《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 24
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
Wannan shafin sadaukarwane gareki JAMILA GUMEL meelarh, Alkhairin Allah yakai miki., nagode kawai da gaske da irin qaunarda kike nunawa rubutuna🥰
Page 24
Yanayin yanda take kai kawo cikin d'akin zai nuna tsanatsar izzarta taku takeyi kamar wanda batason taka qasa dukda kasancewar damuwa tanuna akan fuskarta,
Takai kusan 5minute tana wannan zagayen sallamarda taji alamun shigowane ya sanyata tsayawa wanda take jiran zuwanta kenan sai yanzu ta iso,
Cikin takunta na qasaita ta qarasa gaban gadonta ta zauna ta d'aura daya akan d'aya,
Ta wani jijji da nuna isa da kuma mulki,
Wacce ta shigone itama ta qarasa tazauna a gefen gadon,
Furzarda iska wannan mata tayi tanason yin magana amma nuna isa da izza sun hanata yin hakan,
Wacce ke zaune agefe idanda sabo ta saba da jiji dakai irinna wannan matar,
Daure zuciyarta tayi ta dubi qanwartata tace hajiya suwaiba kin sanya ankirani sannan kuma kinqi cewa komai,
Cikin izza kamar wacce take tsoron magana tace"
Yaya hadiza kiranda nayi miki akan wannan yaro nehaliifa,
Dafa kirji tayi tace shi haliifan menene kuma yafaru?
Kar dai kwabarmu keson yin ruwa,
Girgiza kai tayi hadeda yatsina baki kamar wacce aka takurawa tace"
Kusan hakan domin jakadiya takawomin magana cewa mai martaba dakansa ya dage dayi masa magani yanzu haka zancenda nake miki yafara samun sauqi,
Taqarasa maganar cikin gajarcewa saboda yanayin yanda maganar tayi mata tsayi abaki,
Tagumi Yaya hadiza ta zuba tana fadin ohh ni naga jaraba,
Wannan yaro sai kace d'an gwal mai martaba duk yabi ya tada hankalinsa akansa,
Qara hade rai hajiya suwaiba tayi tace ni duk yanda za'a banso yasamu lafiya,
Yaya hadiza tayi saurin amshe zancen da fadin aikuwa dole musan abunyi zama bai kamaniba hajiya,
Yoh idan yasamu lafiya ai kashinmu ya bushe inada tabbacin da yaronnan lafiyarsa qalau mai martaba daya dade da ajiye mulkinsa yabashi,
Lumshe do hajiya suwaiba tayi ta budesu ahankali sannan tace" yaya hadiza ko nawane zan kashe komai sukeso zan bayar, su dawo da wannan ciwon sabo fill daga nan har zuwa mutuwarsa bana buqatar hankali a gangar jikinsa,
Ko abunda nake dashi zasu qare idan duk wani abunda na mallaka zai tafi saina sanya daya daga cikin yarana sunyi mulki wannan kujera,
Wannan sarauta bazata ta6a kwacewa a hannunsuba,
Haliifa baida damar da zaiyi mulki a qasarnan bazan barshiba, sai dai bayan raina,
Jijjiga kai yaya halima tayi tace hakane yar uwata ina bayanki wannan zalinci da mai yayi kama haka?
Ainaga yayankine manya ai sukeda mulki iyi,
Dan kawai mahaifinsa ya kasance babba sai ace dole dansa zaiyi mulki fisabilillahi ayi mutane babu adalci,
Nisawa hajiya suwaiba tayi tace idanma mahaifinsa shine babba ko qarami wannan bai dameniba yanzu baya raye,
Sannan kuma ni yarana kawai nasani bansan kowaba,
Duk wanda yakeda niyyar shiga tsakanin yarana da mulki zan iyayin komai,
Advertisement
Ban hada mulki da komaiba,
Jijjiga kai yaya hadiza tayi tace wannan haka yake, miqewa tayi tana fadin wanna zancen haka yake yanzu barina tafi can wajansa musan abunyi zama nai ganmuba,
Karkad'a qafa hajiya sabuwa tayi batareda ta furta kalma dayaba tayi mata nuni da drawer,
Tagane mai take mufi hakan yasa cikin sauri ta qarasa gaban drawer tabude kudine aciki ta sanya hannu ta debi iya buqatarta sannan ta maida ta rufe tayi mata sallama."
————-
Umma ce zaune ta kafe yarima haliifa da ido wani irin zafi da tausayinsa takeji cikin ranta,
Rayuwar haliifa na baya take tunawa
Mutum mai cikeda kwajini cikekken mutum mai cika ido, mutum ne wanda kallonsa kawai ya wadatar da zuciya, yana da dabi'u masu matuqar daukan hankali,
Hawayenda ya zubo mata a idonta ta share spoon tadauka ta ebi abinci takai bakinsa kallonta ya tsaya yanayi kamar mai nazarin wani abun,
Haaaa tayi masa alamu ya bude bakinsa bai budeba har sanda takai cokalin tana qoqarin sanya masa abaki ahankali ya bude bakin ta sanya masa abinci sannan taqara share wasu hawayen kawai,
Ummi dake gefe ta kallo umma tana fadin yahya kullum cikin kuka fisabilillahi yanzu yaya kinyiwa kanki adalci kenan? Yakamata ace kin dauki wannan lamari matsayin jarabawa,
Kuma yanzu Alhamdulullahi jikin haliifaa kullun cigaba ake gani, koda yanayinsa ya canja anata kallon cigaba a lamarin uhum kiyi hakuri ki fawwalawa Allah komai shi yasan yanda zaiyi damu kuma shi yasan mai ya tsara gamedamu, tsarin ubangiji shine mai kyau,
Cikin nutsuwa umma ta murmusa tana fadin hakane sadiya Allan yaqara masa lafiya,
Amin ummi ta amsa."
Kwana biyu Al'amuran yarima alhamdulullahi ana ganin sauqi sosai,
Magana ce kawai bayayi amma komai kayi yana binka da idanuwa alamun yana fahimtar duk wani abunda yake faruwa,
Mai martaba ba qaramin dagewa yayiba wajan ganin ya tsaya tsayin daka yana naimawa haliifaa lafiya."
———
Hajiya suwaiba da yaya hadiza wannan karon bada wasa suka shiga lamarinba domin hajiya suwaiba ta shaida cewa ko dukiyarta zata qare aduniya tayi yawo tsirara yariima halifaa bazaiyi mulki ba."
Mai martaba kwana biyu jiki yadan ta6u jiki da jini kasancewar yadan zufa jikin zuba sai ahankali haka kawaima akanyi fama da jiki bare kuma da ciwo,
Awannan lokacin yaya hadiza ta kar6o duk wani qullinda zasuyi amfani dashi,
Ad'aki tasamu hajiya suwaiba ta shaida mata yanda sukayi da mutumin,
Yatsine fuska hajiya suwaiba tayi tace nifa nagaji da wannan zancen wallhy abu yaqici yaqi tura,
Yaya hadiza ta katseta da fadin A'a A'a hajiya aikuwa dai ba'ace yaqici yaqi turaba tunda ko yanzu muna kallon cigaba a lamarin, Yoh dabadan wannan mutumi ba da yanzu aikin gama yagama, na tabbata da yanzu yana kan gadon mulki ba kan gadon haukaba,
Siririn tsaki hajiya suwaiba taja sannan tace ni wannan ba damuwata bace ai kece kika kawo zancen hauka tun farko ban boye mikiba kasheeshi naso ayi,
Advertisement
Uhmm uhmm fa hajiya sawaiba, kinji abunda mutuminnan yafadi da kunneki, kasheshi ba maslaha bane bazai kasu mana yanzuba,
Yatsina fuska tayi tace ni kasheshi bazai zamamin matsalaba aikin sani abayama na aikata bai zama matsalaba sai yanzu akan wannan qaramin yaron,
Kin sani inada hanyoyi da yawa,
Saurin dakatar da ita yaya hadiza tayi tace uhm-uhm idan dai zance yawuce adaina tayar dashi na baya an rigada an aikata,
Yanxu wannan ne agabanmu,
Dan siririn tsaki hajiya suwaiba taja alamun tagaji da duk wad'annan abu buwan burinta yanzu bai wuce ayi abunda za'ayi yawuce ba kawai,
Miqa mata maganin tayi sannan tace ga wannan da man shanu za'a hadashi a tabbatar ya ta6a jikin haliifaa aikuwa komai zai rinca6e yadawo farko, yatsina fuska hajiya suwaiba tayi ta nuna maya gefe tace ta ajiye awajan,
Ajiyewa tayi tana qara nuna mata amfanin maganin,
Da zata fita hajiya suwaiba tace takira mata jakadiya bayan ta fita ta snaarwa jakadiya da kiran uwargijiyartata sannan ta wuce,
Koda jaka diya tazo hajiya suwaiba ta shaida mata cewa takawo mata man shanu cikin qanqanin lokaci tasamo,
Waya hajiya suwaiba tadauka ta tayi kira ta kara akunnenta bayan an dauka tafara fadin salim kazo yanzu ina nemanka amsawa akayi cikin wayar sannan ta katse,
Mintuna qalilan ya iso koda yazo ta shaida masa yanda sukayida yayarta bai amintaba 6atarai yayi yana fadin Ammaah nifa wannan abun duk 6ata lokaci rana daya zanyi aikina nagama da zarar kin bani dama,
Banason ganinsa akwance yana ciwo nafison ganinsa kwance cikin makara,
Dafashi Ammaah tayi tace kada kadamu salim ina gab da baka wannan dama amman yanzu muyi wannan zuwa wani lokaci tukunna,
Miqa masa maganin tayi sannan tace ka shafa a hannunka duk yanda za'ayi kata6a haliifa da hannunka, bude ido yayi yace nikuma,
Amma dai ammah kinsan yanda na tsani ganinsu koh, abawa wata jakadiya mana mai saya saini?
Jijijjiga kai ammah tayi tace nasan da hakan salim ba'a ta6a barin wani yashiga wajansa sai yan uwansa baza'a ta6a barin jakadiya tashigaba, kaikuma babu yanda suka iya dakai basu isa hanakaba,
Cikin baqin ciki salim yakar6a ya shafa a hannunsa ya fice."
—————
Umma tana zaune taji sallamarsa yashigo dubansa tayi cikin mamaki daya gaza 6oyuwa domin rabonta da sanyashi a idanuwanta tun kafin su tafi jinyar yarima,
Hasalima dama bawani haduwa sukeba saboda kowa yana harkar gabansa,
Koda yarima yadawo kuwa basu shigo dubashiba,
Gaida umma yayi yana tambayarta jikin yarima ta amsa babu yabo babu fallasa,
Yana tsaye tayi masa umarni da ya zaune kya6e fuska yayi yana fadin no basaina zaunaba nazo duba jikinnasane kawai nawuce dayake lokacin da kuka dawo bana qasar, gyada kai kawai umma tayi batareda tace komaiba,
Mintuna suka dauka ahaka sannan yadubi umma yace yana inane naga jikinsa zan wuce,
Harga Allah gar cikin ran umma bataso suhadu da yarima ba amma babu yanda zatayi saboda yanzu qaramar magana zata dawo babba, yanzu sai maganganu sutashi,
Miqewa tayi batareda tace komaiba tafara tafiya, tsayawa yayi yana kallonta wani baqin ciki yana dukansa cikin zuciyarsa, har cikin ransa yakejin haushin umma itada danta, yanzu hakama da badan yanason ida nufiba babu abunda zai kawoshi wajanta,
Yanda tatafi batareda ta tanka masaba ya 6ata masa rai, ya gane nufinta yabiyota abaya shine bazata iya fada masaba tatashi tawuce abunta,
Tsayawa unma tayi ta juya baya tana dubansa,
Basarwa yayi kamar baisan tajuyoba,
Ka qaraso umma tafada atakaice,
Yaso yayi kamar baijitaba amma kuma saiya daure yafara takawa izuwa wajanta,
D'akin yarima suka nufa kai tsaye, bacci yarima yakeyi hakan yasa taja ta tsaya, shima ganin haka yasa yaja ya tsaya,
Kallonsa yakeyi cikin zuciyarsa yana jin d'aci wani irin tsana yake yiwa yarima, shine kadai abunda ya tsaya masa agaba arayuwa, idanba dalilinsaba da duk wani matsalarsa ta kau,
Kawarda kai gefe yayi yakasa furta kalman sauqi,
Hannunsa yakai ya ta6a qafar yarina yana fadin jikin dasauqi daga haka yafice,
Sauke numfashi umma tayi kwata-kwata batason abunda zai sanya su rabi yarima,
Bawai dan tana zarginsu akan ciwonsaba sai dan yanda tun farko suke nuna tsanar dannata qiri-qiri bbu ko 6oyewa,
Sanda ta nemi abu ta lullu6eshi sannan taja qofa tafice adakin,
Ko kyallinsa bata gani a palour ba,
Zama tayi taci gabada abunda takeyi."
————-
Cikin 6acin rai salim yashiga dakin mahaifiyarsa wacce ke jiran dawowarasa, yana shiga ta dubeshi dason jin qarin bayani,
Zama yayi gefe sai wani huci yakeyi, hajiya suwaiba tayi saurin qarasawa sukadashi tana fadin ka aikata kasamu ka ta6ashi?
Tsaki yaja sannan yadubi mahaifiyarsa yace"
Ammah natsani wannan mata da danta aduk lokacin da nahau mulki zasubar cikin masarautarnan bazan ta6a juran ganinta tana nunamin isaba,
Dafashi Ammah tayi tana fadin kwantarda hankalinka wannan shine zahiri barin cikin masarautannan yazama kamar dole,
Yanzu fadamin yaya ka saka?
Jijjiga kai yayi alamun eh" murmushi tayi tace Ina alfahari dakai nasan bazaka ta6a bani kunyaba,
Yanzu zuwa gobe zamu jira muji sakamakon aikin,
Zuwa gobe idan banji komaiba nasan abunyi yafada sannan yamiqe yafice."
——————————————————————————-
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Toh Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial72 Chapters
Game On
Matthew Barnett tried to warn those around him -- the Game was going to start soon. Everyone was going to suffer and most were going to die, unless they took some serious steps to prepare themselves for what was to come. Diagnosed with Schizophrenia, he was hospitalized for several months until the proper medications could be found to help him control his inability to distinguish reality from fantasy and could return back to a normal school life.But...What if it was the world which was actually insane, and not him? What if he was right? What if it really was time for everyone to get their "Game On"?Warning: Rated M[18+] for language, sexual themes, gore, violence, adult situations, and too much awesomeness.
8 163 - In Serial21 Chapters
An Evil Justice
Chaos, a neverending cycle of death and madness, has veiled the world with its tendrils of horror. Every day, death reaps countless innocent lives while inferno rages across the lands. The world has become the home to the sinful and tainted, serving as the perfect dystopia.It is within this world of corruption that the innocent are ruthlessly slain every day, their loved ones weeping in pain and despair. It is within this world that children live in terror, unable to grow without being exposed to violence, trickery, and death. And it is within this hateful world that holds the key to bring back the past, which once held peace and love.This key, this character of hope must thrive in the world’s gutter of feces to hone itself into a blade sharp enough to sever the sinful bindings grounding society, but will this key really bring about a new golden age? Or will it only serve to catalyze the impending doom of both the innocent and the tainted? Who knows?Only time can tell…
8 182 - In Serial37 Chapters
Eternal Soul
Luke Snow is your average man, after running he rest on a bench only to wake and see a little girl alone, while trying to help, he witness a strange phenomenon and has one wish granted. Will he regret what he wished for?For now he don't have time to think about it with a great problem that he is dealing with now, he needs a job.
8 83 - In Serial93 Chapters
Rise of a Finance Minister
Robert Maxwell owned a global accounting firm, was a Nobel Prize winning economist, global economic consultant to countries around the globe, but he was dying of old age. Robert reincarnated as William vont Ballard, the third son of Baron Richard vont Ballard. Unlike his siblings, William doesn't want to be knight or wizard, instead he wants to be merchant and an accountant. However, the journey to fulfilling his new life goals continues to throw him twists and turns. Luckily, he finds time for his true passion accounting and economic consulting. Follow Robert on his journey to become the next Minister of Finance for the Kingdom of Fermion. Author's Note: I'm a new writer, so please be patient. I don’t own the rights to the cover photo, please let me know if you want me to remove it.
8 117 - In Serial7 Chapters
Battling for Survival in a New World (On Hiatus)
A sixteen year-old boy passed away in a tragic accident. He awakens in a dark room in a strange body, and with little to aid him. Where is he and what's he to do? A dark isekai story with survival as the primary goal. A/N: Sorry if it's not very good quality, first story.
8 71 - In Serial66 Chapters
LITTLE FURY ( fairy tail. )
( Completed )━━━𝐋𝐈𝐓𝐓𝐋𝐄 𝐅𝐔𝐑𝐘❝With her tiny fists she'll bring a mighty wrath.❞[ BOOK ONE OF DEALANA KA'INO ]⤷ Fem!OC x Fairy Tail⤷ Includes added lore,additional OCs, & more⤷ Based on the Anime⤷ Plans to rewrite soon
8 179

