《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 22
Advertisement
**
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*HASKE WRITTERS ASSOCIATION*💡
Written by
zaynab bawa (z3iiyyb3rw3r)
#Follow me on
Page 22
Sadam yayiwa sawwama alqawarin akan zaiyi karatu iyakar iyawarsa har sai yaga yayi qoqari kodan ya sanyata cikin farin ciki,
Sun fara exam Alhamdulillah komai yana zuwa masa dasauki barinma yanda mutanenda yake tareda su suka dage sosai da addu'a akan jarabawarsa, addu'a baga mummy baga sawwama ba kowa yana nasa qoqarin,
Mummy kuwa har tashin dare takeyi itakuwa sawwama bawai tasaba da tashin dare bane dan bata ta6a yiba,
Hakan yasa cikin sallolinta na ranar take zabga masa addu'a,
Sa'i-sa'i yanzu sadam yake zuwa wajan sawwama kamar yanda ta buqata yazauna yayi karatu,
Shi kansa bahaka yasoba kawai dai yabi yanda tasoone itama anata wajan bawai hakan tasoba kawai tasan cewa idan ta yaci gabada zuwa kullum zai takurane."
———-
Yau satinsu sadam daya da fara exam amma zuciyarsa takasa sama masa ntsuwa gameda karatun sawwama kamar yanda yace saiya gama exam, amma yanzu yana ganin ra'ayinsa yafara canjawa baiga amfanin jira har sai yagama ba,
Saboda bazai juri ganinta cikin halin rashin sani ba, dama ace karatun bokone amma karatun islama aida matsala ayau idan tamutu wajan Allah batada wani uzuri hakan yasa ya yanke shawarar tun tu6arta da maganar fara zuwa makaranta idan yaso daga baya bayan yagama exam sai ayi maganar makarantar boko,
Akwai interval na kwana biyu tsakanin exam dinsu hakan yasa ya yanke shawarar zuwa wajanta yau da dare idan Allah ya kaimu,
Kamar yanda yasaba zuwa bayan ya fita sallan isha'i kai tsaye kawai ya wuce,
Wajanta bayan ya isa ya aika aka kirawota, sawwama dama ta sanya rai da zuwansa shiyasa bata wani jimaba tafito domin tagama shiryawa tsaff,
Tafito cikin tafiyarta na nutsuwa kamar wacce batason taka qasar, yanayin yanda take tafiya a nutse yasanya idan tana tafiya ko qaran takun tafiyanta ba'aji, sadam idonsa yana kan qofar alokacinda idonsa ya sauka akanta ya sauqarda ijiyar zuciya yana mai qara godiya a Allah cikin ransa nutsuwar sawwama kadai ta cancanji asota,
tabbas ganin sawwama kadai kan sanya masa kwanciyar hankali yakanji sanyi yana ratsa duk wani gabban jikinsa aduk lokacinda yayi arba da ita,
Lumshe idanuwa yayi ahankali yabudesu akanta wani irin soyayayrtane take fisgarsa,
Itama sawwama anata wajan hakanne,
Farin ciki ta tsinci kanta aciki alokacinda tadaura idanunta akan fuskarsa mai cikeda dakamala,
Ga wani irin kamshinsa wanda akoda yaushe kafin ka qarasa wajanda yake kamshinsa yake qaraso maka, takan rasa wasu irin turare haka yake amfani dasu wanda kamshinsu ke saukarda nutsuwa da farin ciki,
Qarasawa tayi da murmushi akan fuskarta ta nemi waje tazauna wadan wani kututturen iceh take qofar gidansu,
Advertisement
Cikin muryarta mai sanyi da dadin sauraro ta gaidashi cikin kadabi,
Amsawa yayi yana binta da kallo sakamakon hasken farin wata ya haske gabaki daya ilahirin wajan,
Numfashi yasauke ahankali sannan ya kauda idansa daga kallonta sai alokacin sawwama tasamu sukuni aduk lokacinda ya tsareta da ido alokacin take rasa duk wani kuzarinta, cikin nutsuwa tabude bakinta tace" ya jarabawar?
Murmushi yayi aduk lokacinda sautin muryarta da duki dodon kunnunwansa yakanji dadi, har yanzu baiji murya mai dad'in nataba,
Koda baka santaba muryarta kadai ya isa yasa kajuya ka kalleta,
Idan tayi magana sau daya tabbas zakaso taqara bude baki tayi wata maganar domin dadin sautin muryarta,
Kuma da yadda take magana cikin nutsuwa,
Sadam ya lula cikin tunanin sawwama bai samu damar bata amsar tambayartaba,
Turo dan bakinta tayi tana fadin yaya sadam shine ina magana zakayi shiru ka rabu dani?
Kwayar idonsa ya sauke akanta yana binta da wani irin kallo ita kanta yau tarasa wani irin kallo haka sadam keyi mata mai kashe mata duk wani kuzarinta,
Me kikece? Ya tambaya cikin sanyin murya,
Har lokacin bai daga idanuwansa daga kantaba,
Kanta yana qasa tace ina tambayrka yaya jarabawa?
Alhamdulillah ya amsa atakaice,
Gyaran murya sadam yayi alamun yana sonyin magana hakanne yasan yata d'agowa cikin rashin sa'a abunda take gudun yafaru wato idanuwansu ya sarqe waje daya,
Wani irin faduwa gabanta yafarayi hakan yasa tayi
Saurin sauke idonta qasa dan bazata juri kallon kwayar idanuwansa ba,
Wani irin abu sawwama ke gani cikin kwayar idonsa
Mai daukar hankali tabbas ta tabbada akwai wani sinadari cikin kwayar idonsa kokuma zallan kyawunsu ke kwasarta batada wannan amsar,
Ajiyr zuciya sadam ya sauke cikin nutsuwa yafara magana,
Sawwama zamanki haka bayamin dadi, banason ganinki haka baki zuwa makaranta baki zuwa boko baki zuwa islamiya nayanke shawarar zaki koma islmiya awannan satin,
Dagowa tayi ta dubeshi tace da wani lokaci kenan,
Koma da wani lokacine sawwama ke zaki za6i wacce kikeso idanma ta darene kikeso saiki koma amma zamanki haka sam baiyiba,
Shiru sawwama tayi tana tunani ta tabbata babanta bazai barta tayi islamiya da dare ba garama ace da yamma to amma idan yamma ne sana'arta fa?
Kinyi shiru sawwama ko bakison makarantar ne?
Girgiza kai sawwama tayi tace A'a inaso ma amma dai baba bazai barni zuwa makarantar dare ba,
Shiru sadam yayi yasan dalilin da zaisa baba ya hanata zuwa makaranta da daddare bazai wuce yanada nasaba da abunda ya faruba.
Kuma har in dai hakane yanada gaskiya,
Zuwa yamma fa? Sadam ya jefo mata tambaya,
Kuma ya tsareta da ido,
Zuwa yamma ai ina sana'a,
Wannan ba uzuri bane sawwama sana'a ai bazata hana neman ilimi ba,
Advertisement
Abunda nakeso dake shine ki ajiye sana'ar yamma lokacin makarantar bazai wuce 2hours ba 4-6 idan kika dawo sai kiyi,
Kai ta gyada masa alamun gamsuwa da maganarsa dan batajin zata iyayen musu dashi wani irin kima take ganinsa da ita,
Murmushi yayi hadeda fadin nagode, kanta ta sunkuya qasa batareda tace komaiba,
Miqewa yayi zai tafi yace tayi masa magana da baba sawwama bataso tafiyarsa awannan lokacinba amma babu yanda ta iya haka ta miqe ta sanarwa baba yana magana dashi,
Koda yazo maganar makarantarta yayiwa baba, baba bai wani jaa zancenba ya amince sadam yayi masa godiya kamar wanda shine za'a sanya a makarantar,
Bayan baba yakoma sawwama tafito sukayi sallama yawuce,
Koda baba yashiga ciki ya shaidawa mama yanzu sukayi dashi mama ma taji dadi,
Baba yace yaron yayi tunani mai kyau in sha Allah wannan satin zan fara neman islamiyar wacce muke dan kusa da ita,
Sawwama ne tace mama maganar sana'atafa ko halima zata ringa kamawa kafin nadawo?
Eh hakanma yayi cewar mama,
Halima dai batayi magana bane amma itama har cikin ranta tanason tashiga islamiya amma tunaninta ita kanta sawwamar kudin biya mata sai andage balle aka hada da ita, tunanun hakanda tayi ya sanyata tayi shiru bata fadi akan itama tanasoba."
Washe gari sadam yafita nemawa sawwama islamiya baisha wahalaba yasamu kusa dasu dan tsallaken titine kawai tsakaninsu dasu sawwaman,
Islamiyar tanada kyau sosai amma sai dai school fees yakai wajan 3k registration dinta kuwa yakai 7k ahaka sadam yayi duk wani abunda ya kamata bai koma gidaba sanda ya dinka mata uniform dakuma hijabai saboda tunda yakeda ita da hijab biyu kawai yake kallonta iya rayuwarsa, kuma ahakanma duka sun kode abunda bai saniba dayanma na bokon tane dayake tadaina zuwa shine take amfani da hijab dinta,
Sadam bai yarda yashiga gida da kayanba saboda baida amsar tambayarda mummy zatayi masa,
Sai bayan ya fita sallar isha'i yabiya yakar6i kayan wajanda yabada ajiya,"
Koda ya isa yasamu sawwama tagama tashiga ciki dan haka ya aika aka kirawota,
Bayan sun gaisa ya bata kayan dan bawani dadewa zaiyiba saboda yanada exam gobe da sassafe, kuma gabaki daya yau bai samu yayi karatu ba,
Yayi mata kwatancen school din sannan ya shaida mata akan gobe sufara zuwa sauran abunda yarage bashida yawa da zarar sunje za'a kaisu ajine kawai,
Ganin yana sauri ya sanya bata tambayeshi itadawa ba godiya tayi masa sosai yayi mata sallama yatafi,
Koda tashiga mama taganta da kaya sai tahau fada, akanme yasa zata kar6i kayansa, babane ya dakatar da ita yace baki kar6i kayan kin bude kin ganiba kika hau masifa, saannan ina laifi dan sawwama ta kar6i kayansa aiba ita ta rokeshiba,
Matso nan ya umarce sawwama matsowa tayi ta miqa masa kayan baba yakar6a yabude, kayan islamiya ne kala biyu aciki sai hijabai guda 5 dogaya har qasa,
Sai takardun rejister,
Miqa mata takardan baba yayi sawwama ta amsa ta karanta sai yanzu tagane mai yake nufi dayace gobe sufara zuwa,
Itada halima yayi musu register, uniform dinma na mutum biyune,
Miqawa halima tayi tana fadin hardake yayi mana register tsalle halima ta daka tana murna,
Baba ne yace toh madallah abu yayi kyau Allah yayi masa albarka su duka suka amsa da amin,
Mama ma tace abu yayi kyau gaskiya Allah ya saka masa da gidan aljanna,
Cikin jin dadin addu'ar mama sawwama ta amsa,
Kayan makarantar suka gwada dukansu kayan sunyi musu yawa amma bawai sosaiba hijabin kuwa har qasa yake shara, haka itama na halima dake bambamcin tsayinsu itada sawwama kadanne,
Sauran hijab dinma duka har qasa suka kaima sawwma zasu yadika masu kyau,
Aranar sadam yasha addu'a awajan yan gidannan barinma sawwama wacce dama akwaita dason hijabai rashine kawai yasa tayi hakuri."
Washe gari tun 3:30 suka shirya zuwa islamiya saida sukayi sallah sannan suka kama hanya bayan sun isa akayi musu duk wani abunda yadace sannan aka kaisu aji, ajinsu daya da halima har seat dinma dai nasu dayane,
Sai 6 aka tashi daga islamiyan suka kamo hanyar gida,
Tun daga nesa sawwama take ganin kamar sadam tsaye jikin mashin dinsa tana zuwa kusa kuwa taga shi dinne,
Murmushi ta sakar masa shima ya maida mata qarasawa wajansa tayi tana fadin yaya sadam ina wuni?
Lafiya qlau ya karatun Alhamdulillah ta amsa, baqaramin kyau tayi masa cikin uniform dinba dama kawai yabi hanyar makarantarne dan yaganta cikin uniform,
Yaya jarabawar ta tambaya,
Numfashi ya sauke sannan yace jarabawa Alhamdulillah sai kewarki dake addabata,
Hannu biyu sawwama tasanya ta rufe fuskarta tana dariya, murmushi yayi mai sauti yace kiwuce gida kinga ni dama na biyone kawai naganki kuma na ganki gida zan wuce,
Batayi maganaba halima ta qaraso tana gaidashi ya amsa cikin sakin fuska yana fadin yan makaranta ya karatun Alhamdulillah halima ta amsa sannan tayi masa godiya sosai,
Sawwama tace yawwa babama yace nayi maka godiya,
Kai kawai sadam ya daga mata sannan yace tawuce gida,
Tafiya tayi tana juyowa tana kallonsa yana sakar mata murmushi daga nan yatada mashin dinsa yayi gida suma suka wuce gida."
Gaskiya yawan vote da viewers na wattpad sunyi kadan shiyasa yanzu zan ringa bari sai bayan kwana bibbiyu ina yin update gaskiya viewers da vote sunyi kadan."
✔️ote
Comment
Share
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- End1560 Chapters
The Great Ruler
The Great Thousand World. It is a place where numerous planes intersect, a place where many clans live and a place where a group of lords assemble. The Heavenly Sovereigns appear one by one from the Lower Planes and they will all display a legend that others would desire as they pursue the road of being a ruler in this boundless world. In the Endless Fire Territory that the Flame Emperor controls, thousands of fire blazes through the heavens. Inside the Martial Realm, the power of the Martial Ancestor frightens the heaven and the earth. At the West Heaven Temple, the might of the Emperor of a Hundred Battles is absolute. In the Northern Desolate Hill, a place filled with thousands of graves, the Immortal Owner rules the world. A boy from the Northern Spiritual Realm comes out, riding on a Nine Netherworld Bird, as he charges into the brilliant and diverse world. Just who can rule over their destiny of their path on becoming a Great Ruler? In the Great Thousand World, many strive to become a Great Ruler.
8 3061 - In Serial15 Chapters
The Long and Exciting Life of Kreet the Kobold (Life 3)
The final act. Kreet has been whisked away by the Resurrection Stone to caverns she's not seen before, inhabited by wild kobolds and something else. Meanwhile Kallid and their children begin a long, perilous trek to find her.
8 209 - In Serial10 Chapters
Rhapsody
This story begins with the Fair Folk in power, so strong and cruel that it seems humans have no chance against them – until one day humans find a way. This story begins with the humans, so advanced and knowledgeable that it seems none can outwit them – until one day someone finds a way. This story begins…
8 183 - In Serial13 Chapters
Unfortunate Transmigrator
Lei Shan used to find it normal that people could ride swords to soar through the skies and destroy mountains with punches. That changed when he mysteriously remembered his previous life and realized how absurd everything around him was. Now, nothing makes sense anymore, he doesn't even know who he is supposed to be, and more questions than he can count plague his mind. To top it all off, his only ally is hell-bent on bringing destruction to himself and everyone around him. Release schedule: TBA.
8 90 - In Serial14 Chapters
The Reaper: Consumer of Souls
In a world where the strong rule, and the weak try to become strong. A 12 year old boy learns about the power that he holds. He tries to learn how yo use his power and become stronger to survive. However, life isn't always all pretty and peaceful, there is always danger. Follow the young boy as he struggles to survive with his companions and become strong enough to protect himself and the ones he loves.
8 142 - In Serial11 Chapters
He's Mine (Ayato Sakamaki x OC)
Sabrina (my oc) lived a horrible life with her family. She was forced to cause she was addressed as the Sakamaki's fiance. Sabrina was never interested in them but she then met them in person and she instantly changed her mind. After a few months of spending her time with them, she developed feelings for Ayato. He too has feelings for her but it all changed when Sabrina stopped visiting the Sakamaki household. Years past and they finally met again face to face. What will happen next?
8 141

