye ribarki?
Advertisement
Mu ba abun muyi murna Allah yabamu yaro mai sanin ciwon kansa ba, maimakon yafaɗa halaka sai yazo yafaɗa mana gaskiya, wallhy ban taɓa sanin hankalin sadam yakai haka ba sai yanzu, yarone mai tsoron Allah da hankalin gaske, sai yanzu nagane zan iya barinsa yaje bangon duniya banda damuwa,
Sannan karatu ai koda aure ana karatu, ni ina age ɗin sadam na aureki ban riƙeki ba? ban kula dake ba? Alokacinda naci gabada karatu mun haifi sadam, haihuwarsa ta hanani karatu bare aurenki?"
Dadyn sadam bazafa ka haɗa yanzu ta da ba shekaru nawa baya, yanzu lokaci ya canja, jijjiga kai dady yayi yace hakane lokaci ya canja babu komai taji kije,
Miƙewa tayi ta fice tabar dady da ɗumbin mamaki baiyi zaton cewa abun mummy har yakai hakaba, amma wannan abun mumny akan karatu kaɗai take yinsa? Kokuma tana ɗaya daga cikin mata masu kishin araɓi ƴaƴansu saboda kar yayi aure kulawarda yake basu ta koma man matarsa ne oho?
Kai tsaye ɗakin sadam mummy tawuce atsaye ta tsaya ta bishi da wani irin kallo sannan tace ka kyauta kaji daɗi ka ɓatamin rai tana faɗin haka ta juya tayi waje sadam ya bita da kallo kawai iska ya furzar ya kwanta bai daɗe da kwantawa ba wayarshi tafara ruri, yana dubawa yaga sawwama wani irin daɗi yaji a cikin ransa, sawwama kuwa anata wajan tarasa sukuni hakan yasa akaro na farko ta ɗaga waya ta kirashi,
Picking yayi ya kara a kunnensa, cikin nutsuwa sawwama tayi sallama lumshe ido yayi ya buɗe saannan yaji wani sanyi cikin ransa,
.Bayan sun gaisa sawwama ta tambayeshi mai suka tattauna da baba bai ɓoye mata ba ya shaida mata har yanda sukayi da dadynsa ya shaida mata sai dai yaɗan ɓoye wasu abun saboda baison tashin hankalinta, baiyi mata bayani yanda hankalinta zai tashi ba,
Wayarda sukayi da sawwama ita ta kwantar masa da hankali yaji kamar bai cikin wata damuwa ma gabaki ɗaya."
Mummy ta ɗauki abun da zafi sosai dan 2days sadam yana gaidata ko amsawa batayi hakan yasa ya shiga damuwa sosai,
Ranar ya yanke shawarar ya sameta a ɗaki ya bata hakuri sannan yaji opinion ɗinta tunda shi daga dady har mummy bbu wanda yace masa ga abunda suka tattauna akai,
Da sallama ya shiga ɗakinta, a ciki-ciki mummy ta amsa sallamr ta kauda kanta gefe, ƙarasawa yayi ya zauna agabanta ya tankwashe kafafu, yace mummy ina wuni?."
* FITATTU BIYAR NA KUD'INE.*
*FEEDOHM - SILAR WAYE?*
*ZAINAB BAWA- YARIMA FAYAD.*
*ZEE YABOUR - DR MUHRIX.*
*HAJJA CE - ANNURIN ZUCIYA.*
*NANA DISO - GIMBIYA SUHAYMA.*
LITTAFI BIYAR AKAN___500,
IDAN HUDU KIKE SO___450,
IDAN KUMA UKU NE___400,
IDAN BIYU KIKE SO___350,
IDAN KUMA D'AYA KIKE SO 200.!
TURA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT D'IN.
3126584401 FIDDAUSI MUSA FIRST BANK TARE DA SHAIDAR BIYA A 08036953516
KO KUMA.
ACCOUNT NUMBER:- 0003075326 ZAINAB M BAWA
Jaiz bank SHAIDAR BIYA TA 08161146563.
*KO KATIN MTN TA WANNAN LAMBAR 07065283730 TARE DA SHAIDAR BIYA.*
*SANNAN MUYI ADDING D'INKI A FITATTU GROUP🌹...*
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial36 Chapters
An Unwavering Craftsman
Given the hereditary nature of classes, everyone expects Damien—the child of two high-tiered adventurers—to be granted a high-tier combat class of his own. Expectations are betrayed, however, when Damien finds himself instead saddled with a crafting class of the lowest possible tier: [Neophyte Tailor]. Left practically crippled compared to those with better classes, Damien wants to avoid becoming a pawn in the machinations of the nobility, desiring only to grind his level in peace while wondering why the usual rules of inheritance were broken. Was it his desire to excel by his own effort, rather than an unearned blessing from a god? Did the Five take offence at his opinions on the unfairness of hereditary classes? Or maybe it was something to do with the alien voice that intruded on his ceremony? A voice that offers great power, and freedom from the tyranny of the Five, but that never names its price. This story is litRPG-lite. While the class someone possesses controls most of their lives, people don't get dinged at for every level they gain, nor can they see their status without undergoing a special ritual. The MC has no romantic interest. Crafting is merely a way to game the system, and doesn't feature heavily in the story, aside from a few descriptions on how they're carrying out the system abuse. There is, on one unfortunate occasion, maths. The pace is quick. This was a participant in the Spring 2022 writathon. (i.e. it was posted as-written at high speed. I may give it another editing pass in the future.)
8 186 - In Serial10 Chapters
Humanity Extinguished
I had the same nightmare again. The loss of my first life continues to haunt me, but now it aches like an old wound. A more grievous injury to my psyche was the losses yet to come and the inevitable hellscape I would return to again and again. Reincarnation is my curse. The lives themselves weren't all that bad. Losing people you cared about hurt and all, but even that pain was preferable to experiencing the nothingness between lives for months at a time. It was enough to drive anyone mad. Now I have to focus on breaking this horrible cycle. Thankfully I have all the time in the world. Trace is an average man driven by extraordinary circumstances in an indifferent and cruel world. His reincarnations give him a few key advantages but also take a heavy toll on him. He lives in a world where magic is uncommon and underpowered compared to the limitless physical adaptations you can acquire by getting your hands a little bloody. This story is one of hardship and terrible lows, but also monumental achievements and grand heights. The main character has flaws. While some of these flaws will fade with time, others will worsen. Thank you for taking the time to read my synopsis. I plan to release 2-3 chapters a week. Cover art is 'The Siege and Destruction of Jerusalem by the Romans Under the Command of Titus, A.D. 70' by David Roberts.This art is in the public domain.
8 141 - In Serial6 Chapters
A royal family and a caring thief(Spikedash)COMPLETED
hey guys Spike_Dash here this is an mlp fanfic i made beacause im bored and this has slow updates hope you like it.they ae humans in he storyspike-15twilight-19rainbow-16pinkie-16sunset-17fluttershy-18applejack-17rarity-19scootaloo-11sweetie belle-11applebloom-11etc.sorry for the spelling and the grammarchaoi do not own mlp characters nor the songs
8 121 - In Serial4 Chapters
D&B + Golden Apple ¦ Oneshots!
This is my first oneshot book i hope you guys like this
8 74 - In Serial20 Chapters
fuck you
It's really a "enemy's" to lovers type of thing. I will most likely make it a slow burn because getting into things really fast just annoys me so much. This is a fanfic about ashtray from euphoria. He's not gonna be a 12 year old in this. You and him are 16. And i will try to put out as much chapters as i can at once.(now looking back at it they're not really enemy's but it's ok)
8 147 - In Serial24 Chapters
I miss you Pucca || Garu's story
Pucca had to leave Sooga Village. At first Garu enjoyed it but soon he began to miss the chases, hugs and kisses he received everyday. This story is mainly in Garu's perspective. please don't hate me for this ;-;
8 266

