《ƘADDARAR RAYUWA》Ƙ page 33
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 33
Zaune nabila take gaban mai martaba kanta yana ƙasa cikin ladabi take gaida mai martaba, amsawa mai martaba yayi cikin nuna kulawa yace nabila yaya kuke da mijin naki? A kunyace nabila ta amsa da lafiya Ƙalau, mai martaba yace toh ina dai jikin nasa bbu wata matsala? Girgiza kai nabila tayi tace babu matsalar komai, mai martaba yace toh ma sha Allah, ina bakida wata matsala? Babu komai nabila ta fad'i, to shikenan idan akwai matsala dai kar kiji komai ki sanar dani kinji, in sha Allahu nabila ta amsa mai martaba yace toh tashi kije wajan mijinki Allah yayi miki albarka, amin nabila ta amsa cikin ladabi tayi masa sallama ta koma, ɗakin yarima haaliifaa ta wuce kamar yanda ta barshi haka ta sameshi, yana bacci ƙarasawa tayi ta kai hannunta forehead ɗinsa jikinsa babu zafi temperature ɗinsa normal hakan yasa ta sauƙe ajiyar zuciya, tun jiya daya kwanta baccin dare har yanzu bai tashi ba tayi zaton ko baya jin daɗine amma data taɓa jikinsa taji babu ɗumi sai hankalinta ya kwanta, tsananin tausayin yarima da takeji ya haifar matada soyayyarsa acikin zuciyarta duk da kasancewar ko waje take baya yarda ya zauna a wajan ko abincine bazaici wanda tabashi ba sai umma tazo da kanta,
Lulluɓansa tayi tawuce zuwa palour ta zauna ta nutsa tunanin wannan rashin lafiya ta yarima, wani lokacin zakayi zaton yarima yanada hankalinsa sai dai kawai rashin magana ita wannan cutar tasa tana ɗaure mata kai sosai, samada shekaru nawa amma ciwo yaƙi warkewa kuma bawai ba'a magani ba mai martaba da kansa yake shigowa ya yi masa abunda zaiyi ya fita, wani abun kuma yabata yace tayi agidan kokuma yabata addu'oi ya ce tayi,
wasu tana iyawa wasu kuma bata iyawa saboda bawai tayi wani karatun addini mai zurfi bane, tadai san wasu abubuwan, tana zaune umma tashigo da sallama, miƙewa nabila tayi cikin fara'a tana faɗin sannu da zuwa umma, umma tace yawwa sannu nabila yaya mai jikin? Dasauƙi nabila tafaɗi Juyawa tayi ta shige dining area ta buɗe fridge takawo mata ruwa ta ijiye goran da cup, tsugunawa tayi agaban umna ta tsiyaya mata ruwan ta miƙa mata, karɓa umma tayi taɗansha kaɗan ta ajiye, ta dubi nabila tace yariman yana ciki ne? Nabila tace eh umma yana ciki har yanzu bai tashi daga bacci ba gaban umma yafaɗi tace bai tashi ba kuma? Nabila tace eh, miƙewa umna tayi tace muje na dubashi nabila na gaba umma tana baya suka shiga ɗakin umma ta ƙarasa kusa dashi takai hannunta a neck dinsa tataɓa babu dumi, cikin yana yin damuwa tace toh Allah yasa dai lafiya bari naje zuwa jimawa idan yatashi zan dawo,
Advertisement
Umma tatafi bayan 3hours tadawo amma bai tashiba haka ta zauna tayita jiran tashinsa bai tashiba sanda taga dare yana shirin yi tacewa nabila zata tafi idanda matsala da tasanr da ita ta awaya sannan ta sanarwa mai martaba sannan kuma kada tafita a ɗakin dayake ta zauna a ciki ko zai tashi bata wajan,
toh in sha Allahu zanyi nabila tafaɗi cikin ladabi,
Har dare yayi yarima bai tashi ba nabika tasaya ta zuba masa idanu tajira tashinsa harta gaji, ra6awa tayi gefensa ta kwanta nan da nan bacci ya ɗauketa saida dare ya tsala sosai ihun yarima ya tashi nabila bi takeyi tana rirriƙeshi amma kamar wacce take ingizashi ƙara ihu yakeyi yana mimmikewa wurgarda iya yayi gefe ta buga kanta hakan yasa cikin matsanancin tsoro tatashi tafice a ɗakin hijab ta ɗauka tayi hanyar fita,
Sallamar mai martaba taji cikin sauri yashigo palour ɗin, ganinsa yasa nabila ta matsa masa a hanya ɗakinda yakejin ƙawar nan yanufa yaɗauki tsawok lokaci akan yarima yanayi masa abubuwan da suka dace kafin yadawo dai-dai, aɗakin ya zauna har aka kira sallar asubahi nabila tana zaune a palour bacci yafara ɗaukanta taji murɗa ƙofar mai martaba tashi tayi ta zaune mai martaba yace abun ya lafa zaki iya shiga, toh Allah yasaka da alkhairi nabila tafad'a ta miƙe tayi ɗakin shikuma mai martaba yafice waje donyin sallah,
Atsorace nabila ta shiga ɗakin saboda ya bugata da yawa goshinta yanzu haka harya tashi, ganin yana bacci yasa ya wuce zuwa ɗakinta, sallah tayi sannan ta kwanta bacci saboda baccin da bata samu ba da dare,
10:00am umma tashigo dubashi saboda jiya ta kwana da tunanunsa dakyar ta runtsa,
Bata ga kowa a palour ba hakan tasa ta zauna tana jiran fitowarsu, rumace tashigo ta ƙarasa wajan umma tana faɗin umma ke ɗayace azaune ina anty nabilan take?
Inaga tana cikk umma tabata amsa, ciki ta ƙaras atatasheta sannan tafito tace umma tana ɗakinta ki ƙarasa ɗakin ya yarima mana, miƙewa umma tayi tace toh barina dubashi,
Akwance ta sameshi idonsa a buɗe da alamu ya dad'e da tashi a baccin,
Advertisement
Aranar umma anan ta wuni saboda taji abunda yafaru jiya gabaki ɗaya tacika da tausayinsa shiyasa ta wuni a wajansa."
----
Sawwama bayan tatashi da safe taga jikin mahaifanta duk yayi sanyi gabaki ɗayaa kamar wanda suke tattare da wata damuwa bata tambayesu saboda tasan da hurimintane da sun sanar da ita,
Hakan yasa taci gaba da dawainiyarta na ranar amma hankalinta yana kan abunda ya damu mahaifanta ya sanyasu tashin hankali haka,
Har taje ismaliya tadawo amma bata daina tunanin abunda yake damun iyayenta ba, har abun yaso ya dameta fiyeda su ɗinma,
Da dare sadam ya iso ya kirata a waya ya shaida mata tafito ta samu baba da mama suna zaune a baranda, tace zan fita waje yazo shi, baba yace toh dama kuwa inason magana dashi idan kin isa ki faɗa masa kafin ya tafi ya jirani zamuyi magana a ladabce sawwama ta amsa ta fita zuwa wajansa,
Bayan ta fita bada daɗewa ba ta shaida masa cewa baba yana son magana dashi, gaban sadam yafadi sosai saboda yasan zancen bazai wuce na turowarsa ba,
Bai daɗe ba yace zai tafi tayiwa baba magana,
Bayan baba ya fito sun gaisa baba yake shaida masa yayiwa mahaifansa magana su fito ayi magana baba bai ɓoye masa ba ya shaida masa maganarda sukayi da yayansa jiya, gaban sadam yafina kowani lokaci faduwa nan da nan yashiga damuwa sosai,
Bayan sun gama yayiwa baba sallama yatafi, yana isa yagaki daya ya kidime ya rasa yanda zaiyi cikin rashin mafita ya kira najeeb ya shaida masa, najeeb yace ka sanarwa su dady kawai sadam ai yanzu dai kakai ace anyi maka aure yanzu nima zancenda nake maka wani watan za'aje min tambaya, idan aka sama maka aiki sai kayi aurenka zaka iya rike matarka ai, gara ka sanarwa dady tun wuri saboda kaji yanda kukayi da mahaifinta, wallhy mahaifinta ma mutumin kirkine banda haka ba da tuni yabawa ɗan ɗan uwansa aurenta kai dai yanzu abunda nakeso dakai kazama jajirtacce duk wani abunda zaije yazo kayi hakuri ka jure shi neman aure ya gaji ƙalu bale kala-kala sai kayi hakuri kafin komai zaizo makada sauƙi, ka jure komai da zaka gani daga wajan yan uwanka zuwa wajan yan uwanta, sannan kuma ban baka shawarar fara samun mummy da zancen ba, kafara samun dady kuwa nasan shi zai amince kayi nusar dashi har ya amince kafinnan ka barshi shi da mummy shi sai yayiwa mummy magana da kansa,
Godiya sadam yayi masa sukayi sallama aransa yanzu yanaji koma menene zaije yazo zai jureshi akan sawwama, jira kawai sadam yakeyi gari ya waye domin gobe-gobe zai samu mahaifinsa basai wani lokaci ba, duk wani tsoro da fargaba datake ransa ya ciresu, jira kawai yakeyi gari ya waye yaji yaya zasu kaya da mahaifinsa."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial8 Chapters
The Orb Weaver Chronicles
"The Orb Weaver Chronicles contains several major and unique events that may or may not unknowingly intertwines with one another. The author of these chronicles is unknown, although some have hinted at the symbolism behind its name..." - Year unknown, location unknown 9 February 2022 Update: Welcome to the companion short story compilation of my novel trilogy The Shadow Paradigm. This compilation features prequels, sidequels and sequels to the novel's major plotline, as well as featuring a wide range of characters, new and recurring. Prior knowledge of the novel is not necessary as the Orb Weaver Chronicles' short stories are standalone. Once called The Arkesyyan Chronicles, I've deleted quite a few of its old stories. Due to the new avenue and revision, oriented toward more mystery and film-noir ambience, that I took my stories into, I've removed all aliens and overly sci-fi aspects of the whole TSP lineup, so I've updated the Orb Weaver Chronicles accordingly. I hope you enjoy them, and in time, a revised version will also be updated.
8 93 - In Serial34 Chapters
Series of One-Shots That Might Become Their Own Series.
Just some crap to write when I'm being a lazy son of a gun and not writing chapters for my current stories out right now.
8 155 - In Serial42 Chapters
MUHAMMAD
I decided to bring it back after it being taken down 3 times.THIS BOOK IS NOT ABOUT MUSLIMS!!!!! Take that mess some where else besides my comments or just don't read it.
8 111 - In Serial42 Chapters
The Bad Boy And Me |✅|
Jessica Jensen with her family shifts to a new town. There, Jessica comes across many people one of them being Jace Brewer,the bad boy of the school. She dislikes him with passion but then she comes across something about Jace that shocks her. Jessica later finds out that Jace is not really the one he acts as. She breaks his walls and they later become great friends. The friendship later turns into something so beautiful that you can only understand it when you read it.....The first 3 to 4 chapters are damn shitty but after that you'll enjoy reading it. Please give this book a chance.....I hope you all will like it.Please ignore all the grammatical mistakes.I'll try to edit them soon.
8 66 - In Serial13 Chapters
Rejected by the Bad Boy ✔
ReuploadedMates were supposed to be destined for each other, to remain together for the rest of their lives after bonding. It was a different story for the bullied girl and her bad boy mate, who rejected her for being the wallflower of the pack...
8 62 - In Serial20 Chapters
HIS ALPHA
Her lips brush against his, "Mine," she whispers before kissing him. Sparks flew throughout both of their bodies and their lips molded together perfectly. "You're defiantly coming home with me," she says as she pulls away. Aella winks at him before leaving him frozen against the tree. Adonis Accardi is the Beta to the Moon Stone pack and when he attends a gala for unmated wolves, he didn't expect to meet his mate.Aella Xavier is the Alpha to River Eclipse pack, she is known to be the deadliest Alpha in California but she isn't that at all.Adonis and Aella go off with a rocky start but damn it will be a smooth finish, so just read it.
8 85

