《ƘADDARAR RAYUWA》K page 29
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 29
Auren nabila da yarima yacika shekara daya yayinda duk wani abunda take yimasa na kyautatawa bata canjaba, duk wani abunda tasaba tanayi bata dainaba har yabi jikinta, amma fa rigar bata sauya zaniba domin kuwa har yanzu yarima baiyi sabo da itaba kuma ko sau d'aya bai ta6a kar6an abincin hannunta ba ko sau d'aya idan kuma tana wajen toshi tashi zaiyi bazai zauna awajan ba saima dai idanda umma ko ruma awajan, amma duk da haka tana qoqari a al'amuransa sosai bata nuna gazawa ko gajiya biyayya sosai take yiwa umma fiyeda tunani,
Hankalin umma yanzu yagama kwanciya da auren yarima duk da wani sa'in ma acan take wuni takan zauna tabashi abinci tazauna dashi na wani lokaci haka,
Ruma kuma gabaki d'aya takoma shashin da zama tana ebewa nabila kewa sosai dake itama ruma tana jin ddin Zama da nabila domin tana da kyawawan halayya,"
Shi kansa mai martaba yana son nabila sosai tashiga ransa saboda yanda take kulawa da al'amuran jikannasa."
———-
Tunda yarima yayi aure hajiya suwaiba tarasa duk wani kwanciyar hankalinta, ko matarsa bata ta6a gani ba,
Shiru labarinsa kamar baya cikin masarautar koda tarinsa baya fitowa,
Wannan lamarin ya sanya tadawo kamar wata ta6abibbiya duk ta yanda zataji labarinsa nema kawai takeyi.
————
Mai martaba zaune a dako da littafi na addini a hannunsa yana dan research dinsa kamar yanda ya saba kullum yana kan bincike akam ilimin addini,
Babban malamine wanda duniya kanta take qaruwa da iliminsa wanda duniya take alfahari da samun malami mai ilimin addini irinsa,
Ya wallafa littafai dayawa na addini islamiyayo a qasashe daban daban nasa wanda ya bude, duk wani burinsa bai wuce akan addini ba, duk wani tunaninsa yana qarewane akan addinin musulunci. Dumbin sanin dayake dashi bai hanashi qara neman ilimin ba komai qanqatarsa tsufansa girmansa da shekarunsa da mulkinsa bai sany ya daina neman ilimi ba, duk wani taronda za'ayi na addini a duniya dole sai ya halasci wajan girmamashi akeyi sosai,
Kaff cikin zuri'arsa yarima haliifa ne ya gajeshi, domin ilmi irinna yarima haaliifaa har ya so tadda na kakansa. Ilimjnsa har yakan bawa mar mataba mamaki wani lokacin, hatta da deegree dinsa akan addini yayita,
Da badan addini irin na mai martaba dakuma yarima ba da andade da kawarda su adoron qasa da yarima haliifa ba baikai iwar haka ba."
Advertisement
Daya daga cikin matan mai martaba itace mahaifiyar mijin hajiya suwaiba tana zaune gefensa tana jiransa ya idda bincikensa,
Sai bayan yagama sannan ya juya yana dubanta yana jiran jin mai yakawota, sannu da gida ranka shi dade kai kawai ya gyada mata,
Nisawa tayi sannan tace yallabai kwana biyu banjin labarin jikin yarima? Allah yasa dai yana kan samun sauqi,
An godewa Allah mai martaba yafada daga ban sai sake cewa komai ba, duk yanda taso jin wani zance gameda yarima haalifa bata samu hakanba."
Bayan ta fita daga sashin mai martaba kai tsaye sashin hajiya suwaiba tawuce, a palour ta sameta tareda mutane dayawa a kofa ta tsaida kuyanginda da take tafe dasu,
Hajiya suwaiba tayi mamakin ganinta dan rabonda ta shiga sashinta zai iya kaiwa 7yrs sai dai ita taje ta gaidata sa'i-sa-i,
Duban mutanen wajan tayi tace ku bamu waje zamuyi magana, cikin girmamawa dukansu suka fice ta dubi daya daga cikin jakadanda suke shirin fita tace ki tabbata babu wanda ya shigo sannan kada kowa yazo kusada qofa maganace mai muhimamnci, cikin girmamawa tace angama ranki shi dade yanda kikace haka za'ayi,
Suna fita hajiya suwaiba ta sauka qasa tana gaida ita gaisuwa irinta saurauta,
Gyada mata kai tayi alamun taji ta amsa, sun dade ahaka sannan ta dubi hajiya suwaiba tace Suwaiba!
D'agowa hajiya suwaiba tayi ta dubeta har cikin ranta batajin dadin yanda uwar mijin nata ke kiran sunanta babu ko wani sakayawa aciki ga yanda take gwada mata mulki da iko duk ranarda danta yahau mulki ita kana kakartasu ba barinta zatayiba,
Magana nakeso muyi suwaiba hajiya suwaiba dataji zafin zancenta tadaure tace hajiya aida kin aiko sai nazo basai kinzo da kanki saboda lafiyar qafarki,
Murmusawa hajiya babba tayi sannan tace babu damuwa dama yakamata ina dan taka qafar tawa,
Suwaiba duk abunda kike aikatawa a masarautar nan nasani nasan cewa ciwon yarima da hannunki aciki,
Da sauri hajiya suwaiba ta d'ago tana dubanta da mamaki tsoro duk ya kamata kasa magana tayi ta yida kanta qasa gabanta yana dukan uku-uku tana tunanin wannan magana taje gaban mai martaba aita kade ba itaba har y'ay'anta abun zai shafa gashi burinta bai kaiga cikiba,
Muryar hajiya babbace ta katse mata tunaninta da fad'in kada ki zurfafa tunani duk wani abunda kikeyi nasani suwaiba babu abund bn saniba komai kike aikatawa akan idonane,
Advertisement
Cikin tashin hankali wanda tunda hajiya suwaiba take bata ta6a shiga irinsaba sai yau ta dago tana duban hajiya babba tasan hajiya babba sarai bata lamunta a cutarda wani ko yaya kuwa, balle ma idan tasan abunda ta aikata shekarun baya hukuncin mai tsanani ne,
Ga mamakinta sai taji hajiya babba tana fadin da nadauka zakiyi abun arzikine ya sanya ban saka hannun ba nazauna na zuba miki ido jna jira naga abunda zaki iya ashe ba komai zaki iyaba, tunda yanzu labarin yarima ma baya isoki bakisan wani hali yake cikiba,
Da mamaki hajiya suwaiba ke kallon hajiya babba saboda zancenta ya daure mata kai sosai, kiyi azamar rabashi da matarda yake tare da ita idan kinason ganin yayanki kan kujerar sarautar nan, kiyi gaggawar nemo hanyar datse wannan auren banaso lamarin yakaiga saina saka hannuna ne aciki kisamu mafita tunda wuri, dasaur hajiya suwaiba ta amsa cikin jin dadin hajiya babba na gefenta, tashi hajiya babba tayi takoma shashinta tabar hajiya suwaiba da dumbin mamaki, cikin ranta tana fadin masarautarnan sai dai kaga kowa kabarshi kawai saboda hajiya babba babu wanda yakaita kiran Allah da nuna son jama'a da nuna babu ruwanta abaki,
Tunani kawai hajiya suwaiba keyi dama ba ita kadaice keson kallon bayan yarima b dama sunada yawa haka? To ko su nawane haka wannan tambayar ne batada amsarta domin batasan cikin kowaba."
Kuma ta tabbata ba duk wani abunda takeyi hajiya babba tasaniba ta tabbata da tasan wasu abubuwan abun bazai kai iwar haka hajiya babba bata dauki mataki da kantaba."
———————-
Alhamduillah Allahummar rahamni bil Qur'an waj'alhuli imaman wa nuran wa hudan wa rahma, Allahumma zakkirni minhu ma nasitu wa allimni minh na jahiltu aruzuqna tilawatahu ana al laili wa adrafan nahar waj al huli hujjatan ya rabbal alamin sanda yakai qarshen addu'an sannan itama sawwama ta karanta rufe qur'annin tayi shima ya rufe tanajin wani sanyi cikin ranta wani farin ciki takeji wanda tunda take bata ta6a tsintar kanta acikinsa ba,
Miqa mata qur'anin hannunsa yayi yana fadin alhamdulillah komai yayi farko zaiyi qarshe yau sawwamaty ta had'a qur'ani, qur'anan tarteela,
Da fara'a a yalwace akan fuskarta tace nagode, nagode yaya sadam Allah ya biyaka da mafificin alkhairinsa kasamu rayuwata acikin duhu ka maidata cikin haske ka haskakamin rayuwa ka gyaramin addinina ban ta6a tsintar kaina acikin farin cikina irin nayau,
Murmushi sadam yayi sannan yace amin kema harda ke ai saboda kinada dagewa wajjan karatu wasu koyaya za'aso suyi karatun bazasuyiba amma kiduba cikin shekara daya kika hada tarteel na qur'ani Allah yasa mai amfamine,
Amin yaya sadam nagode kaima harda jajircewarka akai Allah yabiyaka, ahankali ya amsa da amin,
Sai abani tukuici,
Tukuicin me kakeso yaya sadam ka cancanci komai, mutuminda yabaka kyautar ilimi ya cancanci duk wani tukuici da za'a bashi,
Kice kina sona shine tukuicina, danna lura dake idanba roqa nayiba baki ta6a fad'amin, rufe fuskarta tayi tace ina sonka yaya sadam matukar so,
Huuuuuuuuuuuuu ya furzarda iska yar dariya yayi sannan yace sawwamaty ansan matuqar so,
Turo bakinta tayi tana fadin da idan ban san matuqar soba waye zai sani, bayan kaima matuqar so din kake nunamin,
Aduk lokacinda taturo bakinta wani kyau takeyi masa yakan samu kansa da kasa daina kallon ta,
Nisawa yayi yace na yadda toh ina nuna miki matuqar so ni yaushe za'a fara nunamin nawa matuqar so d'in?
Kauda maganar sawwama tayi tace yaya sadam yaushe result dinku zai fito?
Murmushi yayi aduk lokacinda zance yafara nauyi ya lurada sawwama kawarda zancen takeyi, bazata yarda aci gababa,
Ummmmm ban saniba ba amma soon in sha Allahu. Allah yayarda yasa muga alkahiri cewar sawwama,
Amin dai ya amsa, yadan dade awajanta kafin yatafi,
Bayan takoma gida baba yace mamana yakamata yanzu sadam yaturo manya su shiga zancen tunda yanzu ai yarigada ya gama karatun idan yazo gobe ki sanar dashi,
Toh sawwama ta amsa a kunyace."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Toh Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial85 Chapters
Beast Cultivating System
A woman felt her life didn't have meaning and was missing something, she envisioned a more exciting future in which she had a goal to achieve.Coincidentally, this came in the form a bolt of lighting which sent her into the newborn body of a spirit beast with True Dragon heritage, into the world of cultivation where the strong eats the weak. Whilst awakening inside an unfamiliar world and body, she was pondering her newfound situation a robotic noise interrupted her thoughts indicating that the beast cultivating system has activated.Bloodline purity? Legendary bloodlines? Talent?Her system can provide it all.Armed with the knowledge of being a race in which is hunted by other beasts for its bloodline or enslaved by other cultivators, she knew the only way to keep safe in this chaotic world is getting stronger.Dragon pic: https://lawrencemann.co.uk/portfolio_page/spitfyah/ I have posted this on web novel; https://www.webnovel.com/book/12432453405442605/Beast-Cultivating-System
8 261 - In Serial18 Chapters
Clockwork powers? Sure! Wait, why am i on a fantasy world?
This story follows an mc that just turned 18, called Mitch. He was a simple guy. Liked his anime liked his hentai, until a God from a another side talked to him and gave him a bribe. God-Sup bitch, wanna work for me? And so he was like. Mc-yeah, why not! You wanna know what the God offered him? Read the title, and if you wanna know the story read the prologue Warning:may contain riches and b*tches in high abundance.
8 157 - In Serial30 Chapters
Subcutanean
Horror // LGBTQ+ // Novel // COMPLETE! ~*~ Insecure college senior Orion loves music, books, and his best friend Niko. But when the two discover a secret basement much bigger than it should be, they're soon trapped in a mirror-world filled with two-faced doppelgängers and long-buried secrets. Most dangerous of all is Orion's consuming obsession: somewhere down there, is there a Niko who loves him back? Subcutanean is a novel from an award-winning game designer, with a unique twist: each telling of the story is unique. No two versions are ever quite the same. The version shared here on Royal Road is version #01893 of the story: find out how to get your own unique copy. CW: This novel has no explicit sex scenes and only PG-13 level violence, but does touch on themes of depression and suicide, so has been marked "Mature."
8 132 - In Serial24 Chapters
Sold To Be His
(Mafia Series#3)He advanced towards me and grabbed my arm painfully. I hissed under his hold and tried to pull my arm away from him but all in vain. "Who are you?" I asked, sacredly. He squeezed my arm which was causing pain in my arm. It would leave a buries for sure. He chuckled darkly and pulled me to him which made me hit with his chest. He quickly moved his hand from my arm to my waist and pulled me impossibly close. I looked at him in uncontrollable fear. I felt his other hand move on my back and felt something pinching on my arm, painfully. I looked at him with wide eyes and tearful eyes which were flowing through my eyes, that were slowly closing."Your future!" I heard him saying in dangerous voice as my eyes were closing without my permission. I tried to open them but failed and let myself sunk in the darkness. - - -Izzah, a beautiful and talented doctor. Always there to help and support anyone in the hours of need.But what will she do when she is sold to a mafia man?Daniel, handsome and dashing mafia man. Who hates lies and don't know the meaning of love.But what will he do when Izzah enters in his life? And why he kidnaps her and bought her?- - -Status~Started: 15/06/2019.Completed: --/--/----.
8 152 - In Serial65 Chapters
In the Sky with Diamonds » s. hyde
"Why do you only call me when you're high?""But I'm always high."that seventies showseason one-season six + epiloguehighest rankings: 1 in 70s 1 in 1970s 1 in hydefanfic 1 in stevenhyde 2 in that70sshow 563 in fanfiction completed 12.31.182017 © an_intellectual
8 96 - In Serial8 Chapters
Cute but Deadly(Tails.ExexFem!reader)
You saw Tails die with your own eyes and ran away while Sonic.Exe killed everyone you known.You come back to defeat Sonic.Exe once for all,but is your best friend really dead?Warning:Language,Maybe🍋, blood, and angst.
8 79

