《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 34
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 34
Washe gari dady ya fita da wuri dan haka sadam bai samu yayi magana dashi ba, wunin ranar haka sadam yayi shi jikinsa gabaƙi ɗaya babu ƙwari, har mummy sands ta afahimci hakan amma bata tanka masaba saboda tace duk ranarda abunda yake damunsa yayi tsamari taji tunda har yaƙi faɗa mata abun bai dameshi bane, daga ƙarshe wunin ranar a gidansu najeen yayi shi najeeb yaci gabada bashi shawarwari yanda zai ɓullowa al'amarin da yanda zaiyiwa dady magana ya ɗauki maganarsa da muhummanci sai dare yadawo yana son ganin sawwama amma bai samu yajeba, saboda yafiso har sai randa yayiwa dady magana dady ya amince tukunna zaije wajanta da gwarin guiwa, sadam bai samu ya zauna da mahaifinsa yayi masa magana dashiba saboda da wuri yake fita aiki sannan kuma yadawo da dare, dan haka ya yanke shawarar cewa zai bari a weekend ya sameshi d azancen, sannan kuma har wannan lokacin bai ƙara komawa wajen sawwama ba amma kullum suna waya akai-akai duk yanda yakeson ganinta haka ya haƙura,
Ranar friday haka ya wuni da faɗuwar gaba saboda washe gari yake sanya ran yiwa dady magana saboda ya gaji da wuni da kwana da taraddadi cikin ransa,
Bacci kaɗan sadam yayi aranar gani yakeyi kamar safiya bazata yiba saboda yanda ya ƙagu yayiwa mahaifinsa magana, tunda yaji wani daga cikin ƴan uwan baba sun fito neman aurenta ya gigita da zullumi take kwana aransa, zuciyarsa bazata iya jure rashin sawwama ba,
sai bayan yyi sallar asubahi sannan bacci mai nauyi ya ɗaukeshi, bai farkaba sai wajan ƙarfe goma 10:00am yatashi toilet yawuce yayi brush yayi wanka ya fito ya sanya kaya ya fita zuwa palour, qannensa yasamu a palour suna zaune hassna tace yaya sadam breaksfast ɗinka yana man diining mummy tace idan kafito a gaya maka,
Toh yafaɗi sannan yawuce dining bai wani tsaya cin abinci sosai ba saboda yanda hankalinsa duk baya jikinsa ɗakin dady ya wuce kai tsaye bayan yayi sallama ya tsaya bakin ƙofa mummy dake ciki tace shigo mana sadam,
Advertisement
Toh sadam ya amsa sannan ya sanya kansa ciki, a kishingiɗe ya samu dady yayinda mummy take gefensa ga dukkan alamu taɗi takeyi masa kuma yana jin daɗin taɗin dan yanda annuri ya nuna a fuskarsa, ƙarasawa sadam yayi ɗan kusa dasu ya zauna akan guiwowinsa ina kwana dady yafaɗa yana kallon mahaifinnnasa dady ya amsa fuskarsa sake cikeda annashuwa yace lafiya ƙlau sadam katashi lafiya?
Lafiya ƙlau sadam ya ansa sannan yace mummy ina kwana? lafiya son harka tashi? Eh mummy natashi,
Shiru sadam ya zauna yayi yarasa ta yanda zai furta zancen dayake bakinsa,
Dady ya tashi ya zauna ganin sadam a zaune yasan magana yake tattare dashi lafiya sadam naga kamar kana son yin wata magana kuma kayi shiru karkaji komai faɗa kawai,
Kallon mummy yayi yace mummy dan Allah zamuyi magana da dady, zaro ido mummy tayi tace mai kake nufi kenan?
Sun kuida kai sadam yayi yace da dady kaɗai nakeson yin magana,
Da mamaki mummy ke kallon sadam wato har akwai maganarda zaiyi da dadynsa batareda ita ba?
Murmushi dady yayi yace toh mummy d'an bamu waje zamuyi magana da son ɗinki dady yayi magana cikin zolaya, kyaɓe baki mummy tayi ta miƙe tana faɗin tunda ba'a gayyatarmu a cikin zancen ai koba afaɗa ba zamu tafi, mummy tayi ta waje sadam ya bita da kallo, ta fita da kusan 2minute amma sadam baice komai ba, dady yace sadam kai nake sauraro, waiwayawa sadam yayi ya kalli ƙofa sai yana kallon kamar mummy bata tafi ba miƙewa yayi yaje ya leƙa ƙofar, ganin bata waajn ya sanya yaja ƙofan ya sanya mata key yadawo kusada dady ya zauna shi dai dady kawai ya tsaya yana kallon ikon Allah bai san wace magana bace haka da har sai an kulle ƙofa kafin ayita,
Zaunawa sadam yayi daf da dady yace dady dan Allah wata alfarma nake nema awajanka, dady ka taimaka ka tausayamin ka dubi wannan zance da zanyi maka da kyakkyawan tunaninka, dady ka duba zancenann da muhummanci kamar yanda kowani lokaci nake ɗaukan all'amurana da muhimmanci,
Advertisement
Murmusawa dady yayi yace In sha Allah can yiwa lamarim kyakkyawan fahimta sadam kai dai yanzu karkaji komai faɗamin wace maganace?"
Dady ni dai dan Allah kayimin alqawarin bazaka ƙi zancen da nazo maka dashi ba, girgiza kai dady yayi yace bazanyi maka alkawari ba sadam saboda bansan zancen ba amma nayi alƙawari zanyi iya ƙoƙarina nayiwa zancen kyakkyawan fahimta yanda bazan cutar dakai ba, yanzu inajinka faɗamin abunda ke tafe dakai kabar wannan noƙe-noƙen, dady dan Allah kayimun aure wallhy aure nakeso yafaɗi zancen da sauri kamar wanda zai sanya kuka,
Dady bai san lokacinda yafara dariya ba yace sure kakeso sadam? Sun kuida kai sadam yayi yace eh, jijjiga kai dady yayi yace sai yanzu na fahimci dalilin dayasa bakaso mummynka taji zancen, amma sadam kasan yanda za'a kaya da mummynka akan wannan zancen koh?
har yanzu kallon ƙaramin yaro take maka wanda bai isa aureba, nasani sadam yace sannan yadaura da fadin sanin hakan yasa na sameka dady saboda kai kafi kowa fahimtata kuma nasan idan har ka amince to zaka iya shawomin man mummy,
Nisawa dady yayi yace har indai ta wajena ne banda matsala sadam saboda ko ni lokacin dana auri mummynka ban kai age ɗinka ba, kuma na riƙeta mun zauna lafiya idanba ɗan abunda ba'a rasawaba bazata ce maka ga wani mummunan abunda nayi mataba, amma inaso kasani na auri mummynka tana sona insa sonta, yanzu kai akwai wacce zaka kakesone?har kakeson aurenta?"
Gyada kai sadam yayi yace eh dady, nisawa dady yayi yace nafarko sadam kai ba aiki gareka ba, mummynka baso takeyiba kana kallon ahaka zaka samu farin cikin da kakeso?
nan da nan idon sadam suka cicciko yace dady dan Allah ka taimaka wallhy yarinyar nan tun bata kai haka ba nafara zuwa wajanta babanta ya hanata kula kowa hatta da ƴaƴan ƴan uwansa sun nuna suna sonta babanta ya hana saboda yanaso yadawo mutumin kirki mai cika maganarsa, dady dan Allah karkace a'a zan zama mayaudari, bazasu ɗaukeni mutum mai gaskiya ba ko kaɗan mutumcina zai zube idanuwansu, nima kaina cikin zuciyata can zame me kallon kaina matsayin maci amana, dady ina fada maka hakane saboda nasan zaka fahimceni kuma a halin yanzu bbu amfanin ɓoye maka komai,
Jijjiga kai dady yayi yace naji amma mai yasa abaya ka ɓoyemin? Saboda ina tsoron yanda mummy zata ɗauki zancen sadam tafaɗi,
Toh sadam nidai yanzu bazance komai ba sai dai Allah ya za6a mana abunda yafi alkhairi zanyi ƙoƙoari har naga nacika maka burinka, amma kasani kada ka saka hope akaina da yawa ka ɗauki alamuranka da miƙawa ubangiji shine zaiyi maka magnin komai ba niba,
tashi kaje idan zaka wuce kacewa mummynka inason magana da ita sai naji ta bakinta saboda tanada hakki akanka bazan taɓa yimaka aure ba tareda amincewarta ba."
* FITATTU BIYAR NA KUD'INE.*
*FEEDOHM - SILAR WAYE?*
*ZAINAB BAWA- YARIMA FAYAD.*
*ZEE YABOUR - DR MUHRIX.*
*HAJJA CE - ANNURIN ZUCIYA.*
*NANA DISO - GIMBIYA SUHAYMA.*
LITTAFI BIYAR AKAN___500,
IDAN HUDU KIKE SO___450,
IDAN KUMA UKU NE___400,
IDAN BIYU KIKE SO___350,
IDAN KUMA D'AYA KIKE SO 200.!
TURA KUDINKI TA WANNAN ACCOUNT D'IN.
3126584401 FIDDAUSI MUSA FIRST BANK TARE DA SHAIDAR BIYA A 08036953516
KO KUMA.
ACCOUNT NUMBER:- 0003075326 ZAINAB M BAWA
Jaiz bank SHAIDAR BIYA TA 08161146563.
*KO KATIN MTN TA WANNAN LAMBAR 07065283730 TARE DA SHAIDAR BIYA.*
*SANNAN MUYI ADDING D'INKI A FITATTU GROUP🌹...*
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial151 Chapters
Emperor of Blue Flower Mountain
**NOT ON HIATUS! Updates are just slow right now!** Once upon a time, there lived two great and mighty spirits on the mountain. One loved humans, the other hated them. When their differences could not be reconciled, they came to blows, and the human loving spirit was chased out.Now there is only one spirit on the mountain. He sits on the peaks, looking down on those below him. Disaster and death is his reputation, and it is well earned. He is the Fairy Emperor, the King, and no one dares disobeys him. But he is empty on the inside.For he is alone.When anger and jealousy take everything, only love can create something new. This is a story of hope, redemption, and second chances.---- Discord for early releases and FREE STUFF: https://discord.gg/Q2tQhQH ---- Book 1: Empress of Blue Flower Mountain - Complete Book 2:Emperor of Blue Flower Mountain - In Progress Book 3:Princes of Blue Flower Mountain - N/A Cover done by me, the Author.
8 495 - In Serial16 Chapters
Golden Valley [Español] [Terror/Misterio]
Tus creencias se convierten en tus pensamientos, tus pensamientos se convierten en tus palabras, tus palabras se convierten en tus acciones, tus acciones se convierten en tus hábitos, tus hábitos se convierten en tus valores, tus valores se convierten en tu destino y tu destino está en Golden Valley Novela de Misterio/Terror clásica. Inspirada en juegos clásicos de terror, populares de los últimos tiempos como: silent hill,amnesia,resident evil,outlast,ect...
8 128 - In Serial10 Chapters
The Mermaid's Shoal
Elfyn O Se has lived by the laws of the sea his whole life. He'd go by Elf to his friends if he had any left, but at least his crew are willing to work with him, and it's not because he accidently cursed them all. Yet, maybe he can pull them together for one last job that might ease the fury of the tyrannical mermaid he wronged so long ago. He might have a chance to break the binds for himself and his crew, if he can pull it off. There's just one problem; a rival mermaid called Anwen. As mysterious as she is terrifying - and adamant that Elf can't win - she offers an alternative to break the curse if the crew can help her get home. The crew of the Ossory now finds themselves caught in an odyssey brimming with magic and monsters. Battling against champions of terrible adversaries, mysterious lights from the deep, and kleptomatic selkies who deal in blood, Elf is faced with a choice. Will he risk the future of his world to save his crews' souls, or condemn them all to protect the archipelago from certain calamity?
8 226 - In Serial22 Chapters
Mission Jurassic [Zach Mitchell x Male!Reader]
In which you must complete your first mission while also protecting two boys. Along the way, you find yourself falling for the older brother.
8 189 - In Serial38 Chapters
The Wing's Chronicle | Levi X Reader
Rank #1 LeviXReader (January. 26, 2021)Captain Levi Ackerman decided to clean the old headquarters castle's library and accidentally found a mysterious book It was the book we're the well known history behind the Wings Of Freedom's Chronicle were written that the Great Mortal Goddess with an Angel wings was born with special abilities to control all the nature elements and create a better melody using her Golden Violin and use it as her weapon against the enemies after she came down on Earth to help and save the Humanity They say that if you encounter her melody and her shadows dancing in the dark it means that she forbiddenly fallen in love with you and you're the reason why she become a half fallen But what if Levi encounter her from the past and he doesn't even have any idea that the Goddess was always around him? Are the rumors about the Chronicles are true and does she will go down to save them against the Titans?
8 187 - In Serial21 Chapters
Haikyuu One Shots
But stepmother Ball is life
8 340

