《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 24
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
Wannan shafin sadaukarwane gareki JAMILA GUMEL meelarh, Alkhairin Allah yakai miki., nagode kawai da gaske da irin qaunarda kike nunawa rubutuna🥰
Page 24
Yanayin yanda take kai kawo cikin d'akin zai nuna tsanatsar izzarta taku takeyi kamar wanda batason taka qasa dukda kasancewar damuwa tanuna akan fuskarta,
Takai kusan 5minute tana wannan zagayen sallamarda taji alamun shigowane ya sanyata tsayawa wanda take jiran zuwanta kenan sai yanzu ta iso,
Cikin takunta na qasaita ta qarasa gaban gadonta ta zauna ta d'aura daya akan d'aya,
Ta wani jijji da nuna isa da kuma mulki,
Wacce ta shigone itama ta qarasa tazauna a gefen gadon,
Furzarda iska wannan mata tayi tanason yin magana amma nuna isa da izza sun hanata yin hakan,
Wacce ke zaune agefe idanda sabo ta saba da jiji dakai irinna wannan matar,
Daure zuciyarta tayi ta dubi qanwartata tace hajiya suwaiba kin sanya ankirani sannan kuma kinqi cewa komai,
Cikin izza kamar wacce take tsoron magana tace"
Yaya hadiza kiranda nayi miki akan wannan yaro nehaliifa,
Dafa kirji tayi tace shi haliifan menene kuma yafaru?
Kar dai kwabarmu keson yin ruwa,
Girgiza kai tayi hadeda yatsina baki kamar wacce aka takurawa tace"
Kusan hakan domin jakadiya takawomin magana cewa mai martaba dakansa ya dage dayi masa magani yanzu haka zancenda nake miki yafara samun sauqi,
Taqarasa maganar cikin gajarcewa saboda yanayin yanda maganar tayi mata tsayi abaki,
Tagumi Yaya hadiza ta zuba tana fadin ohh ni naga jaraba,
Wannan yaro sai kace d'an gwal mai martaba duk yabi ya tada hankalinsa akansa,
Qara hade rai hajiya suwaiba tayi tace ni duk yanda za'a banso yasamu lafiya,
Yaya hadiza tayi saurin amshe zancen da fadin aikuwa dole musan abunyi zama bai kamaniba hajiya,
Yoh idan yasamu lafiya ai kashinmu ya bushe inada tabbacin da yaronnan lafiyarsa qalau mai martaba daya dade da ajiye mulkinsa yabashi,
Lumshe do hajiya suwaiba tayi ta budesu ahankali sannan tace" yaya hadiza ko nawane zan kashe komai sukeso zan bayar, su dawo da wannan ciwon sabo fill daga nan har zuwa mutuwarsa bana buqatar hankali a gangar jikinsa,
Ko abunda nake dashi zasu qare idan duk wani abunda na mallaka zai tafi saina sanya daya daga cikin yarana sunyi mulki wannan kujera,
Wannan sarauta bazata ta6a kwacewa a hannunsuba,
Haliifa baida damar da zaiyi mulki a qasarnan bazan barshiba, sai dai bayan raina,
Jijjiga kai yaya halima tayi tace hakane yar uwata ina bayanki wannan zalinci da mai yayi kama haka?
Ainaga yayankine manya ai sukeda mulki iyi,
Dan kawai mahaifinsa ya kasance babba sai ace dole dansa zaiyi mulki fisabilillahi ayi mutane babu adalci,
Nisawa hajiya suwaiba tayi tace idanma mahaifinsa shine babba ko qarami wannan bai dameniba yanzu baya raye,
Sannan kuma ni yarana kawai nasani bansan kowaba,
Duk wanda yakeda niyyar shiga tsakanin yarana da mulki zan iyayin komai,
Advertisement
Ban hada mulki da komaiba,
Jijjiga kai yaya hadiza tayi tace wannan haka yake, miqewa tayi tana fadin wanna zancen haka yake yanzu barina tafi can wajansa musan abunyi zama nai ganmuba,
Karkad'a qafa hajiya sabuwa tayi batareda ta furta kalma dayaba tayi mata nuni da drawer,
Tagane mai take mufi hakan yasa cikin sauri ta qarasa gaban drawer tabude kudine aciki ta sanya hannu ta debi iya buqatarta sannan ta maida ta rufe tayi mata sallama."
————-
Umma ce zaune ta kafe yarima haliifa da ido wani irin zafi da tausayinsa takeji cikin ranta,
Rayuwar haliifa na baya take tunawa
Mutum mai cikeda kwajini cikekken mutum mai cika ido, mutum ne wanda kallonsa kawai ya wadatar da zuciya, yana da dabi'u masu matuqar daukan hankali,
Hawayenda ya zubo mata a idonta ta share spoon tadauka ta ebi abinci takai bakinsa kallonta ya tsaya yanayi kamar mai nazarin wani abun,
Haaaa tayi masa alamu ya bude bakinsa bai budeba har sanda takai cokalin tana qoqarin sanya masa abaki ahankali ya bude bakin ta sanya masa abinci sannan taqara share wasu hawayen kawai,
Ummi dake gefe ta kallo umma tana fadin yahya kullum cikin kuka fisabilillahi yanzu yaya kinyiwa kanki adalci kenan? Yakamata ace kin dauki wannan lamari matsayin jarabawa,
Kuma yanzu Alhamdulullahi jikin haliifaa kullun cigaba ake gani, koda yanayinsa ya canja anata kallon cigaba a lamarin uhum kiyi hakuri ki fawwalawa Allah komai shi yasan yanda zaiyi damu kuma shi yasan mai ya tsara gamedamu, tsarin ubangiji shine mai kyau,
Cikin nutsuwa umma ta murmusa tana fadin hakane sadiya Allan yaqara masa lafiya,
Amin ummi ta amsa."
Kwana biyu Al'amuran yarima alhamdulullahi ana ganin sauqi sosai,
Magana ce kawai bayayi amma komai kayi yana binka da idanuwa alamun yana fahimtar duk wani abunda yake faruwa,
Mai martaba ba qaramin dagewa yayiba wajan ganin ya tsaya tsayin daka yana naimawa haliifaa lafiya."
———
Hajiya suwaiba da yaya hadiza wannan karon bada wasa suka shiga lamarinba domin hajiya suwaiba ta shaida cewa ko dukiyarta zata qare aduniya tayi yawo tsirara yariima halifaa bazaiyi mulki ba."
Mai martaba kwana biyu jiki yadan ta6u jiki da jini kasancewar yadan zufa jikin zuba sai ahankali haka kawaima akanyi fama da jiki bare kuma da ciwo,
Awannan lokacin yaya hadiza ta kar6o duk wani qullinda zasuyi amfani dashi,
Ad'aki tasamu hajiya suwaiba ta shaida mata yanda sukayi da mutumin,
Yatsine fuska hajiya suwaiba tayi tace nifa nagaji da wannan zancen wallhy abu yaqici yaqi tura,
Yaya hadiza ta katseta da fadin A'a A'a hajiya aikuwa dai ba'ace yaqici yaqi turaba tunda ko yanzu muna kallon cigaba a lamarin, Yoh dabadan wannan mutumi ba da yanzu aikin gama yagama, na tabbata da yanzu yana kan gadon mulki ba kan gadon haukaba,
Siririn tsaki hajiya suwaiba taja sannan tace ni wannan ba damuwata bace ai kece kika kawo zancen hauka tun farko ban boye mikiba kasheeshi naso ayi,
Advertisement
Uhmm uhmm fa hajiya sawaiba, kinji abunda mutuminnan yafadi da kunneki, kasheshi ba maslaha bane bazai kasu mana yanzuba,
Yatsina fuska tayi tace ni kasheshi bazai zamamin matsalaba aikin sani abayama na aikata bai zama matsalaba sai yanzu akan wannan qaramin yaron,
Kin sani inada hanyoyi da yawa,
Saurin dakatar da ita yaya hadiza tayi tace uhm-uhm idan dai zance yawuce adaina tayar dashi na baya an rigada an aikata,
Yanxu wannan ne agabanmu,
Dan siririn tsaki hajiya suwaiba taja alamun tagaji da duk wad'annan abu buwan burinta yanzu bai wuce ayi abunda za'ayi yawuce ba kawai,
Miqa mata maganin tayi sannan tace ga wannan da man shanu za'a hadashi a tabbatar ya ta6a jikin haliifaa aikuwa komai zai rinca6e yadawo farko, yatsina fuska hajiya suwaiba tayi ta nuna maya gefe tace ta ajiye awajan,
Ajiyewa tayi tana qara nuna mata amfanin maganin,
Da zata fita hajiya suwaiba tace takira mata jakadiya bayan ta fita ta snaarwa jakadiya da kiran uwargijiyartata sannan ta wuce,
Koda jaka diya tazo hajiya suwaiba ta shaida mata cewa takawo mata man shanu cikin qanqanin lokaci tasamo,
Waya hajiya suwaiba tadauka ta tayi kira ta kara akunnenta bayan an dauka tafara fadin salim kazo yanzu ina nemanka amsawa akayi cikin wayar sannan ta katse,
Mintuna qalilan ya iso koda yazo ta shaida masa yanda sukayida yayarta bai amintaba 6atarai yayi yana fadin Ammaah nifa wannan abun duk 6ata lokaci rana daya zanyi aikina nagama da zarar kin bani dama,
Banason ganinsa akwance yana ciwo nafison ganinsa kwance cikin makara,
Dafashi Ammaah tayi tace kada kadamu salim ina gab da baka wannan dama amman yanzu muyi wannan zuwa wani lokaci tukunna,
Miqa masa maganin tayi sannan tace ka shafa a hannunka duk yanda za'ayi kata6a haliifa da hannunka, bude ido yayi yace nikuma,
Amma dai ammah kinsan yanda na tsani ganinsu koh, abawa wata jakadiya mana mai saya saini?
Jijijjiga kai ammah tayi tace nasan da hakan salim ba'a ta6a barin wani yashiga wajansa sai yan uwansa baza'a ta6a barin jakadiya tashigaba, kaikuma babu yanda suka iya dakai basu isa hanakaba,
Cikin baqin ciki salim yakar6a ya shafa a hannunsa ya fice."
—————
Umma tana zaune taji sallamarsa yashigo dubansa tayi cikin mamaki daya gaza 6oyuwa domin rabonta da sanyashi a idanuwanta tun kafin su tafi jinyar yarima,
Hasalima dama bawani haduwa sukeba saboda kowa yana harkar gabansa,
Koda yarima yadawo kuwa basu shigo dubashiba,
Gaida umma yayi yana tambayarta jikin yarima ta amsa babu yabo babu fallasa,
Yana tsaye tayi masa umarni da ya zaune kya6e fuska yayi yana fadin no basaina zaunaba nazo duba jikinnasane kawai nawuce dayake lokacin da kuka dawo bana qasar, gyada kai kawai umma tayi batareda tace komaiba,
Mintuna suka dauka ahaka sannan yadubi umma yace yana inane naga jikinsa zan wuce,
Harga Allah gar cikin ran umma bataso suhadu da yarima ba amma babu yanda zatayi saboda yanzu qaramar magana zata dawo babba, yanzu sai maganganu sutashi,
Miqewa tayi batareda tace komaiba tafara tafiya, tsayawa yayi yana kallonta wani baqin ciki yana dukansa cikin zuciyarsa, har cikin ransa yakejin haushin umma itada danta, yanzu hakama da badan yanason ida nufiba babu abunda zai kawoshi wajanta,
Yanda tatafi batareda ta tanka masaba ya 6ata masa rai, ya gane nufinta yabiyota abaya shine bazata iya fada masaba tatashi tawuce abunta,
Tsayawa unma tayi ta juya baya tana dubansa,
Basarwa yayi kamar baisan tajuyoba,
Ka qaraso umma tafada atakaice,
Yaso yayi kamar baijitaba amma kuma saiya daure yafara takawa izuwa wajanta,
D'akin yarima suka nufa kai tsaye, bacci yarima yakeyi hakan yasa taja ta tsaya, shima ganin haka yasa yaja ya tsaya,
Kallonsa yakeyi cikin zuciyarsa yana jin d'aci wani irin tsana yake yiwa yarima, shine kadai abunda ya tsaya masa agaba arayuwa, idanba dalilinsaba da duk wani matsalarsa ta kau,
Kawarda kai gefe yayi yakasa furta kalman sauqi,
Hannunsa yakai ya ta6a qafar yarina yana fadin jikin dasauqi daga haka yafice,
Sauke numfashi umma tayi kwata-kwata batason abunda zai sanya su rabi yarima,
Bawai dan tana zarginsu akan ciwonsaba sai dan yanda tun farko suke nuna tsanar dannata qiri-qiri bbu ko 6oyewa,
Sanda ta nemi abu ta lullu6eshi sannan taja qofa tafice adakin,
Ko kyallinsa bata gani a palour ba,
Zama tayi taci gabada abunda takeyi."
————-
Cikin 6acin rai salim yashiga dakin mahaifiyarsa wacce ke jiran dawowarasa, yana shiga ta dubeshi dason jin qarin bayani,
Zama yayi gefe sai wani huci yakeyi, hajiya suwaiba tayi saurin qarasawa sukadashi tana fadin ka aikata kasamu ka ta6ashi?
Tsaki yaja sannan yadubi mahaifiyarsa yace"
Ammah natsani wannan mata da danta aduk lokacin da nahau mulki zasubar cikin masarautarnan bazan ta6a juran ganinta tana nunamin isaba,
Dafashi Ammah tayi tana fadin kwantarda hankalinka wannan shine zahiri barin cikin masarautannan yazama kamar dole,
Yanzu fadamin yaya ka saka?
Jijjiga kai yayi alamun eh" murmushi tayi tace Ina alfahari dakai nasan bazaka ta6a bani kunyaba,
Yanzu zuwa gobe zamu jira muji sakamakon aikin,
Zuwa gobe idan banji komaiba nasan abunyi yafada sannan yamiqe yafice."
——————————————————————————-
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Toh Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial49 Chapters
Tempest Rogue
This story follows Auron, a man who has been plagued with vivid nightmares his entire life. While running away from a beating, a splitting headache causes him to fall to his knees. Once again his nightmares bleed into reality. The next "episode" he has brings him from the scene of his nightmare, to a posionous swamp. To make matters worse his memories from earth are fading, and these nightmares that plagued his childhood, filled with darkness and a red coocoon, are back and worse than ever. As he clings to the only memories he has left, he is forced to fight through a world of brutal blood thirsty monsters, dungeons, and a complex magic system governed by an ancient agreement. First time writing any sort of story. Everything is still a work in progress. As I improve on my writing I will go back and edit parts. Early chapters are subject to change as I grow my ability. I am going to try my best to write this world and improve as I go. My goal is to make my dream come to life through the medium of text. This is why I wanted to post it here. Feel free to comment, and bring constructive criticism. Hope you enjoy! More info (Spoiler warning): only read if you are picky, read a lot, and want to waste no time with a story you may not want read. This book is a litrpg. This means it contains stat tables, and other game elements. (Which you may gloss over if you would like) It is written in a fantasy world, in the style of a progression fantasy. The main character grows in power as the story plays out. My characters are written to my best ability, but you may find them immature. The MC has to adjust to fighting, and killing which he struggles with for a while. His partner is a magical salamander who is a friend and mentor. The world building, monsters, and descriptions are also low tier. (I am working hard to change that!) If you are okay reading something by someone who is just getting started then welcome! I am doing my best, and incrementally improving as I go.
8 189 - In Serial28 Chapters
Murderous Loves
"Look into my eyes"I whispered he adjusted his eyes to look into mine. "1 month ago, my mother was murdered. I came home to see her dead body lying dead on the floor. The man who killed her hasn't escaped yet. Imagine the rage I felt when I saw the man with the same 34 magnum that killed my mama in the waistband of his pants" I pressed his head harder against the table. "You tell me what I could do when I was filled with rage." Zeke a 16 year old boy comes home to find his mom murdered, after killing the man who murdered his mother hes sent to jail, how will his new life be when he is released and how will his city feel about the new murder running around town.
8 414 - In Serial23 Chapters
Deified
They say the universe began when The Seven awoke. They, seven humans from Earth have been transported from their homes to a completely new world, a blank canvas of a universe for them to fill with their newfound omnipotence. But they soon find they are not free to do as they wished. A being claiming to be the god of their world told them they must build a fantasy world for their entertainment. Thus, these new gods must cooperate (mostly), plan and construct a new world, becoming the cosmogonic myth of their own creation. "Fantasy Landscape - slolsss" by Douglas Tofoli is marked with CC PDM 1.0
8 148 - In Serial20 Chapters
Re:Shinobi
probrably not going to update until winter break. Death is an unusual thing.It's A force only few can escape.yet when you do you feel so lonely.I never counted myself among those few,that was until i died.My death was something only seen in web novels. You know it is really the most common of deaths in web novels. When i died i didn't stay dead.I was reincarnated into a world of ninjas.A world of death,pain sorrow and destruction.Yet in all that there is beauty.My past won't leave me alone,my emotions are to stubborn.i don't want to remember.........I hope i survive this.This is the new summary hope you like.Creative roasting allowed This my first fic so show the errors in my waysReviewGive ideas of what you want to see in the future.
8 139 - In Serial160 Chapters
Life Quotes
Quotes to help you reflect or remember times from your life. VOTE | COMMENT | FOLLOW MY PROFILE | CHECK OUT MY OTHER STORIES
8 205 - In Serial4 Chapters
Endsworld
This entire story is basically just me, having seen a piece of art on Tumblr, rereading Gerard Way's The True Lives Of The Fabulous Killjoys and getting an idea that may or may not be a good thing?Set in a futuristic world similar to the one in Killjoys, but a bit less cynical. (If that makes sense)Please note that I've done absolutely no planning for this, have no idea when it will update or where I'm going, and the only ships in it are the ones that are confirmed to be canon. This means only Paultryck and Kim&Katya, whose ship name I don't know, and from what I've heard, Eduardo&Laurel is also canon(?), though I'm not sure if the neighbors will actually be in this much. Again, haven't planned anything!All I can say for sure is I won't kill any of the main cast, and this will revolve around the original four, namely Edd, Tom, Matt and Tord, with pre-The End designs (read as, "I like edgy Tord with darker hair"). Essentially it's their designs from Spares.Rated PG-13 to possibly M depending on where you live for gore/death and swearing-I'm not really one for gruesome details though so I try to keep the gory stuff a bit vague. You can always ask me about how bad it is before reading if you're worried it'll upset you, my inbox is always open.
8 69

