《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 25
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on "
Ina alfahari dake antyna, ina matuqar alfahari dake Allah ya sanyaminke a aljannah ya biya miki buqatunki na alkhairi, Allah yasaka miki da mafificin alkhairi, *ANTY RASHIDA*(mrs mustapha)."
Alkhairin Allah yakai miki aduk yanda kike XEECUL🥰 wannan shafi sadaukarwane agareki."
Page 25
Wuni zubur haliifaa yayi yana bacci bai farkaba, miqewa umma tayi akaro na biyar tashiga d'akinsa domin dubashi,
Ajiyar zuciya tasauke ganin yanda yake baccinsa cikin nutsuwa,
Ahankali ta fito ta rufo da qofar saboda kada qaranta ya tasheshi,
Zaunawa tayi tana fadin yau dai yarima haliifa bacci yaketayi gabaki d'aya wunin wannan ranar,
Ummi dake zaune agafe tace" jikin haliifa kam yanzu abun sai godiya kullum lafiya yake samu Allah yaqara masa lafiya,
Amin umma ta amsa zancen y'ar uwartata cikin jin dadi."
————-
Har dare ya farayi hajiya suwaiba tana jiran taji labari akan jinyar yarima amma shiru babu wanda yakawo mata wani labari gameda hakan,
Aikawa tayi aka kira mata jakadiya, bayan tashigo ta tsugunna ta kwashi gaisuwa tayi shiru tana jiran jin dalilin kiran,
Hajiya suwaiba tadauki lokaci kafin tace bakiji wani abun gameda shahsinsu haliifaa ba??
Cikin ladabi jakadiya tace har yanzu babu wani abunda naji,
Jijjiga kai hajiya suwaiba tayi tace shikenan zaki iya tafiya, amma kina jin wani labari ki tabbatar kinzo kin sanar mun,
Toh ta amsa sannan ta fita,
Tsaki hajiya suwaiba tayi tana tunanin anya kuwa wannan abun yaya hadiza zaiyi aiki?
Itafa daga yanzu ta rigada ta yankewa kanta shawara babu wani jira da zata qara yi zata aikata abunda take kallo shine mata mafita,
Zata bawa salim dama yayi aikinsa kokuma ita tayi aikinta."
———————
Bayan isha'i umma ta dubi ummi tana fadin kinga har yanzu yarima bai farkaba gashi kuma baici komai ba yau through out, ummi ce tace" toh ko za'a tasheshine abashi abincin saboda cikin dare kada ya farka,
Miqewa umma tayi tace toh barina gwada tashinsa kinsan shi dole saiya yi niyya kafin yake kar6an abincin Allah yasa yayarda,
Qarasawa tayi cikin d'akin agavan bed din ta tsaya ta sanya hannu ta ta6a shi temperature d'insa normal, d'an bubbugashi tayi amma shiru bai miqeba taqara bubbugashi still baiyi motsiba, hannunta takai dai-dai saitin hancinsa ajiyar zuciya ta sauke jin yanda numfashinsa yake fita a hankali, rufo masa qofar tayi ta dawo saboda taga yanda yake jin dadin baccin,
Tsakar dare umma tana kwance a d'akinta taji wani irin qawa had'eda kuwwa,
Advertisement
Arazane ta miqe tana fadin inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un wanna wace irin qarace haka?
Yarimane ya fad'o mata arai da sauri ta sakko da kafafunta daga kan gadon, hijab tadaura akan doguwar rigarta tayi waje,
Duk illahirin mutannenda suke sashinta kowa ya fito, tareda ummi suka qaraso wajan cikin tashin hankali tayi hanyar dakin yarima,
Sauran masu aiki da suka tsattsaya a qofar kowa yana taraddadin shiga suka buda mata itada ummi suka shige d'akin kai tsaye,
Da gudu da qarasa ganin yanda yake wata irin qawa yana sassandarewa,
Hannunsa ta kama ta riqe tana fadin inna lillahi wa'inna ilaihi raji'un haliifa maiya sameka?
Kuka tasaka saboda tanada raunin zuciya ta kamkameshi ajikinta tana kuka sai qoqarin kwacewa yakeyi dayake yanada karfi tashi daya ya kwace yaci gaba da kawa mai amsa kuwwa,
Qarasawa ummi tayi itama tahau gadon tafara yimasa addu'a tana tofa masa kusan 3minute suna ahaka saika ruma tashigo,
Kuka tasake tana fadin na shiga uku,
Kanta babu dankwali bbu takalmi aqafarta tafice a sashin bata tsaya ko inaba sai sashin mai martaba duk yanda tsakanin wajen takeda nisa amma a qaramun lokaci ta isa,
Tana isa masu gadin sashin suka fara tsareta kota kansu batayiba har sanda takai izuwa falonsa qofar d'akinsa ta tsaya tana kuma tana bubbugawa, mai martaba dake kan sallaya yaci bubbugawar qofa, bai kulaba har sanda ta idda ya sallame tukunna,
Ba'a daina bugun haukanda akeyiba shima bai kulaba sai da ya idda,
Tashi yayi yana fadin subhanallah waye haka?
Cikin kuka ruma take fadin yaya yarima! Yaya yarima!
Dasauri ya qaraso ya bude qofar cikin faduwar gaba yace mai kuma yasamu yariman?
Nima ban saniba tafad'a cikin kuka,
Jirani ina zuwa yafadi cikin qanqanin lokaci ya shirya ya fito,
A lokacin aka kawo motoci suka shirya suka fita,
Koda ya isa kai tsaye ya shiga d'akin da yarima yake,
Yayiwa su umma umarni dasu fice adakin su barsu su kadai,
Umma na kuka tafita ummi ma tafita ya zamana saura shida yarima kadai,
Wasu yan dabaru yayiwa yarima yadade cikin d'akin dan har saida aka kira sallan asubahu kafinnan yafito lokacin qawanda yarima haliifa yakeyi ya lafa,
Ficewa mai martaba yayi zuwa masallaci daga nan kuma sai ya koma shahinsa dan hutawa,
Sai bayan anyi sallah umma takoma d'akin idonta yayi jaa saboda yanda taci kuka,
Qarasawa gabon gadon tayi ta tsura masa idanuwan ba bacci yakeyiba amma hankalinsa ba ajikinsa yakeba,
Zaunawa tayi ta kamo hannunsa da yayi sanyi qlau hawaye yana bin kan kumatunta,
Advertisement
Allah yabaka lafiya yarone Allah cire maka wannan lalaura tafad'a kuka yana shirin cin karfinta,
Babu yanda ta iya dole tasha kukanta ta gaji saida hantsi kafin tabar d'akinsa,
Jiki babu karfi tayi wanka amma bata iya sanya komai abakintaba,
10:00am mai martaba ya aiko yana son ganinta,
Bata 6ata kokaci ba 10:30am tayi mata a sashin mai martaba,
Tana zaune a palour bai dauki lokaciba yfito,
Gaidashi umma tayi cikin ladabi ya amsa yana tambayarta mai jiki,
Amsawa tayi da fadin Alhamdullah,
Cikin tausayawa mai martaba yake kallon umma, acikin surukansa kaff babu wanda yakaita hankali da nutsuwa irin soyayyarda yake yiwa dansa yasanya yakejin itama batada bambamci da dannasa,
Shine dalilin daya hanata fita daga gidan bayan mutuwar dannasa,
Kuma data tashi ta raini jikinka ta bashi tarbiya mai kyau wanda ko ina yashiga ana yaba halinsa. Da irin tarbiyarda yasamu duk yanda ya shiga mahaifiyarda ta haifeshima tana shna addu'a ba shiba kad'ai,
Nisawa yayi cikin tausayawa yace" hafsatu! D'agowa umma tayi cikin ladabi ta dubeshi sannan ta dukar da kanta tace" na'am abba,
Nisawa mai martaba yayi sannan yace wani abu na hanga ganeda ciwon yarima na yanke shawararda abunda ya kamata,
Nasan ba lallai shawararda na yanke tayi miki dad'iba,
Amma hakan shine mafi A'ala,
Yarima zai dawo sashina da zama gabaki d'aya,
Sannan kuma abuna biyu shine, zanma yarima aure domin yasamu mai kula dashi da kyau,
Idan da mace kusa dashi wasu abubuwan dasuzo dasauki, sannan ko bayan aurenda zanyi masa zai zauna anan 6arin daya layin shida matarsa,
Ta dalilin wannan auren sai kiga Allah ya dubu niyyarmu yabashi lafiya,
Umma cikin zuciyarta bataji wani abu gameda dawowar yarima wajan mai martaba ba, saboda tasan shi zaifi kula dashi zai samu wanda zasu kula dashi fiyeda kowa, kuma zaman awajansa zaifi zama masa sirri, akoda yaushe kuma zai samu damar yimasa magani, ta tabbata idan asaahin mai martaba yake babu mai shiga wajan yarima dai-dai da matansa kuwa,
Dan mai martaba ba fita yakeyi sosaiba zaman fada bawani yinsa yakeyiba sabida da jikin tsufa,
Nisawa umma tayi bayan tagama tunaninta cikin ladabi tace duk yanda kayi dai-dai ne abba Allah yabashi lafiya,
Amin mai martaba ya amsa sannan yace Allah yayi miki albarka zuwa dare zanzo da kaina in tafi dashi,
Sallama umma tayi masa tatafi,
Bayan umma takoma ta shaidawa ummi yanda sukayi da mai martaba sannan tace wallhy ni ba wannan bane damuwata tunda nasan can wajansa zaifi samun kulawa, damuwata itace aurenda yace zaiyi masa, dududu nawa yariman yake?
Bazai wuce 24yrs ba sannan kuma gashi bansan wace irin mace za'a aura masaba shin wacce zata kula dashibr kokuma wacce bazata kula dashiba shine babban damuwata,
Nisawa ummi tayi sannan tace nikam banga aibu a hakanba saboda yanzu duk cikinmu babu wacce zata kula dashi kamar matar aurensa, kinga auren shine yafi,
Nima bawa naga aibun hakan bane cewa umma kawai dai ina duba yanayinda yake cikine,
Hakane kam mudai namu addu'ane zallah Allah yabashi lafiya shine babban damuwarmu, amma nasan mai martaba kafin ya aikata abu yakan tsaya yayi shawara sosai akai."
——————-
Hajiya sabuwa kuwa da asubahi zancen ciwon yarima ya risketa taji dadi sosai,
Amma shaida mata da akayi mai martaba yaje acikin daren ya lafa ba qaramin tashin hankali ta shigaba,
Abunda bata saniba shine addu'a bata bar komaiba."
———
Umma na zaune da yamma abokin abban yarima yazo dubasu kamar yanda yasaba baya daukan lokaci baizo dubasu ba duk dukiyarda suke dashi ba hakan yake hanawa shima ya narkar musu da tashi dukiyarba,
Har qasa biyu ya fitada yarima saboda nema masa lafiya ba'a daceba,
Koda abban yarima ya rasu duk dukiyarda mahaifin yabar musu dakuma wacce take cikin gidan sarautar bai hanashi daukan wasu daka cikin dawainiyar yarima da mahaifiyarshiba,
Bayan sun gaisa umma ta shaida nasa yanda sukayi da mai martaba saboda kamar mahaifi haka tadauke ma yarima, yaji dadi sosai, cikin ransa yake ayyanawa da'ace yanada yarinya budurwa da batayi aureba toda ma yarima zai bawa amma kuma yarasab mata biyune duk sunyi aure sai uku maza,
Abun arziki yakawo musu sannan yayi musu sallama yatafi,
Da dare yayi maimartaba da kansa yazo yadauki yarima ya tafi dashi kamar yanda yace."
Idan kunason na ringa qoqartawa inayu muku typing gaskiya comment yayi yawa danni rashin comment na daya daga cikin abunda yake hanani typing."
————
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Toh Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial333 Chapters
Gate Guardian - Song of the Frozen Soul
#2 on Wattpad's Lightnovel Category! Since the beginning of time, the world has been the slaughtering ground of the Eidolons; mysterious beings from a parallel universe that contaminates the mind of the people to commit deadly sins. In an ambitious struggle to put an end to this evil corruption, warriors with extraordinary abilities; the Gate Guardians relentlessly fight these monsters. One day, Alaric ceases to become a regular high school student - He becomes trapped in the crevice of dimensions and suddenly attacked by an Eidolon. Coming to his rescue just in time is a Gate Guardian named Tiara, his weird new classmate. So now, he is stuck with this clumsy maiden who swore to protect him from these extradimensional monsters! A wacky romance between the two will start to unfold! But unbeknownst to them, a much darker force lurks in the shadows that will lead to Tiara’s brutal murder... This is a song of love. This is a song of hope. This is a song of laughters. This is a song of tears. This is the Song of the Frozen Soul. Support: https://www.paypal.me/archlordzero
8 169 - In Serial6 Chapters
Redemption
Remnants of ancient history told of a time when great magics were possible, but now most go their entire life without knowledge of its existance. However, things will soon change as the wall holding back the past begins to break and mana again floods the world. But more than just mana was sealed away... ~ Back from a long hiatus, this time with some semblence of a plan and both the time and the desire to write. Writing still needs work to be sure, but I plan to see that chapter number get as high as I can and work out the kinks along the way.
8 136 - In Serial38 Chapters
Cryptic Asunder (Book one)
A life full of joy and tragedy, Vila's story begins with the very person she despises. Thankfully, a man by the name of Sommi rescues her from the clutches of her master. Years go by with her bubble of ignorance to what goes on anywhere else and she lives happily on the outskirts of Kai village. This all changes when she comes home from the market one day to find her little hut ransacked and her hero, Sommi, gone. A man named Vensen haunts her every thought as she travels the country of Aishy and the void itself in search of her father figure. Many strange and horrifying events take place as Vila also encounters revelations of who she is and the family she comes from. None of it makes sense, and yet there is a hidden string of order in it all. -------------------------------------------- Written by Robin Dobi, all rights reserved as of 2010 (c) (first draft) 3rd revision. First book of trilogy/chronicles. Picture was made soley by me! Any and all copies of this story without the author's permission or knowledge is illegal. Those who are bold enough to commit such a crime will be prosecuted! Rated as mature content for language, violence, and dark concepts. 16 years of age and up is the suggested maturity. YOU HAVE BEEN WARNED!
8 237 - In Serial45 Chapters
Unspoken Thoughts
𝗨𝗡𝗦𝗣𝗢𝗞𝗘𝗡 𝗧𝗛𝗢𝗨𝗚𝗛𝗧𝗦 is a collection of bitter, sweet, and bittersweet poems about painful love, true love, happy endings, sad endings, heartaches, falling in love, fall out of love, heartbreaks, being left behind, and leaving someone you love behind.With a total of 40 different poems, 𝘜𝘯𝘴𝘱𝘰𝘬𝘦𝘯 𝘛𝘩𝘰𝘶𝘨𝘩𝘵𝘴, a three-part poetry collection, will make you laugh and cry at the same time. A poetry collection that makes you realize how happy and painful is when you enter the world called . . . 𝙡𝙤𝙫𝙚.
8 125 - In Serial16 Chapters
Deepest Desire
Sent to a new world with a few extra ""items"" Jake was told if he won his deepest desire would be granted. In a world of Dark Ages it was time for light to shine through.
8 173 - In Serial12 Chapters
Fortunate and Unfortunate Events #1-#12 to A School Dream
**THESE EVENTS HAPPEN AFTER THE EVENTS OF A School Dream. IF YOU HAVE NOT READ THAT THEN DO NOT READ THIS YET**Lena's gone off to college. Everyone's going through their own things as they grow up into the young adults that they become to be. A lot of events happen during the time when the two are separated...
8 177

