《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 26
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Page 26
Tun ranarda wannan abun yafaru kullum kwanan duniya yarima saiya tashi cikin dare yayita wannan kuwwa da ihun, mai martaba yana iya qoqarinsa wajan yimasa addu'oi to Alhamdulillahi dai abun yaragu, yanzu ba sosai yake tashiba sai sa'i-sa'i,
Dake kullum mai martaba yakan yi masa addu'a cikin ruwa addu'ar tazama itace ruwan shansa akowani lokaci,
Lokacinda labarin komawar yarima sashin mai martaba ya riski hajiya suwaiba sanda tayi y'ar qaramar hauka,
Sumbatu ta ringayi da fad'e-fad'e tasan yanzu batada wani contact da yarima,
Duk yanda zatakaiga son cutar dashi hakan bazai yiwuba saboda amintattun mutane ne atare a sashin mai martaba wanda zasu iya bada rayuwarsu akansa, batada wani hope yanzu,
Hajiya suwaiba tarasa mai yake mata dad'i da ta yanke shawarar bazata qara tuntu6ar yaya hadiza ba amma yanzu batada wata mafita daya wuce wajanta,
A waya ta kirata ta shaida mata cewa tana son ganinta, yaya hadiza tana kallon kiranta tasan tatsuniyar gizo bata wuce ta qoqi, hajiya suwaiba bata ta6a nemanta har sai idan tana neman wani abun a wajanta, cikin rawar jiki yaya hadiza ta shirya zuwa wajan qanwartata saboda a wannan aikenda takeyi mata ba qaramin samu takeyiba,
Bayan tazo hajiya suwaiba ta shaida mata duk wani halinda ake ciki,
Aikuwa yaya hadiza batayi qasa a guiwa ba ta amshi kud'i ta tafi tsubbace-tsubbacensu, taje wajan mutane sunfi biyar kowanne idan taje shaida masa takeyi akan yayi aiki batareda an basu wani abu su aikataba saboda basuda contact da wanda sukeson aikatawa lamarin,
Abubuwa dadama yaya hadiza ke amso musu, takan kawo suyi amfani dashi
Sannan kuma da kwanaki kadan suke bayarwa suke tusa aikinsu, suyi su qara basa daukan lokaci sai sunyi shirkansu son ransu,
Awannan lokaci yanda suka dage kan wannan abun badan Allah yasa mai martaba yana tsaye akan yarima ba da yarima bazai qara wani lokaci araye ba,
Addu'a mai martaba yakeyi ba dare ba rana dama kuma addu'a sabonsa ce ba ciwoma bare kuma da ciwo,
Kullum da safe umma ke zuwa tana dubashi takan d'an dauki lokaci wajansa kafin tadawo, idan taje sai dai ya zuba mata idanuwa kawai yayita kallonta babu baki bai iya furta koda kalma d'ayane, sai dai ido,
Rana dai-dai ne idan umma tadawo daga wajan yarima bata zubda kwalla, wani sa'in tun awajansa take zubda kwallar tausayinsa,
Itama umma bata zaunaba addu'a takeyi sosai tad'age da addu'a fiyeda na kowani lokaci,
Mai martaba yanzu zancen auren yarimane kawai agabansa ya tsaya yana son nema masa mace mai nagarta wacce zata kula dashi acikin yanayinda yake batareda ta cutar dashi ba koda na misqala zarratin."
Advertisement
—————-
Mummy data koma gida jikinta yayi sanyi sosai maganar gaskiya kuma magana d'aya itace bazata ta6a barin sadam yayi aureba batareda yayi zurfi akaratu ba, ita kanta abidan nawa take? Bare sadam shi da yake namiji,
Mummy tagama zancenta ita kadai ta shanye acikinta bata bari dady yajiba bare sadam,
Tasan halin dady yanzu abune mai mugun sauqi yace yanajin kunyan yayanta zai yarda ayi auren,
Cire komai tayi cikin ranta saboda tasan baza'a ta6a yiwa sadam aure batareda amincewarta ba tafara tunanin irin kyautarda zata yiwa sadam na cin jarabawarsa da yayi."
Sadam yakaiwa sawwama result dinsa tagani sosai tayi murna da result dinsa har mamakin yanda ta nuna farin ciki yakeyi,
Tsura mata idanuwa yayi yanda fuskarta ta yalwata da fara'a sai tayi masa kyau sosai,
Daura idonta tayi akan fuskarsa idanuwansu ya hade waje d'aya kunyace ta kama sawwama ta sunkuida kanta qasa tana murmushi,
Numfashi ya furzar mai d'umi soyayyar sawwama takansa wani lokaci yaji qirjinsa yayi masa nauyi,
Shi kadai sai yayita ajiyar zuciya d'abi'unta da halayyarta ke dad'a sanyawa soyayyarta tana daduwa cikin zuciyarsa sannan soyayyarta tayita fusgarsa aduk lokacinda yake tare da ita,
Lokuta da dama Batareda sanin saba yake tsura mata idanuwa yakan tsinci kansa da kallonta sannan kuma saiya kasa dauke idanuwansa daga kanta,
Komai nata cikin nutuwa take yinsa, hankalinta yafi qarfin shekarunta, ajiyar zuciya ya qara saukewa yana jin yanda zuciyarsa tayi nauyi tacika da soyayyarta,
Dubanta yayi cikin so da qaunarta yace sawwamaty na kawo miki result kin gani kin yaba amma baki bani tukuiciba,
Kinsan idan nine kika kawomin abun farin ciki haka bazan iya barinki batareda nabaki tukuiciba,
Shiru sawwama tayi batasan mai zata bashiba tasan batada wani abunda zata bashi komai yana dashi arayuwa,
Sunkuida kanta qasa tayi jikin sanyin jiki tace to mai kake so?
Kagani banda abunda zan baka komai kana dashi,
Murmushi yayi yace kene kuwa kike da abunda zaki bani,
Menene shi? Ta tambaya cikin sauri sannan tadaura da cewa Kafadmin har indai baifi karfinaba bai kuma sabawa shari'a ba nayi alqawarin bakashi babu abunda kafi karfinshi aguna,
Murmushi yayi yana jin muryarta mai sanyi tana ratsa kunnensa da gabobin jikinsa izuwa kowani bargo dake cikin jikinsa,
Lumshe ido yayi yace baifi karfinkiba sawwamaty bai kuma sabawa shari'a ba,
Tukuicinki shine ki furtamin kina sona,
Cikin jin kunya sawwma ta sanya tafin hannunta ta rufe fuskarta tana y'ar dariya,
Murmushi yayi hadeda lumshe idanuwa yasake budesu akanta, ajiyar zuciya yasauke a hankali hadeda furzarda iska mai zafi, ya tabbata yana yiwa sawwama so mai tsanani shiyasa yake ganin komai nata kalan burgewane dashi komai tayi abun yakan zama ya burgeshi hadeda kuma wani salon daukar hankali babban abun shine nutsuwarda take tattare dashi,
Advertisement
Ehem am all ears 👂 ina sauraronki,
Jikin jin kunya sawwma tace ai basaina fadaba kasan inayi,
Uhm-uhm naki wannan wayon adai fadan naji da kunnena,
Sanya kanta cikin hijabi tayi akanhanki yanda zai jiyota da muryarta mai dadin gaske tace" ina sonka yaya sadam, cak sanda numfashin ya tsaya na wani lokaci jikinsa kamar wanda aka zare masa kuzarinsa kawai yazama wani statue saboda yanda kalmar da dukeshi sosai ta shige ta samu mafaka cikin zuciyarsa ta maqale garin shiga cikin zuciyar harta zare masa kuzarinsa na wani lokaci,
Jin shirun yayi yawa ya sanya sawwama tafito da kanta ta kalleshi,
Ganin yanda ya zuba mata idanuwansa masu ruwan kyau ya sanyata turo bakinta cikin shagwaba tana fadin yaya sadam kaifa kasanyani fada kuma ka tsaya kana kallona,
Runtse idonsa yayi hadeda fadin ya Allah bude idon yayi akanta yace ai nakasa aikata komaine gabaki d'aya kalmar tatafi mun daduk wani kuzarina,
Rufe fuska sawwama tayi tana dariya, murmushi yayi yace matana badai kunyaba, kunyarki kadai takan dad'amin soyayarki cikin zuciyata,
Qara sunna kai sawwama tayi cikin zuciyarta tana jin dadin yanda sadam yake yabon duk wasu halayyarta duk da kasancewar wani lokacin sai taga kamar kawai yana fadane amma duk da hakan tanajin dadi acikin ranta aduk sanda ya yayabi halayenta,
Sadam yadade wajan sawwama dan har 9 tawuce kafinnan yatashi zaiyi mata sallama har sunyi sallama ya dubi sawwama yana fadin sawwamaty bazaki qara fad'aba kinga ba sau daya kika fada, kuma kamata yayi ace duk wani course nasa fadan dabanne,
Murmushi tayi tace toh ina sonka dasuari tayi cikin gida tana gama fadin hakan,
Y'ar dariya sadam yayi kawai yanda tayi tafiyar dasauri kamar wacce tayi laifi shine yabashi dariya,
Ajiyar zuciya ya sauke yawuce yayi gida dan kada ya karya dokan dady dayake bi masa baya abun kuma bazaiyi ddi ba."
Sadam ya dage da koyawa sawwama karatu sosai yadage akan ganin tasamu wadataccen ilimi wanda ita kanta zatayi alfahari dashi, dan ilimi shine mutum ko aikin mai ilimi da maras shi ba d'aya bane,
Yanason macenda tasan addini hakan yasa zai dage wajan ganin sawwama tayi karatun addini fiyeda tunani,
Wannan shine son gaskiya sadam yana son mace mai addini hakan yasa yafara qoqarin maida sawwama tazama daya daga cikinsu bawai yarabu da ita dan batada dashiba ya nemi mai shi wannan ba soyayyayr gaskiya bace,
Har in dai kanason abu da gaske wanda kake dashi yakamata ka gyara yazamana yadawo irin yanda kakeso bawai dan wanda kakeso bai dashi ba nemi wani maishiba,
Wannan shine ake kira soyayyar gaskiya mugudu tare mu tsira tare kamar yanda yakeson tsira wajan ubangiji haka yakesonmawa sawwama shiyasa yadage sosai kuma Alhamdulillah ko ayanzu sawwama tasan abubuwa dayawa bayan wanda ake koya mata a school harda wanda shi kansa sadam yake daura mata kuma ya lura tanada sanya kai sosai wajan neman ilimi kuma Allah yana shige mata gaba al'amuran suna zuwa mata da sauqi."
——————
Lokacin satinsu sadam uku da gama exam alokacin yake sanya ran zaiyiwa sawwama maganar komawa makarantar boko,
Mummy kuwa tana ta shirya suprise dinda yakeson yiwa sadam amma sai dady ya rigada dan ya shaida mata ya biya musu umra su uku itada sadam da shi,
Mummy tayi murna sosai nan ta sanarwa sadam shima yayi murna sosai,
Mummy ita tabar tata kyautar sai bayan sun dawo dayake tafiyar tasu bazata wuce nan da 1week ba."
—————
Cikin amintattun mai martaba ya duba ya qara sabar wanda ya yarda dasu aciki kiransu yayi ya shaida musu cewa acikinsu yanason wani yabawa yarima auren yarsa, amma baiyi musu doleba yace tunda sun san lafiyar yarima so idan wani aciki yaga zai iya sai ya bada,
Yarda dasu da yayi ya sanya ya za6esu cikin wanda zai nemowa yarima auren d'iyarsu, kuma koda yarima yanada lafiya idan bawai shi da kansa yaga macenda yakesoba toh acikin yayansu zai nemawa yarima aure, yabasu lokaci suyi shawara saboda baison auren yawuce sati d'aya zuwa yamma yace su fada masa idan da wanda ya amince."
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Toh Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial106 Chapters
BROKEN CHAINS
A young orphaned street child and thief stumbles head first into a world of cultivation. She uncovers her bloodline and follows the path of cultivation.This is the story of Yun Kou, how she climbs her way up this cultivation world, filled with powerful clan's, Wild Spirits, Demons and Beasts and cultivation sects. Many tropes of common cultivation novels are used.But there won't be any cheats.
8 206 - In Serial58 Chapters
Primordial Majesty (原始神)
Among the countless stars, at the highest level of nirvana, there was mystical place known as the Jade Heaven Land. As the grand Imperial Commander of Heaven, Shen Qin was worshiped for his cultivation talent and tremendous achievements in the paths of Dao; being one of the guardians who maintained order in the immortal plane. However, on a certain fateful night, in order to chase down and eradicate an ancient god who had heavily sinned, Shen Qin had to pay an immense price and was thus, godly wounded. With his life hovering between immortality and eternity, the will of life inside his tranquil heart, which had been tamed through millenniums, began to once again burn fiercely… Schedule for now: N/A My blog at https://ninedream.wordpress.com/ Support my novel on Patreon! https://www.patreon.com/ninedream Status: Ongoing, Active
8 198 - In Serial6 Chapters
Tales of Heroes and Demons
Every great story begins in tragedy…A story of true heroes, forged through hardship…A story of a world thrown in turmoil…A story of heroes, battling the forces of evil…However, every great story has a humble beginning.In the Ancient Times, the world was in turmoil. Only through the efforts of a martial hero, wielding the Flaming Medallion and the Heavenly Sword, was the Dark Lord slain.Now, eight hundred thousand years have passed…Yang Jing, a disciple of the Order of Heaven, dies on a mission. However, he finds no rest after death. Reincarnating into the body of Cheng Yuan, a mere mortal, will he recover his martial prowess, or is there a deeper meaning to his reincarnation?Will he answer the call of a world thrown into turmoil? To follow in the footsteps of those before him, and defeat the Dark Lord once and for all? [Remake of my older story 'The Sage and the Sword' with a number of important changes and revisions.] Cover: From Pixabay, website for sharing copyright free images. Design: From Canva.
8 78 - In Serial27 Chapters
Corinth
This is the story of an expanding empire, not understanding its reach, unfulfilled by its goals, and misled by its gods. It follows a group of travellers as they try to expand the empire, and probe the edges of its control. It is set in a world in which power is directly connected to origins, ancestry, and the gods of a culture. It examines the effects of conflict on a people when they can’t be disconnected from their surroundings, and thus true mobility is not possible. The first book will be focusing on a group trying to explore and settle the lands east of their empire. Deciding that a new push is needed, groups are being funded to take and farm the near-empty land, and this group of four is heading out ahead of many of the settlers. The four - Sojo, Mirrel, Eyn, and Brehen - hope to find and chart something of importance in a vast, nearly unexplored landscape, and bring the knowledge back to make their fortune. This story will be focusing on the people that make, inspire, and ultimately shape the course of an empire's ambitions. It is hosted at https://thecorinthianman.wordpress.com/ and updates Wednesdays.
8 80 - In Serial6 Chapters
resources-
a book of resources, including face claims, where to find good pictures, and what programs to use for graphic design
8 593 - In Serial53 Chapters
Bad Boy
Emily Nolan is the 16 year old daughter of Marcus Nolan alpha of Sapphire pack and goes to Andrew's high school she lives the perfect life until a certain boy crosses her path.
8 105

