《ƘADDARAR RAYUWA》QPage 28
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 28
Satinsu sadam biyu suna ibada suka dawo gida yayinda hankalinsa gabaki d'aya yayi wajan sawwama kayanda ya siya mata gabaki d'aya a bag din hannunsa ya ajiyesu bai yarda ya hada abubuwanda ya siya mata dana mummy ba saboda baisan yanda zata dauki lmarin ba,
Bayan sun isa gida hutun kwana daya kawai ya yi yatafi wajan sawwwama ba qaramin murna sawwama tayi da ganinsa ba shima haka ji yayi kamar wanda ya dauki tsawon lokaci batareda ya gantaba aaranar yakai wajan 10:00pm kafinanna yabar wajan sawwma koda tashiga gida sanda baba yayi mata fada sosai, shikam bayan ya koma gida kusan kowa ya shiga daki so babu wanda yasan da rashin dawowarsa,
Bayan sun dawo da 5days ya kawowa sawwama tsaraba sosai ya yi mata siyayya barinma abayas masu kyau sosai harda baba yakawowa jallabiya."
Sadam yaji dadin yanda ya samu sawwama ta maida hankali sosai akan karatunta yayi mamaki domin bayan tafiyarsa da kanta take ta qarawa kanta karatu,
Rayuwarsu tafiya takeyi a kullum qara sabo sukeyi soyayyarsu qara nisa takeyi duk wannan abunda akeyi har yau mummy bata fahimci halinda sadam yake ciki ba."
—————
Nabila tana kula da yarima sosai yanda ya dace sai dai ko kadan yaqi sakin jiki da ita duk yanda zatazo su zauna waje daya dashi tana zaunawa awjan zai tashi tana kula da maganinsa yanda ya kamata duk wani abunda mai martaba yakawo ayi masa bbu 6ata lokaci takeyinsa,
Da safe bayan ta kaiwa yarima abinci babu yanda batayi dashiba yaci ko kallon wajanda take yaqiyi,
Tsayawa tayi tana kallonsa yanda ya kauda kansa gefe, ta6e baki tayi dama tasan bawai zaici bane kawai dai takawo masa ne,
Wucewa tayi izuwa dakinta ta kwanta wani bacci ya dauketa gabaki daya agajiye take jinta, maganar gaskiya ita dai nabila bata saba aikin wahalaba saboda mahaifinta yanada kudi sosai ita dai kawai tanada zuciya mai kyau dakuma hali mai kyaune shiyasa da daura niyyar kulada yarima kuma tanada tausayi sosai,
Sai bayan tayi bacci tatashi sannan tafita izuwwa palour kamar yanda ta barshi haka ta sameshi bai tashi daga wajanda yake zauneba tausayinsa ya kamata, qare masa kallo tayi idan za'a fada maka bazaka ta6a yarda cewa yarima baida lafiya ba kamar yanda mutane suke fadi ciwon hauka, ita bataga wani haukanda yakeyiba, shidai kawai bai magana kuma koda magana kayi bazai ta6a nuna maka ya fahimci mai kace ba ga dukkan alamu kuma baya fahimtar ne sai dai yabi mutum da ido kawai, sai kuma ihu dayakeyi da daddare sa'i-sa'i zaunawa tayi kusa dashi ta dauki abincin takai bakinsa duk yanda tayi ya bude bakin amma firr yaqi,
Advertisement
Tana cikin lallashinsa yaci abincin taji sallamar umma sosai umma taji dadin ganin yanda nabila ta sanya kai tanata lallashinsa miqewa nabila tayi cikin girmamawa tana yiwa umma sannu da zuwa,
Zaunawa umma tayi tana murmushi tana kallonta tana fadin sannu nabila an kwana qlau?
Sunkuyarda kai qasa nabila tayi sannan tazauna aqasan carfet tana gaida umma, amsawa umma tayi cikin fara'a tana fadin sannu da aiki nabila Allah yabiyaki, qasa nabila tayi da kanta sannan tace amin a hankali,
Daukar abincin umman tayi tana fadin yana rigima koh?
Yaqi cin abinci ai haka yakeyi, murmushi nabila tayi ta sunkuida kanta qasa tace umma bayason cin abinci wata rana haka yake kwana baici komai ba,
Murmushi umma tayi tace kada ki damu zanna zuwa ina bashi dama sau daya yake cin abinci arana baya wuce haka sai ruwa,
Eban abincin tayi takai bakinsa a hankali ya bude bakin umma ta sanya masa,
Murmushi umma tayi ta sanya hannu ta share masa gefen bakinsa tana son yaronta sosai hka tana tausayin fiyeda kima,
Sanda tagama bashi sannan ta ajiye tabashi ruwa, nabila ta tsura musu ido cikin tausayi da kuma qaunarsu yanda taga umma na tafiyar dashi kamar wanda batason koda kudane ya ta6ashi ta lura umma nason yarima sosai so maras misaltuwa, son da take masa baya iya 6oyuwa,
Umma tadan dade sannan tayi musu sallama tatafi tanajin nabila ta qara kwanta mata arai,
Washe gari da safe nabila ta shirya taje gaida mai martaba bayan sun gaisa mai martaba yadubeta cikin kulawa yace ina bakida wata damuwa? girgiza kai nabila tayi tace babu komai,
Toh Allah ya miki albarka idan dai kinji da wani abu kada kiji komai ki sanar dani bazanso ki cutu ba,
Jijjiga kai tayi tace in sha Allah,
Daga nan tafita sashin umma,
Bayan sun gaisa umma tace nabila aida baki fito bama zan shigo zuwa jimawa kadan, kada kina fita kina barinshi shi kadai kinji? toh nabila ta amsa cikin ladabi umma tace yawwa Allah yamiki albarka maza tashi kije kutafi da ruma saita tayaki zama zuwa dare, idan kuma kinaso ta dawo sashinku da zama saina sanarda mai martaba saboda Zaman kadaici kada yayi miki yawa,
Murmushi nabila tayi tace aikuwa umma zanso haka saita dawo mu zauna,
Umma tace toh babu komai in sha Allah zan yiwa mai martaba magana,
Ruma datake jinsu cikin murna tace umma dama wallhy ya yarima kullum sai nayi mafarkinsa nima zan fiso nakoma can din."
Haka kuwa akayi da umma taje gaida mai martaba ta shaida masa buqatarta mai martaba baiqiba washe gari ruma takoma shashin da zama,
Advertisement
Da dare yayi taga nabila tashiga daki ta kwanta mai makon d'akin da yarima yake, ruma kamar zatayi shiru sai kuma takasa hakuri tace' anty nabila ba'a d'akin ya yarima zaki kwana ba?
Ba'a cika barinsa shi dayaba saboda cikin dare yana tashi,
Murmushin nabila tayi tace dafarko can nake kwana sai naga kamar ina takurashi saboda bai sakewa har in dai ina wajen shiyasa nadawo nan,
Jijji ga kai ruma tayi ta koma ta kwanta."
Da safe ruma ta shirya tafice zuwa school ba ita tadawo ba sai la'asar.
Haka dai rayuwa taci gaba da tafiya musu amma ko kadan yarima yaqi sabo da nabila fir ko abincin hannunta yaqi ci daga ummansa sai ummansa kadai yake kar6an abinci ko ruma ma sai lokaci-lokaci yake shan ruwan hannunta."
—————-
Bayan dawowar sadam da 1week an shiga satinda za'a koma school mummy ta siya mai mota kamar yanda ta fad'a dama cewa nata gift din sai shn dawo, baqaramin murma sadam yayiba,
Wash gari yakaiwa sawwama tagani, itama tayi murna tayi ta yiwa mummy addu'a sosai yaji dad'in addu'ar ta ga mahaifiyarsa,
Nisawa sadam yayi yana kallon sawwama nutsuwarta ke qara masa soyayyarta cikin zuciya, cikin kulawa sadam yace sawwmaty inaso zaki koma school saboda zamanki haka bawani amfani gareshi ba,
Sunkuida kai sawwma tayi tace ni bazanqi komawa school ba amma kafara tuntubar baba tukunna kaji mai zaice,
Nisawa yayi yace in sha Allah zan masa magana,
Sawwwama inaso kiyi karatu sosai mummyna tana son karatu sosai dalilin karatu ya sanya ta siyamin wannan motar sawwama ki daure kiyi karatu idan bakiyi karatu ba mummyna zata iya rabamu yayi maganar cikin karyewar zuciya,
Dasauri sawwama ta d'ago ta dubeshi cikin tashin hankali tace tarabamu kuma yaya sadam akan karatun? Lumshe ido yayi hadeda jijjiga kansa yace eh mummy nason karatu sosai fiyeda tunaninki,
Shiru sawwama tayi gabanta ya tsananta faduwa saboda bata kawo rabuwa tsakaninta da sadam saboda yanda ta sanyashi aranta,
Ganin yanda jikinta yayi sanyi yasa sadam ganin wautarsa na gaya mata wannan maganar lallashinta ya fara yi da fadin, ki kwatarda hankalinki sawwmaty in sha Allah bbu mai rabani dake idan bakiyi karatu ba nace kuma ni zan zauna dake ko ayaya ina sonki,
Bazan ta6a bari arabamu ba in sha Allah zamu kasance atare,
Qaqalan murmushi sawwama tayi amma hankalinta duk yabi yatashi."
Bayan ya tafi haka yabarta da tunanun wannan abun cikin ranta,
Haka takwana da tunanin washe gari da safe kafin baba yafita sawwama taje ta sameshi noqe-noqe tafarayi takasa fada masa, kallonta yayi gar zai fita sai kuma yaja ya tsaya yana fadin mamana akwai wata magana ne? Bakinki yanason cewa wani abun, sosa kai sawwama tayi takasa fadawa baba, sake baron yayi ya isa kusada ita yana fadin mamana lafiya kuwa? Wani abunne yafaru?
Girgiza kai sawwama tayi yace to menene mamana,
Kanta yana qasa tace baba dama inason komawa makaranta ne idanda hali idan kuma babu saina hakura babu komai,
Murmushi baba yayi jin kalamanta akowani irin zance takanyi amfani da kalaman nutsuwa da hankali,
Kijira idanna dawo mamana zamuyi magana in sha Allah komawarki makaranta bazata gagarba,
Godiya sawwama tayi masa sannan ta yi masa adawo lafiya."
Da sadam yazo ta shaida masa cewa baba ya amince yace zai nema mata makaranta wacce zatana zuwa,
Murmushin jin dadi sadam yayi yace shikenan baki jira na tambayeshi ba shine kika tambayeshi da kanki?
Tura baki sawwama tayi tace bakaine kace za'a rabamu ba shine na fada masa dakaina,
Murmushi sadam yayi yace ai nace miki bazan ta6a bari arabamu ba ko?
Qara tura baki sawwama tayi tace naji tsoro sosai,
Murmushi sadam yayi yana kallonta yace sawwamaty yaushe kika kamu sosai ne haka?
Rufe ido sawwama tayi tace nima bansaniba,
Murmushi sadam yayi kunyar sawwama tana burgeshi komai awajanta kunya ne,
Nisawa yayi yana qara jin sonta a furzarda iska yace akwai school a islamiyanku tayi miki?
Zaro ido sawwama tayi tace yaya sadam ta islamiyarmu fa makarantar kud'i ce,
Uhum nasani ai tayi miki?
Gyada kai sawwama tayi shikenan, kawai yace bai qara cewa komai ba."
Cikin qaramin lokaci yasamawa sawwama admission a ss1 amma a 3rd term ake ahaka aka bata admissin tafara zuwa,
Yayinda shikuma sadam suka koma school ya shiga shekararsa ta karshe,
Ahaka rayuwa take ta tafiya mawa sawwama da sadam cikin so da kaunar juna, ahaka su sawwama suka shiga SS2 shikuma sadam yana first semester d'insa na final year."
—————
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Toh Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial935 Chapters
Dual Cultivation
Su Yang is a powerful Dual Cultivator who was imprisoned after he offended the Heavenly Emperor.
8 213 - In Serial47 Chapters
Godslayers
In the ancient, brutal days, the Eifni Organization reached heaven through violence and tore the gods from their thrones. Now their methods are more precise. Etheric technology allows them to measure love, create beauty, and reincarnate the souls of the dead into new bodies. By embedding specially-trained operatives—godslayers—into a culture, they can create the exact conditions to kill a god and save the souls it would otherwise devour. Lilith was a run-of-the-mill college atheist until a divine being took a bite out of her soul. Rescued by the Eifni Organization, she signed on as a godslayer. Now, after years of training, she's deploying on her first real mission to a planet called Theria. Objective: perform reconnaissance on the local pantheon and clear out as many of the gods as they can before the strike team arrives. There's just one problem: the Therians seem to know they're coming. Godslayers is a story about intrigue, meaning, and people being too clever for their own good. Updates Tuesdays and Fridays.
8 214 - In Serial21 Chapters
Impera
Gaius is the Emperor of The Roman Empire, that is one of his own creation in Impera. Ruling a massive empire, Gaius does what no other ever managed, uniting the entire world under the imperial banner. Hailed as the World Conqueror, a series of events unfold such that Gaius is forced into a world shaped by his past actions. He will face the true burdens and benefits his position awards, embarking in a struggle far beyond his worst nightmares. In his journey, Gaius will understand what truly means to be an Emperor, and what it takes to rule.
8 167 - In Serial23 Chapters
The Journey of The Three Immortals
"Haha,Good luck working together,kiddos."A middle-aged man waved his disciples goodbye,while being cursed at by the three disciples falling to their "doom".The three siblings,rivals,all residing in one body,and having to take care of a brat. How can they work together despite fighting at the most trivial of things?This is their story.Warning: Mature content , Xianxia, Obscenities , Multiple POVs , Gore , OP MC , Personality switch , A lot of dark humorThis story may have romance(Straight or BL) in it, but definitely not harem.---------------------------------Hello, this is Chaifoo and this is my first attempt at writing a novel.I may not be able to update daily due to my busy school days, but I hope you will enjoy this novel. If you could, please give me some suggestions and advice based on the novel.Thank you!
8 126 - In Serial6 Chapters
Would you like to continue?
*"Damn, not again where did I go wrong?", Durante Martins wondered. "The man surely said the prize is in one of these 49 suitcases and I've opened 47 already and no matter what I still lose. I'm starting to think this games rigged or something. *Durante Martins, your classic 17 year old who has only lived for like 112 years. How? With countless do overs of course follow Martins on his journey full of comedy and drama.
8 184 - In Serial29 Chapters
Apartment Below- Partly Dialogue ✔
Highest ranking #40 in short stories(Unedited)"I have hung up on you twice already. Don't you understand that I do not have time for you to complain about the fact that you have to clean your room Elizabeth?!""I am not Elizabeth. I just called to ask you a question-""Well I do not have the time to talk too you either."----When a boy calls the girl above and keeps calling.
8 133

