《ƘADDARAR RAYUWA》K page 32
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 32
Da fara'a baba ya ƙarasa wajan yana faɗin A'a yaya zakari kaine agidan namu? Aida kayimun aike sai nazo basai kazo ba, da fara'a yaya zakari yace A'a zuwanne ai ya kama shi yasa kaganni niɗinne yakamata inzo ba kaiba, baba yace toh Allah yasa dai lafiya yaya? yaya zakari yace Ahh lafiyace ta kawoni wallhy haɗeda ɗumbin alkairi, baba yace toh alhamdulillahi madallah abu yayi kyau,
Gaisawa sukayi baba ya tambayi ya iyali yaya zakari yace sunanan lafiya to madallah haka akeso ai baba ya amsa,
miƙewa baba yayi yace barina shiga ciki na dauko tabarma yana faɗin haka ya sanya kansa ya shiga ciki a ƙanƙanin lokaci yadawo hannunsa riƙeda tabarma shimfiɗawa yayi yace yaya bismillah suka zauna,
Yaya zakari yace toh alkhairi ke tafe dani hamisu yarone ɗan wajena ismail ya hango abunda mu bamu hangoba kasan ana faɗin abunda babba ya hango yaro ko ya hau rimi bazai hango ba amma wannan karon zancem ba haka yake ba wannna karon yaron shine ya hangi abunda mu manyan bamu ganiba,
Cikin rashin fahimtar yanda maganar yaya zakari tadosa baba yace kamar me kenan ba yaya?
Shigowar halima zauren hannunta d'aukeda ruwa a cup na silver yasa sukayi shiru amsa sallamarta sukayi ta isa ta ajiye ruwan had'eda gaida yaya zakari amsawa yayi cikin fara'a,
Sai bayan tatafi sannan yaya zakari yace toh ismaila dai yazomun da wani zance, to shine na zauna dakyau nayi tunani sai naga zancensa yana kan hanya, yaro yayi kyan kai,
Shiru baba yayi yana saurarensa yaya zakari yaci gabada faɗin
Wato shi ismail yaga ƴar wajanka babbar me sunan mama kenan koh?
Baba yace sawwama kenan?
Yaya zakari yace eh ita ce inaga babbar dai yacemin ranar dayazo ya ganta ya yaba da hankalinta sosai sannan ya shaidamin cewa yana sonta zai aureta, gaban baba yafad'i dammm jin zancen ɗan uwannnasa yaya zakari yaci gaba da faɗin to shine nace barina sameka dan wannan abun farin ciki ne sosai zumunci mai ƙarfine zai ƙara ƙulluwa atsakani, dama nace masa toh baza'ayi abu kai tsayeba zan sameka kai mahaifin yarinya in faɗa maka sannan kuma kaje kayi shawara da mahaifiyar yarinya dakuma ita kanta yarinya kaji ta bakinsu idan babu idan wani tsayayye sai ayi magana tunda wuri ayi abu cikin kwanciyar hankali, tunda nasan koda ka samesu toh ai abu bazai gagara ba dan suma zasuyi murna amma adai samesu ɗin,
Advertisement
Baba kansa yana ƙasa daƙyar ya iya ɗagowa ya ɓoye damuwarsa yace toh shikenan yaya In sha Allahu can samesu muyi magana yanda mukayi zan sanar dakai Allah ya za6a mana abunda yafi alkhairi, yaya zakari ya amsa da amim miƙewa yayi yana faɗin toni barina wuce yanda kukayi sai ka sanar dani ɗin,
Baba yace har tafiya yaya baku gaisa da mutanen gidanba gashi kuma ko ruwa baka shaba, yaya zakari yace Alhamdulillahi nagode ina gama cin abinci na taho ka gaidamin da iyalin, baba yace toh zataji, miƙewa yayi ya rakashi har waje da ɗan nisa kafinnan yadawo,
Jiki a sanyaye baba ya shiga gida zama yayi gabaki ɗaya kamar wanda ruwa ya cinyeshi, mama ta kalli baba cikin kulawa tace baban sawwama wani abunne yafaru?
Girgiza kai baba yayi yace ummi bai faruba amna yana gab da faruwa saboda zancenda yaya zakari yazomin dashi yau yayi matuƙar girgizani narasa awani ma'auni can ajiye zancen,
Mama ta matso kusa dashi tace mai yazo maka dashi kuma?
Shiru baba yayi yakasa cewa komai yayi ƙasa da kansa, mama wacce iya tunaninta ya tsaya a abunda ta fahimta tace baban sawwama hhar indai akainane kada ka sanya ranka a damuwa nasan zancen bai wuce ace ka ƙara aure domin samun ɗa namiji da zai gajeka ya kula da kai ba, idanta nine kada kaji damuwa domin ba hanaka zanyi ba,
Girgiza kai baba yayi yace da wannan ne zaifi yimun sauki ummi domin inada damar da dance eh ko A'a wannan kaina kaɗai ya ashafa ba ƴaƴana ba zan iya ɗaukan ko wani irin lamari duk zafinsa akaina amma ba akan ƴaƴana ba,
Mama wacce kanta ya gama kullewa tace ban gane mai kake mufiba baban sawwama, baba yace wai ɗan wajansa isma'il yakeson auren sawwama, dafa ƙirji mama tayi tace auren sawwama kuma?
Baba yace haka dai yace kingani na farko bazan iya bashi auren sawwama ba saboda dalilai biyu, na biyu rashin bashi auren sawwama zai ta6a zamuncin mu,
Advertisement
Abu na farko da zaisa bazan bashi auren sawwama ba shine dalilin wannan abu daya faru da ita idan ɗansa ya aureta dole zai san da faruwar hakan zai dauki mamana da wata manufa ya ringa yimata mummunan kallo, ba fata akeyiba ba lallai ya iyaci gaba da zama da itaba, kuma bazai yiwu mugaya musu yanzuba saboda faruwar abu samada shekara uku ace bamu sanar da dangiba saida akazo neman aurenta zasu iya yiwa mamana wani mummunan fassara nikuma bazanso hakaba yayinda bazanso abunda zai taɓa zuciyar mamana ko yaya yake sannan daga karshe zasu iya cewa sun fasa auren yayinda sukaji wannan labarin kuma ba lallai dan suna ƴan uwanmu ace sun rufa mana siriinmu ba,-
Abu na biyu da zaisa bazan bashi aurentaba shine inason abunda mamana takeso mamana tanason wannan yaro sadam, dan kyautatawa ɗan ƴan uwana dasu kansu ƴan uwana bzan iya tauyewa ƴata hakkinta ba yazamana na barta ko oho sukuma na biya musu buqata ba na shiga rayuwarta na fifita farin cikinsu akan nata, bazan iyaba bazan iya yanda wasu iyaye sukeyi su fifita farin cikin ɗan ɗan uwansu akan na ƴaƴansu ba, shine yaganta yace yanaso kinga idanna bashi aurenta shi na cika masa buri na faranta masa na bashi abunda yakeso yayinda na baƙantawa ƴata na rabata da abunda takeso, kinga hakan babban shiga hakkine, wannan yaro sadam yayi ɗawainiya da sawwama yayi ƙoƙari ya naima mata ilimi na arabi dana boko sutura idanna samu inayi mata dai-dai gwargwado amma kafin nayi mata ɗaya yayi mata uku, yanason sawwama sosai kina kallon idan naki bashi aure nabawa ɗan ɗan uwana me sunanmu zai dawo?
Maciya amana mama tabashi amsa itama jikinta yayi sanyi baba yace bayan cin amana harda butulci, dan haka zuwa gobe idan yazo dakaina zan sameshi muyi magana dashi ya sanarwa iyayensa suzo ayi magana tunda aka fara haka gara ayi yawuce mana kawai duk wani tsai gumi da gutsuri tsome ya ƙare, ƴan uwana kuma nasan yanda zanyi dasu,
Sannan dan Allah wannan zance daga ni sai ke banason mamana tasan da wannan dance saboda nasan halinta dason faranta mana zata iya sacrificing na farin cikinta akanmu,
mama tace in sha Allahu babu wanda zaiji wannan zance, baba yace toh Allah yasa,
Baba ranar bacci ɓarawone kawai ya ɗaukeshi ya tsaya yanata tunanun yanda zai ɓullowa all'amarin."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial8 Chapters
Epic Blade - a LitRPG Adventure
It's the most advanced virtual reality gaming system ever created. So real, you might wind up in another world. A LitRPG / GameLit adventure full of monsters, portals, loot, and leveling up. Tobias Martin is one of the best gamers in the world, playing the most advanced game ever created. When a mysterious portal in the game appears, he enters a new world of magic that's more real than he ever could have imagined. Forced to start from scratch, he must build himself back up to a top level adventurer if he ever wants to get home again. Along the way, he will explore a world full of wonder and danger, meet new friends, slay terrifying monsters, and level up like his life depends on it. Because it does. Can Tobias survive the most epic adventure he has ever encountered? Get started on your next epic adventure today!
8 104 - In Serial21 Chapters
My next life as a skeleton.
My father was going to kill my mother. Should i save her. I made a decision and saved her but got killed in this incident. When i opened my eyes i was a skeleton in a dungeon. I will become stronger and will not die in this life.
8 82 - In Serial6 Chapters
Shoot on sight
Zone has no owner, it has its rules It shows no mercy, to both wise and fools. It has no God, it gives no hope It gives to kind, last rites and rope. It’s a Hell on Earth where demons thrive But people kill, to get inside. People kill, to leave this place People die, for a chance to stay. For those, outside, they dream of horrors We live inside, horrific borders. We live, we thrive, just like those demons. Here, our lives, they have a meaning. Zone has no God, it has no Devil But it has us and its enough We are in Hell or maybe Heaven Gates are here, in front of us. The Zone has many rules and none of them would make much sense to you, living on the Outside. For example here, you would never hear, “I’m sorry for your loss”. Only silence would be the answer. The most empathetic action you would receive, is an open flask and a nod. People here don’t expect to live long and happy lives and even the most optimistic person at most, would hope to die inside of a blender. It's the most painless and quickest way to die in The Zone, and the cleanest. Your body would be torn apart in a second by countless gravitational pulls, all centered on you, leaving nothing but a red circle outside of its perimeter.
8 70 - In Serial12 Chapters
The Citadel of Stairs, The Armory Book One
A band of five mercenaries serve a dead god across scattered lands of powers and principalities, answering to no allegiance or authority but their own, and the needs of their dead god's afterlife. To power their heaven's dying mechanisms they must kill and send those stolen souls above so that their god's refugee faithful have a place to go when they die, even if all that's left to them is an eternity of waiting. There is no peace for this five. No rest. There is only the next job. Cover Art Credit: Dan Mandell
8 183 - In Serial6 Chapters
To live is to Dream (LitRPG; First Draft)
A new Power has come into the World and seeks to change it. Being on the last dregs of sanity and full of alcohol Daniel West receives an opportunity to seek revenge. -----------------------------------------------------------------------------------------------------------------To live is to Dream is the second book of the Just a Dream series. You do not have to read the first to enjoy the second, but there will be recurring characters along the line. The first book features Mir, a man that dislikes how his current world appears and hence wants to change it. The second book will feature other people and how the changes implemented by Mir affect their lives. For those interested in my first book, it's easy to find it. Just beware that with the first book, it was my first time writing and there are a lot of grammar errors despite lots of editing, at least at the beginning of the book. The cover was done by Lmarief. I had requested something bizarre and she delivered. I have even used it as part of the story since her interpretation of my imagination was a bit different. Still, I loved it. As a thank you gift, I posted a link to her profile here for others who want a unique cover. https://www.royalroad.com/profile/220043
8 54 - In Serial13 Chapters
Andy and Sam Rookie Blue
rookie blue
8 92

