《ƘADDARAR RAYUWA》ƘPage 31
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 31
Hajiya suwaiba ce zaune maganganun hajiya babba ne suke dawo mata, me hajiya babba take nufi da cewa tayi gaggawar raba yarima da matar sa, hakan yana nufin matarsa tana d'aya daga cikin waɗanta suke bashi kariya kennan? Har in dai kuwa hakane to tabbas zata samo hanyarda zata rabashi da matarsa, to amma ta yaya kenan? Wannan ne bata saniba domin ko matar tasa bata ta6a sanyawa a ido ba balle wani magana ya shiga tsakaninsu ba, baare har ta samu hanyarda zata isa gareta, koda ta isa gareta batada tabbacin zata amince da zancenta, tunda hhat tashigo cikin gidan sarauta ta tabbata itama da nata shirin ta shigo, toh amma
har in dai raba yarima da matarsa yanada nasaba da cin nasararta to dole kuwa ta nemo hanyarda zata rabashi da ita domin duk wata hanyarda zai kawo mata cikas wajan cika burinta zata tosheta zatasan yanda zatayi tayi maganin wannan hanya,
Bazata lamunci duk wani abunda zai kawo nakasu wa cikar burinta ba,
Wayarta dake gefenta ta jawo tayi dialing number ɗin yaya hadiza, cikin hanzari yaya hadiza taɗaga kiran, hajiya suwaiba bata bari sun gaisa ba tace yaya inason ganinki yanzu, ba'a ɗauko lokaci ba yaya hadiza ta'iso hajiya suwaiba tace" yaya ashe cikin masarautarnan bamu kaɗai muke farautar rayuwar yarima ba, man ta labarta mata yanda sukayi da hajiya babba, yaya hadiza tace ahaf dama ai nagaya miki cikin wannan masarauta kibar kowa da kika ganshi dan babu wanda zai buɗe miki cikinsa ki gani amma da sai kin sha mamaki, duk wanda kikaga yana wani nuƙu-nuƙu to munafunci ne,
Amma zancen hajiya babba nayi mamaki kuma banyi mamaki ba, sai dai fa hajiya kada mu sake da ita domin itama ba abun yarda bane, kada mu sake mu buɗe mata sirrinmu Saboda idan tasan abunda yafaru shekarun baya itace zata fara tona mana asiri sannna ta sanya aci mana zarafi, A wulakantamu a dauki mummunan mataki akanmu,
Advertisement
Dogon numfashi hajiya suwaiba taja tace wannann haka yake bazamu ta6a yin wannan kuskurenba bazamu ta6a barinta tasan wannan sirrin ba,
Yanzu mukoma zancen wannan matar yaronan haliifaa nifa inaga abunda take faɗi gaskiyane yakamata mu rabashi da ita wannan shine cikon burinmu sannan ta hanyarda zamu sameta har mu rabata dashine shine matsalar, murmusawa yaya hadiza tayi tace wannan aiba matsala bace bakuma abun damuwa bane hajiya, ki bani nan da 1week zaki sha mamaki,
Jijjiga kai hajiya sawaiba tayi tace indai 1week ne nabaki yaya hadiza kada ki bani kunya nidai burina yacika ya fiyemin komai gidan duniyar nan, sunkuida murya yaya hadiza tayi sannan tayi da kanta Ƙasa tace aikuwa hajiya har in dai ina rayuwa a doron ƙasa yazama kamar dole burinki sai ya ciki, zan tafi ko bangon duniya ne dan cika miki burinki, cikon burinki ai shine namu, idan burinki ya cika nima nawa yacika, duk wani abunda kikga ina yinsa a gidan duniya danke da ƴaƴanki nake yinsa, haba hajiya ai ki kwantarda hankalinki haba-haba ai indai ina raye burinki zai cika, nan tafara yiwa hajiya suwaiba daɗin baki domin samin shiga wajanta,
Aikuwa hajiya suwaiba taji daɗi tace toh yanzu ki ƙarasa cikin drawer can ki ɗebi abunda yake ciki zuwa gobe zanyi miki aika, ni dai abunda nakeso dake shine kada ki zauna tako'ina shiga zakiyi,
Yaya hadiza tace aikuwa hajiya wannan yazama dole babu zama ahaka sukayi sallama."
—————
Da sauri sadam yawuce palour ɗin Kar mummy ta ganshi yana sanɗa kamar wani ɓarawo kafin ya isa ƙofa ya tsinkayi muryar mummy tana faɗin ina zakaje mummy dake ƙofar ɗaki ta jefo masa tambaya, tsayawa yayi cak sannan ya juyo ya kalli mummy cikin son waskewa yace zanje wajan najeeb ne yanzu zan dawo,
dawo kazauna zamuyi magana mummy tafaɗa haɗeda ƙarasawa kujera ta zauna, ƙarasowa yayi ya zauna sanda mummy taɗan ɗauki lokaci sannan tace sadam menene yake damunka? I smell something fishy, akwai damuwa atattare dakai maza faɗamin damuwarka,
Advertisement
Ɗan murmushin da bai kai zuci ba yayi yace babu komai mummy ni babu abunda yake damuna wani abunne yafaru?
Mummy ta tsaya tana ƙare masa kallo daga yanda yake magana zaka gane cewa baida gaskiya, mummy tace sadam kada ka maidami ƙaramar yarinya nifa mahaifiyarka ce kada kace zakayimin wayo, wayo kuma mummy? to akanme zanyi miki wayo? Nifa ɗankine, ki yarda dani da gaske nakeyi babu komai idanda wani abun ke zan fara zuwa ina faɗawa kinsan banda wanda yawuceki kinsani mummy dafa shoulders ɗinta yayi yace to mai yasa can ɓoye miiki damuwata ma? Kefa mahaifiya tace ki kwantar da hankalinki, miƙewa yayi yace mummy dare zaiyi bari naje yanzu can dawo bazan daɗeba yana gama faɗin haka yayi wane da sauri, da kallo mummy tabishi amma sam bata yarda da abunda yake fad'aba saboda jikinta yana bata cewa yana tareda damuwa dan gabaki ɗaya kwanakinnan ya canja,
Miƙewa tayi tana faɗin koma dai menene idan yayi tsami zanji,
Wajan sawwama sadam yaje bai daɗeba yadawo saboda yaga idon mummy yana kansa zata sanya ido taga lokacin dawowarsa,
Bayan yadawo ya kirata a waya anan suka qarasa hirar tasu."
Baba yana zaune bayan isha'i yadawo suna d'an tattaunawa da mama, sallama sukaji daga zauren gidan baba yace muryar wa nakeji kamar ta yaya zakari? mama tace anya kuwa baban hafsa yaya zakari awannan lokacin? Kodai muryarce tayi kama,
Sake yin sallamar da aakayine mama tace toh nima dai yanzu kamar hakan naji ka duba mana,
miƙewa baba yayi yana amsa sallamar da wa'alaikasslam ya fita waje domin ganin mai sallamar."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Nasan bazaki kasa karanta Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial11 Chapters
Tamer Untamed
What will you do if your world faced an unparalleled threat? One that'll just keep coming back. No matter how hard you try to get rid of it? Be prepared for the story of Bishop Riley, a modern day teenager who faces such a threat. His whole life turns upside down and inside out when a mysterious brochure appears in his bathroom. Together with the beasts he tames, this unlucky teen will stop the unstoppable force. That is if his terrible luck doesn't kill him first or the beasts don't eat him or anything else that could go wrong......
8 192 - In Serial36 Chapters
Blood Limit
This time I've gone ahead and chosen my very own bloodline limit. With it, how could I possibly fail. the thing that stand in the path I forge shall soon fall away for its time for my own grand appearance as The MC! ~Arc 1 chapter 1-19 ~Arc 2 chapter 20- ?" ------_________------- (Disclaimer : Ok ill be brief and say I don't own naruto at all if you readers notice things from other shows or whatever I'm not the creator nor claim to be. ) But I am absolute owner of my other novel which isn't s fanfict. ~~ ~ This is only a Naruto fanfiction, if I add any thing it will be only from anime - maybe games and nothing else. If I add things from other anime it will be seen here. -Naruto (world, abilities, characters) -Fantasy (Swamp, Elf, zombie, modern day, 'pending..') - ~synopsis in/complete editing~
8 176 - In Serial9 Chapters
Devils Demons and Dead Men
By the time most people have heard of the newest multiplayer fantasy role-playing game Kings and Conquests, developer Fairly Unusual Games has been overwhelmed by a $200 million crowdfunding haul. Founders Accounts are going to six-figure contributors. There is talk of an augmented reality mobile accessory app and 3D printable treasures that can be sold for real money. The hype is beyond belief. Gaming fans go berzerk. With contributors and the media eagerly anticipating a release date announcement, Fairly Unusual's stock suddenly and inexplicably plunges. CEO Garrett Wyland, once a darling of both Silicon Valley and Wall Street, is indicted by a federal Grand Jury for insider trading the day before his company files for Chapter 11 bankruptcy. Less than 48 hours later, Wyland is shot and killed by officers of the Mississippi Highway Patrol attempting to execute a fugitive warrant. A briefcase full of cash, a fake ID and an airline ticket are found in his car. Weeks pass. With accusations flying, lawsuits being filed nationwide and revelation after revelation rocking the online and offline media, a fourth-rate host of a little-known game streaming channel receives an e-mailed gift marked 'Kings and Conquests News' from one of his subscribers. Thinking it's some kind of prank, Jordan Hall opens it and discovers a Founder's account login to a fully functional Kings and Conquests server, a 100-year pre-paid subscription and map coordinates marking a dangerously isolated in-game location labeled 'Safekeep.' The e-mail is from Garrett Wyland.
8 69 - In Serial12 Chapters
Nagol: The Skeleton King
Nagol one of the last crusaders of Light leads his order to defeat the Demon king, with heavy casualties. Nagols order is reduced to three survivors but just as the Demon king is slain the United Kingdoms of Order turn on the Crusaders destroying the proud order of Light. Witnessing his own mother slain then his best friend before he himself was brought down by the soldiers he had fought side by side with. His Rage and Sorrow caused the Goddess of light great suffering, and so her brother The God of Death took him to be forged into the King of the undead.
8 79 - In Serial11 Chapters
Danganropa OneShots
Like the title said, it's just Danganropa oneshots I mostly will do Amasai though💙= Fluff💔= AngstI do take ship requests I do not own Danganropa or any of the artwork shown here I will try to update at least once a week
8 197 - In Serial7 Chapters
Fallen angel
This is my first one so expect it to be crap. Basically Izuku depressed and abused then gets saved by aizawa so dadzawa storyAlso I'm on phone so expect spelling mistakes
8 157

