《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 27
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 27
Bayan maganar da mai martaba yayi da amintattunsa washe gari da safe d'aya daga cikinsu yasameshi akan ya amince da a aurawa yarsa ma yarima, tara sauran dukansu mai martaba yayi ya ya tambayesu yaji shawararda suka yanke, babu 6ata lokaci sukayi muhawara atsakaninsu suka shaida masa akan wanda yafara shaidawa mai martaba ya amince yarsa yarima zai aura saboda su dukansu sun amince amma idan akayi la'akari duk cikinsu shine yafara amincewa, cikin fahimtar juna sukayi taro suka watse,
alokacin mai martaba ya shaida mawa mahaifin yarinyar cewa akan za'a kawo komai da akeda buqata cikin qanqanin lokaci yakeson auren nan da sati daya sannan ya shaida masa akan baya buqatar wani shagali duk qanqantarsa a bikin koda su sa lalle da komai bayaso a daura aure mahaifinta ya rako amarya d'akinta,
Bayan sun gama yanke shawara mai martaba ya sanya aka kira umma ya shaida mata mahaifin yarinyar galadiman garin kennan da kuma yanda sukayi dashi ya shaida mata nan da 1week yake buqatar auren umma tayiwa mai martaba godiya sosai saboda yanzu hankanlinta ya kwanta da zancen aurenda mai martaba zaiyiwa yarima saboda yanda taga jikin yarima yana samun sauki sosai,
Bayan umma tafita ta sanarwa ummi yanda sukayi sannan ta ce ahado lefe cikin qanqanin lokaci saboda kudi ta turawa ummi hado lefe kaya ma sha Allah sunyi kyau sosai akwatunane set biyu guda sha hudu masu kyawun gaske da kaya masu tsadar gaske,
Ba'akai lefenba cewar umma idan tazo gidan za'a kai mata kayanta sashinta,
Har daurin aure yarage saura 3days babu wanda yasanda zancen auren acikin masarautar
Duk yanda hajiya suwaiba takaiga son jin wani abun gameda yarima bata samuba saboda ta fannin mai martaba babu wani information dayake fita,
Sai ana gobe daurin auren kafin mai martaba ya sanar,
Wannan zance yazowa mutane ba bazata barinma hajiya suwaiba wacce taji zancen kamar sauqar aradu,
Tashin hankali tashiga sosai irin yanda taji zancen tunaninta daya kodai yarima yasamu lafiyane dahar za'ayi masa aure,
Duk yanda taso samun wasu bayanai abun ya faskara har y'ay'anta ta sanya su naima mata wani bayani ko zasu jiyo daga wata majiya amma babu,
Advertisement
Abunda hajiy suwaiba bata saniba yanzu duk wani abunda ya shafi yarima saninsa yakoma daga mai martaba sai umma atsakaninsu suke duk wani abunda ya shafeshi,
Aranar takira yaya hadiza kafin ta iso ta kirata awaya yafi sau goma dan gani takeyi kamar ba isowa zatayiba,
Tana isowa hajiya suwaiba ta shaida mata halinda ake ciki, cikin tashin hankali tace ni bansan koya samu lafiya bane har zancen takaiga yin aure, bansan wani hali ake cikiba yanzu banda wani bayani akansa,
Shirya yanzu zamu fita tare dake dan yanzu bazan iya zamaba, sam zama bai kamaniba har in dai bansan halinda ake cikiba,
Cikin qanqanin lokaci suka shirya suka tafi tareda salim yaya hadiza takaita wajen wanda tafi yarda da aikinsa, ya shaida musu cewa yarima bai samu lafiya ba kawai dai za'ayi masa aurene saboda su kauda hankalin jama'a kuma yanada tabbacin bawai zama matar zatayiba saboda haukarsa gaba takeyi ya tabbata babu mai iya zama da mahaukaci, haka dai yayita gaya musu magana sannan yabasu wasu abubuwanda zasu qarayi saboda dawwamarda yarima a halinda yake ciki,
Hajiya suwaiba ta karbi iya wanda zasuyi amfani dashi ma karan kansu sannan ta shaida masa yarima basuda wani contact dashi babu mai iya shhiga sashin ya aikata masa wani abun, maida maganinsa yayi yace kubar wannan awajena yanzu dai abada abun yanka tukunna zakuga aiki,
Kudi hajiya suwaiba tabasu wanda ita kanta batasan iya yawansu ba tayi masa sallama suka wuce,
Cikin mota salim sai kwafa yakeyi cikin zafin rai yake fadin ammah tun farko dakin bani dama da yanzu tarihim wannan yaro yaqare amma kullum sai ace ba yanzuba ba yanzuba, yanzu wa gari ya waya? Da yanzu abu bai kaiga 6aci hakaba,
Ammah batace masa komaiba saboda tasan irin zuciyarsa kuma tun a baya itake tausarsa take hanashi aikata nufinsa sai yanzu take dana sanin tsaidashi a wancan lokacin datayi, da yanzu komai yadawo labari da rayuwar haliifa adoron kasa tadawo tarihi,
Bata iya ce masa komaiba har yayi abunda zaiyi ya ja bakinsa yayi shiru,
Ita kuwa yaya hadiza shiru tayi tana jinsu kawai dan bataso hajiya suwaiba ta biyota da kanta ba saboda tana samu sosai aduk lokacinda ta aiketa,
Yanzu kuwa tasan bazata samu komai ba saboda tasan hajiya suwaiba idan bukatarta zata iya kashe ko nawane amma banda haka kawai tadauki kudi tabaka bazata ta6a hakanba,
Advertisement
Tana jinsu har su har yagama bambaminsa sannan yayi shiru ya maida hankalinsa akan tuqin har suka isa kuma babu wanda yaqara tankawa."
Washe gari da safe mutane suka shaida daurin auren yarima haliifaaa da amaryarsa nabila akan sadaki 500k naira dubu dari biyar,
Duk da bikin ba'ayi wani taro ba amma yadan tar jama'a itama umma nata wajen yan uwanta sunso suzo amma ta hanasu tace daga baya sai suzo suga matar dan bataga amfanin zuwannasu ba,
Da dare kuwa mahaifinta ya sakota a mota driver yana jansu har sashin mai martaba ya kawota,
Bayan isowarsa tun amota yakeyi mata nasiha akan ta zauna lafiya da mijinta sannan ta kula dashi tsakani da Allah tasani cewa shi aure bautane sannan shi yarima mijine a wajanta kada taganshi baida lafiya tace zata rainashi kokuma taqi yimasa biyayya ko ahakan data ganshi yana sama da ita kuma yazama dole tayi masa biyayya,
Nasiha sosai ya ringa yimata ta sunkui da kanta nasiharsa tana shiga kanta,
Yana kaita har palourn mai martaba suka gaisa da mai martaba yayi masa sallama yatafi,
Ba'a dade da kawota sashinba umma ta iso, sosai mai martaba yayi mata nasiha sannan ya umurci umma data kaita wajanda yarima yake,
Riqe hannunta umma tayi ta nufi wata qofa, tana bude qofan tashiga palour ne mai kyawun gaske da kujeru set biyu aciki daya gefe royal chairs ne daya gefen kuma turkish chairs,
Falon yayi kyau sosai sai d'akuna da suke ciki guda uku,
Tsayawa umma tayi a palour d'in ta sanya hannu ta daga gelen nabila hadeda daura mata shi akayi, sanya hannu tayi ta d'ago ha6anta ma sha Allah ta furta a fili nabila kyakkyawace sosai ga kamala da nutsuwa akan fuskarta, cikin jin kunya nabila tayi da kanta qasa,
Kamo hannunta umma tayi tace nabila nabaki amanar yarima dan Allah ki kularmin dashi kamar yanda uwa zata kulada danta, in sha Allah nabila ta furta a hankali, wata qofa ta nufa ta bude tashiga da sallama, yarima haliifaa dake zaune bakin gado ya juyo ya dubesu, ahaka idan ka kalli yarima zakace bbu wani abunda yake damunsa dan komai nashi a kimtse hattada kayanda yake jikinsama sabbi ne, ido ya zuba musu har suka qaraso wajansa zaunarda ita gefensa umma tayi tadubi yarima tace haliifaa na ga nabila nan nakawo maka, matarka ce kaji, ido kawai ya zuba mata harta gama bayaninta tayi musu sallama tafita,
Kallo nabila ta qarewa yarima tsaf mutum har mutum cikakke mai kyawun gaske amma rashin lafiya ta maidashi mutum mutumi, tausayinsa yayi mugun kamata, tadaura aniya aranta zata kula dashi har ranarda zai samu lafiya."
———
Sadam sunata shirin tafiya bai fadawa sawwma har sanda komai ya kammala ranarda kuwa daya fada mata tayi murna sosai amma sai dai taji batajin dadin rabuwarda zasuyi nadan wani lokaci batajin zata iya jure rashin ganinsa na wannan lokacin shima kansa sadam nasa wurin hakene yana daurewane kawai amma yana tunanin halinda zai shiga a dan wannan lokacin."
Ranar litinin jirginsu yatashi zuwa saudia,
Kwanansu uku acan sadam yadamu sosai sai yanzu yaga rashin azancinsa narashin saya mata waya dabaiyiba yasanda cewa idan yaji muryarta koda wani abunne zai rage masa,
Haka dai duk babu dadi yawan ibada da sukeyine ma ya sanya wasu lokutan baya samun lokacin tunanin
Sau dayawa addu'oinsa bai wuce akanshi da sawwma ba, har mummy sanda yaringa sanyawa cikin addu'arsa saboda itace yake kallon zata bashi matsala a aurensa da sawwama,
Itama sawwama awajanta tanajin jiki sosai na rashin sadam a d'an wad'annan kwanakin, kullum cikin irgen kwanakin dawowaraa takeyi kamar yanda ya shaida mata cewa 2weeks kawai zasuyi yanzu a lissafinta 9days kenan da tafiyarsu."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Toh Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial154 Chapters
Into Nothing
Rewrite in progress. 10/11/2021 10/18/21 school sucks 😔 Wow, I forgot about the whole wait for approval thing. Whoops.
8 157 - In Serial18 Chapters
The Cracked Earth
Chris had played more than his fair share of games, yet with the advent of the dive gear he hadn't found anything that caught his interest. It was while he was looking for time to kill that he discovered The Cracked Earth. Before he realized it he was already in the game. He set off on a journey that would be unforgettable. From the lush continent of Faran to the player-killer heavy lands of Ghandahar, he will face trials he could never expect. And in the end he will be faced with the true purpose of the game.
8 120 - In Serial28 Chapters
Warfare Between Lost Hearts
During the long awaited war crisis in Manila, every legal-aged inhabitant, specifically voters, are required to work for the government in order to reestablish the living land and battle against a mass terrorist attack. The country where the terrorist originated are still in the unknown and under further research. Juveniles haven’t got any choice yet to live by themselves. Building a town, planting food crops, hunting animals and even manslaughter is required in the generation by means of survival. Keisha and his brother, Jaden, are left alone haunted by vicious brutes hiding from the shadows. Until then they found hope wherein they can rule over and persist the ongoing catastrophe.
8 210 - In Serial18 Chapters
Tales of a main character
The story of a main character who breaks the 4th wall too many times. Doesn't co-operate with the author. Is Unfunny and gives too many philosophical thoughts and trivia.
8 250 - In Serial17 Chapters
Alzholme
Alzholme, the city of the heavens, a refuge for the lost of a dead world. Within the domed city-station, several species exist together at once. A tentative peace is maintained through the order of the city after a civil war only 20 years ago. Within the lowest parts of the city, the massive forest known as The Megaden, a conspiracy stirs to upset the peace...-------Saul is a detective working for the Merchant's guild. After hearing that several crates of goods have been smuggled out of the upper section in the dead of night, he's sent on assignment to the Megaden in order to find out where this all leads. Along the way he teams up with a local and a member of the Maskless, the Erudine secret judicators.Twenty-Two, a mysterious mercenary works with two humans in the Megaden. Their purpose is to research the ancient ruins and technology found within the forest. As they explore the abandoned buildings, they find themselves brushing odds with the unknown history of the city and the powers in charge of the Megaden itself.
8 156 - In Serial6 Chapters
What if? Ayanokouji of Class C
I'll try and make ayanokouji act like he does in LN and will change a bit of the story such as the manabu confrontation and sudo case and all because he in class c.
8 130

