《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 24
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
Wannan shafin sadaukarwane gareki JAMILA GUMEL meelarh, Alkhairin Allah yakai miki., nagode kawai da gaske da irin qaunarda kike nunawa rubutuna🥰
Page 24
Yanayin yanda take kai kawo cikin d'akin zai nuna tsanatsar izzarta taku takeyi kamar wanda batason taka qasa dukda kasancewar damuwa tanuna akan fuskarta,
Takai kusan 5minute tana wannan zagayen sallamarda taji alamun shigowane ya sanyata tsayawa wanda take jiran zuwanta kenan sai yanzu ta iso,
Cikin takunta na qasaita ta qarasa gaban gadonta ta zauna ta d'aura daya akan d'aya,
Ta wani jijji da nuna isa da kuma mulki,
Wacce ta shigone itama ta qarasa tazauna a gefen gadon,
Furzarda iska wannan mata tayi tanason yin magana amma nuna isa da izza sun hanata yin hakan,
Wacce ke zaune agefe idanda sabo ta saba da jiji dakai irinna wannan matar,
Daure zuciyarta tayi ta dubi qanwartata tace hajiya suwaiba kin sanya ankirani sannan kuma kinqi cewa komai,
Cikin izza kamar wacce take tsoron magana tace"
Yaya hadiza kiranda nayi miki akan wannan yaro nehaliifa,
Dafa kirji tayi tace shi haliifan menene kuma yafaru?
Kar dai kwabarmu keson yin ruwa,
Girgiza kai tayi hadeda yatsina baki kamar wacce aka takurawa tace"
Kusan hakan domin jakadiya takawomin magana cewa mai martaba dakansa ya dage dayi masa magani yanzu haka zancenda nake miki yafara samun sauqi,
Taqarasa maganar cikin gajarcewa saboda yanayin yanda maganar tayi mata tsayi abaki,
Tagumi Yaya hadiza ta zuba tana fadin ohh ni naga jaraba,
Wannan yaro sai kace d'an gwal mai martaba duk yabi ya tada hankalinsa akansa,
Qara hade rai hajiya suwaiba tayi tace ni duk yanda za'a banso yasamu lafiya,
Yaya hadiza tayi saurin amshe zancen da fadin aikuwa dole musan abunyi zama bai kamaniba hajiya,
Yoh idan yasamu lafiya ai kashinmu ya bushe inada tabbacin da yaronnan lafiyarsa qalau mai martaba daya dade da ajiye mulkinsa yabashi,
Lumshe do hajiya suwaiba tayi ta budesu ahankali sannan tace" yaya hadiza ko nawane zan kashe komai sukeso zan bayar, su dawo da wannan ciwon sabo fill daga nan har zuwa mutuwarsa bana buqatar hankali a gangar jikinsa,
Ko abunda nake dashi zasu qare idan duk wani abunda na mallaka zai tafi saina sanya daya daga cikin yarana sunyi mulki wannan kujera,
Wannan sarauta bazata ta6a kwacewa a hannunsuba,
Haliifa baida damar da zaiyi mulki a qasarnan bazan barshiba, sai dai bayan raina,
Jijjiga kai yaya halima tayi tace hakane yar uwata ina bayanki wannan zalinci da mai yayi kama haka?
Ainaga yayankine manya ai sukeda mulki iyi,
Dan kawai mahaifinsa ya kasance babba sai ace dole dansa zaiyi mulki fisabilillahi ayi mutane babu adalci,
Nisawa hajiya suwaiba tayi tace idanma mahaifinsa shine babba ko qarami wannan bai dameniba yanzu baya raye,
Sannan kuma ni yarana kawai nasani bansan kowaba,
Duk wanda yakeda niyyar shiga tsakanin yarana da mulki zan iyayin komai,
Advertisement
Ban hada mulki da komaiba,
Jijjiga kai yaya hadiza tayi tace wannan haka yake, miqewa tayi tana fadin wanna zancen haka yake yanzu barina tafi can wajansa musan abunyi zama nai ganmuba,
Karkad'a qafa hajiya sabuwa tayi batareda ta furta kalma dayaba tayi mata nuni da drawer,
Tagane mai take mufi hakan yasa cikin sauri ta qarasa gaban drawer tabude kudine aciki ta sanya hannu ta debi iya buqatarta sannan ta maida ta rufe tayi mata sallama."
————-
Umma ce zaune ta kafe yarima haliifa da ido wani irin zafi da tausayinsa takeji cikin ranta,
Rayuwar haliifa na baya take tunawa
Mutum mai cikeda kwajini cikekken mutum mai cika ido, mutum ne wanda kallonsa kawai ya wadatar da zuciya, yana da dabi'u masu matuqar daukan hankali,
Hawayenda ya zubo mata a idonta ta share spoon tadauka ta ebi abinci takai bakinsa kallonta ya tsaya yanayi kamar mai nazarin wani abun,
Haaaa tayi masa alamu ya bude bakinsa bai budeba har sanda takai cokalin tana qoqarin sanya masa abaki ahankali ya bude bakin ta sanya masa abinci sannan taqara share wasu hawayen kawai,
Ummi dake gefe ta kallo umma tana fadin yahya kullum cikin kuka fisabilillahi yanzu yaya kinyiwa kanki adalci kenan? Yakamata ace kin dauki wannan lamari matsayin jarabawa,
Kuma yanzu Alhamdulullahi jikin haliifaa kullun cigaba ake gani, koda yanayinsa ya canja anata kallon cigaba a lamarin uhum kiyi hakuri ki fawwalawa Allah komai shi yasan yanda zaiyi damu kuma shi yasan mai ya tsara gamedamu, tsarin ubangiji shine mai kyau,
Cikin nutsuwa umma ta murmusa tana fadin hakane sadiya Allan yaqara masa lafiya,
Amin ummi ta amsa."
Kwana biyu Al'amuran yarima alhamdulullahi ana ganin sauqi sosai,
Magana ce kawai bayayi amma komai kayi yana binka da idanuwa alamun yana fahimtar duk wani abunda yake faruwa,
Mai martaba ba qaramin dagewa yayiba wajan ganin ya tsaya tsayin daka yana naimawa haliifaa lafiya."
———
Hajiya suwaiba da yaya hadiza wannan karon bada wasa suka shiga lamarinba domin hajiya suwaiba ta shaida cewa ko dukiyarta zata qare aduniya tayi yawo tsirara yariima halifaa bazaiyi mulki ba."
Mai martaba kwana biyu jiki yadan ta6u jiki da jini kasancewar yadan zufa jikin zuba sai ahankali haka kawaima akanyi fama da jiki bare kuma da ciwo,
Awannan lokacin yaya hadiza ta kar6o duk wani qullinda zasuyi amfani dashi,
Ad'aki tasamu hajiya suwaiba ta shaida mata yanda sukayi da mutumin,
Yatsine fuska hajiya suwaiba tayi tace nifa nagaji da wannan zancen wallhy abu yaqici yaqi tura,
Yaya hadiza ta katseta da fadin A'a A'a hajiya aikuwa dai ba'ace yaqici yaqi turaba tunda ko yanzu muna kallon cigaba a lamarin, Yoh dabadan wannan mutumi ba da yanzu aikin gama yagama, na tabbata da yanzu yana kan gadon mulki ba kan gadon haukaba,
Siririn tsaki hajiya suwaiba taja sannan tace ni wannan ba damuwata bace ai kece kika kawo zancen hauka tun farko ban boye mikiba kasheeshi naso ayi,
Advertisement
Uhmm uhmm fa hajiya sawaiba, kinji abunda mutuminnan yafadi da kunneki, kasheshi ba maslaha bane bazai kasu mana yanzuba,
Yatsina fuska tayi tace ni kasheshi bazai zamamin matsalaba aikin sani abayama na aikata bai zama matsalaba sai yanzu akan wannan qaramin yaron,
Kin sani inada hanyoyi da yawa,
Saurin dakatar da ita yaya hadiza tayi tace uhm-uhm idan dai zance yawuce adaina tayar dashi na baya an rigada an aikata,
Yanxu wannan ne agabanmu,
Dan siririn tsaki hajiya suwaiba taja alamun tagaji da duk wad'annan abu buwan burinta yanzu bai wuce ayi abunda za'ayi yawuce ba kawai,
Miqa mata maganin tayi sannan tace ga wannan da man shanu za'a hadashi a tabbatar ya ta6a jikin haliifaa aikuwa komai zai rinca6e yadawo farko, yatsina fuska hajiya suwaiba tayi ta nuna maya gefe tace ta ajiye awajan,
Ajiyewa tayi tana qara nuna mata amfanin maganin,
Da zata fita hajiya suwaiba tace takira mata jakadiya bayan ta fita ta snaarwa jakadiya da kiran uwargijiyartata sannan ta wuce,
Koda jaka diya tazo hajiya suwaiba ta shaida mata cewa takawo mata man shanu cikin qanqanin lokaci tasamo,
Waya hajiya suwaiba tadauka ta tayi kira ta kara akunnenta bayan an dauka tafara fadin salim kazo yanzu ina nemanka amsawa akayi cikin wayar sannan ta katse,
Mintuna qalilan ya iso koda yazo ta shaida masa yanda sukayida yayarta bai amintaba 6atarai yayi yana fadin Ammaah nifa wannan abun duk 6ata lokaci rana daya zanyi aikina nagama da zarar kin bani dama,
Banason ganinsa akwance yana ciwo nafison ganinsa kwance cikin makara,
Dafashi Ammaah tayi tace kada kadamu salim ina gab da baka wannan dama amman yanzu muyi wannan zuwa wani lokaci tukunna,
Miqa masa maganin tayi sannan tace ka shafa a hannunka duk yanda za'ayi kata6a haliifa da hannunka, bude ido yayi yace nikuma,
Amma dai ammah kinsan yanda na tsani ganinsu koh, abawa wata jakadiya mana mai saya saini?
Jijijjiga kai ammah tayi tace nasan da hakan salim ba'a ta6a barin wani yashiga wajansa sai yan uwansa baza'a ta6a barin jakadiya tashigaba, kaikuma babu yanda suka iya dakai basu isa hanakaba,
Cikin baqin ciki salim yakar6a ya shafa a hannunsa ya fice."
—————
Umma tana zaune taji sallamarsa yashigo dubansa tayi cikin mamaki daya gaza 6oyuwa domin rabonta da sanyashi a idanuwanta tun kafin su tafi jinyar yarima,
Hasalima dama bawani haduwa sukeba saboda kowa yana harkar gabansa,
Koda yarima yadawo kuwa basu shigo dubashiba,
Gaida umma yayi yana tambayarta jikin yarima ta amsa babu yabo babu fallasa,
Yana tsaye tayi masa umarni da ya zaune kya6e fuska yayi yana fadin no basaina zaunaba nazo duba jikinnasane kawai nawuce dayake lokacin da kuka dawo bana qasar, gyada kai kawai umma tayi batareda tace komaiba,
Mintuna suka dauka ahaka sannan yadubi umma yace yana inane naga jikinsa zan wuce,
Harga Allah gar cikin ran umma bataso suhadu da yarima ba amma babu yanda zatayi saboda yanzu qaramar magana zata dawo babba, yanzu sai maganganu sutashi,
Miqewa tayi batareda tace komaiba tafara tafiya, tsayawa yayi yana kallonta wani baqin ciki yana dukansa cikin zuciyarsa, har cikin ransa yakejin haushin umma itada danta, yanzu hakama da badan yanason ida nufiba babu abunda zai kawoshi wajanta,
Yanda tatafi batareda ta tanka masaba ya 6ata masa rai, ya gane nufinta yabiyota abaya shine bazata iya fada masaba tatashi tawuce abunta,
Tsayawa unma tayi ta juya baya tana dubansa,
Basarwa yayi kamar baisan tajuyoba,
Ka qaraso umma tafada atakaice,
Yaso yayi kamar baijitaba amma kuma saiya daure yafara takawa izuwa wajanta,
D'akin yarima suka nufa kai tsaye, bacci yarima yakeyi hakan yasa taja ta tsaya, shima ganin haka yasa yaja ya tsaya,
Kallonsa yakeyi cikin zuciyarsa yana jin d'aci wani irin tsana yake yiwa yarima, shine kadai abunda ya tsaya masa agaba arayuwa, idanba dalilinsaba da duk wani matsalarsa ta kau,
Kawarda kai gefe yayi yakasa furta kalman sauqi,
Hannunsa yakai ya ta6a qafar yarina yana fadin jikin dasauqi daga haka yafice,
Sauke numfashi umma tayi kwata-kwata batason abunda zai sanya su rabi yarima,
Bawai dan tana zarginsu akan ciwonsaba sai dan yanda tun farko suke nuna tsanar dannata qiri-qiri bbu ko 6oyewa,
Sanda ta nemi abu ta lullu6eshi sannan taja qofa tafice adakin,
Ko kyallinsa bata gani a palour ba,
Zama tayi taci gabada abunda takeyi."
————-
Cikin 6acin rai salim yashiga dakin mahaifiyarsa wacce ke jiran dawowarasa, yana shiga ta dubeshi dason jin qarin bayani,
Zama yayi gefe sai wani huci yakeyi, hajiya suwaiba tayi saurin qarasawa sukadashi tana fadin ka aikata kasamu ka ta6ashi?
Tsaki yaja sannan yadubi mahaifiyarsa yace"
Ammah natsani wannan mata da danta aduk lokacin da nahau mulki zasubar cikin masarautarnan bazan ta6a juran ganinta tana nunamin isaba,
Dafashi Ammah tayi tana fadin kwantarda hankalinka wannan shine zahiri barin cikin masarautannan yazama kamar dole,
Yanzu fadamin yaya ka saka?
Jijjiga kai yayi alamun eh" murmushi tayi tace Ina alfahari dakai nasan bazaka ta6a bani kunyaba,
Yanzu zuwa gobe zamu jira muji sakamakon aikin,
Zuwa gobe idan banji komaiba nasan abunyi yafada sannan yamiqe yafice."
——————————————————————————-
Ina kuke masoyana masoyan rubutuna🥰 hajiyata kin karanta bibiyata akeyi? Toh Y'ar fari fa? Dakuma wanda nake rubutawa yanzu Qaddarar rayuwa? To yaya kikaji salon🥰😍 ya qayatar koh? hajiyata wadannan aiba komai bane somon ta6ine cikin shirinda nayi na nishadatar daku hajiyoyina manyan mata Ku biyoni cikin littafina na YARIMA FAYAD🥰 wannan littafin salonsa daban yake akwaia zazza6ar qauna🥰😍 ciki dana tanada muku, 200kacal zaki sameshi, ga dadi ga sauqi🥰 Don neman qarin bayani,
tuntubeni ta wannan no 08161146563,
Kokuma ki biya kudinki ta wannan accnt 0003075326 zainab m bawa JAIZ BANK.
Ku antayo daga ciki😊😌
Hajiyata kada ki bari abaki labari."
✔️ote
Comment
Follow
Share plss
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial210 Chapters
Lament of the Fallen
What happens when the great war is over and the 'good' side has won? What happens to the last surviving members of the fallen 'evil' side of the conflict? This is the tale of one of those survivors. Will she try to seek revenge? Will she try to hide her origin and ancestry and live in peace? Or will the universe have something else in mind?
8 230 - In Serial35 Chapters
Dungeons & Demons
*!* This story is currently being continued on a different page, following years of hiatus and extensive rewrites *!* Please follow the link to read the up-to-date version: https://www.royalroad.com/fiction/53863/cycles-of-ruin Basil von Doom is a powerful dungeon keeper with a simple mission: to bring ruin and destruction upon civilized worlds at the height of their decadence and stagnation. Much like his father before him, the new master of House Doom is a prodigy of war, yet the venerable minions of his household still hold strange loyalties toward his missing ancestor, silently comparing the legendary rage of his father to the more pragmatic approach of the son. Adding to Basil’s frustrations is the lack of accomplishment he feels for his work, with the dungeon keeper often taking on handicaps just to give his enemies a fighting chance. With all the power and wealth one could ever dream of already within his grasp, Basil now finds that the achievements of others kindle more joy in his heart than his own crushing victories. Thus Basil has taken up mentoring the next generation of dungeon keepers to try and diagnose the cause for his own lack of passion. With his apprentice, Elnora, managing most of the daily work around the dungeon, Basil can finally turn his attention towards his personal concerns, such as tackling the shadow of his legendary father that still looms large over him.
8 158 - In Serial9 Chapters
An Ode to Swordsmen
The country is thrown into chaos after the Emperor's Jade Sword, a symbol of his divine right to rule, is stolen by a powerful swordsman. An imperial army ravages the land in search of it, left only a few clues of its whereabouts. Martial arts sects look on in horror as their innocent brothers are cut down. Lakhuto, a gifted swordsman from the Mount Kunlun Sect, is forced into the conflict when his sect is attacked. Having little knowledge of the secular world, he must learn how to blend in as he makes his away across China undetected. His plans to warn other sects of the approaching danger are thrown into chaos when he runs into a wounded criminal and an enigmatic martial artist, who reveals to him a conspiracy spanning half a century. Surrounded by an army, with danger hidden in every shadow, he must discover who stole the Jade Sword and framed several sects, before the entire country is set ablaze.
8 91 - In Serial19 Chapters
The Unknown Hero
When the world decided to change it didn't happen with a bang, instead it came with a buzz. Then screams of horror. And after that...
8 178 - In Serial29 Chapters
Lost in Acleirea
After finishing the newest, generic anime about a teenage boy being sent to another world, a thirteen year old boy, Kyle, finds himself before a man named Genie. After Genie reads his mind and grants his wishes he sends Kyle to the continent of Acleirea. Fastforward four years and Kyle is a seventeen year old mercenary who's called by an old friend. After accepting to protect his daughter, Kyle finds himself being sent to a school filled with magic. Is this the adventure that Kyle's kid self wanted? (Uploading schedule is whenever I have time and will try to upload everyday)
8 154 - In Serial42 Chapters
She Will Persist
"I'm not feisty I just don't care for people's shit."Adira Bowman is an ex- mind-controlled assassin who got herself captured by a secret all-boys spy agency. The director of the agency now wants her to become an agent, put her skills to use and have her train among his ragtag crew of smirking rebels scarred with tragedy, fighting mafia bosses and tracking master assassins. And he has sent a very crafty agent her age to recruit her.Soon Adira stumbles into a dark agency secret; the hushed tragedy of a forbidden romance. She's put on a demonic terrorism case with a group of boys who only have spying in common. And the boy who recruited her originally, well, he might just actually be able to get her to finally forgive herself for everything she has ever done. Amidst tracing the origins of nuclear bombs and a stopping a terrorist attack, feelings may be kindled and rekindled...Will Adira persist insisting that she deserves to be punished, or will she get caught up in a world of spying, lying, hiding, befriending, forgiving and...loving?
8 98

