《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 18
Advertisement
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Writing by
Zaynab bawa
Follow on
Page 18
Wannan dare sawwama bata samu ta runtsa ba, kamar yanda taga rana haka taganshi har tsoron wayewar gari takai batayi bacci ba, gashi wani irin sauri da daren yayi mata, adaren sawwama taja Allah ya isa ma wanda ya aikata mata wanna abun yafi cikin kwando, baqin ciki da tashin hankali daya sanyata aciki kadai ya isa Allah ya saka mata, ta dalilinsane take cikin wannan fargaba da zullumi da tashin hankali, sake sakenda taringayi kenan har sanda taji kiran sallah,
Gani tayi Anyi saurin kiran sallah, daren yayi mata gajarta garin ya waye mata da wuri anata wajan, koda mama tazo tashinta ta sameta idonta biyu,
Mama batayi tunanin sawwama batayi bacci bane anata tunanin kiran sallah ne ya tasheta, da fargaba tatashi dan gani takeyi rabuwarsu ne yazo taje tayi alwala baba yajasu sallah, Addu'a kam kala-kala sawwama tayisu wasuma bata ta6a yiba amma yau sanda tayi."
Haka da gari ya waye ma gani takeyi komai sauri yakeyi mata,
Ba taso yamma tayi saboda ba taso sadam yazo har wannan magana tashiga tsakaninsu da mahaifinta ta tabbata daga wannan lokaci bazata sake sanyashi a kwayar idanuwanta ba,
Haka tawuni jiki duk a sanyaye mama da kanta ta fahimci hakan ta kirata tanata yimata nasiha akan tadauki qaddara ko wace irice,
Kuma koda ace wannan yatafi idan yaji abunda tafaru da ita Allah zai sake kawo mata wani,
Haka tayita lalla6ata."
Sai bayan anyi magrib kafinann sadam yazo, ayanda ya saba zama ya isa ya zauna,
Sawwama tana kallonsa jikinta yadauki rawa takasa gaisheshi tana addu'ar Allah yasa kar yazo sai kuma gashi yazo,
Gabantane yahau faduwa ta sunkuida kanta qasa har cikin ranta bataso zuwansaba,
Dakyar ta iya furta sannu da zuwa,
Amsawa yayi da fadin yawwa,
Daga nan dukansu sukayi shiru,
Har yanzu baki yanke shawaraba kenan?
Ya jefo mata tambaya,
Nisawa tayi cikin nutsuwa tafara magana da fadin yanzu yanke shawara yana wajan ka,
Kamar yaya awajena?
Ya tambaya amma kinsa nikam aii na sanar dake abunda yake zuciyata sannan kuma nabarki ki yanke hukunci,
Girgiza kai tayi sannan tace yanzu hukuncinka ne yarage ni nawa zakaji daga baya,
Cikin rashin fahimta yace kmar yaya? babana ne yakeson ganinka zaiyi magana dakai, ta katse zancen batareda tabashi amsa tambayarsa ba,
Toh sadam ya amsa
Ko d'ar sadam baiji ajikinsaba cewar mahaifinta yana nemnasa, yasan koda mahaifinta bai nemeshiba shi zai nemeshi, tunda yasan shi bada wasa yazoba,
Advertisement
D'agowa tayi taga yanayinsa amma sai taga babu ko alamar damuwa atattare dashi,
Alokacin ta qara tabbatarwa cewa da gaske yakeyi danta tabbata daba da gaske yakeyiba da tana ambatar mahaifinta yanayinsa zai canja,
Kallonta yayi yace baban yana inane?
Yana cikin gida tabashi amsa,
Ki sanar masada zuwana sadam ya umurci sawwama,
Jiki a sanyaye sawwama ta tashi tanufi gida tana tafiya tana kalloshi kamar wanda ya kasance kallonta na karshe dashi kenan,
Ta shiga cikin gida tasamu baba yana zaune abarandar qofar d'aki qarasawa tayi ta durkusa tana fadin sannu da dawowa baba,
Amsawa yayi yana fadin sannu sawwama,
Duqarda kanta qasa tayi tace" baba ya iso,
To madallah yana qofar gidane?
Girgiza kai tayi tace A'a yana wajan canne,
Maza je kice masa ya qaraso zuwa qofar gida,
Miqewa sawwama tayi cikin nustuwa tafice baiji zuwantaba ya nutsa cikin tunani saida tayi sallama da siririyar muryarta,
D'agowa yayi ya amsa cikin nutsuwa,
Qasa tayi da kanta tafara wasada yatsun hannunta a hankali ta furta wai inji baba ka qarasa zuwa qofar gida,
Miqewa yayi yace muje cikin nutsuwa tafara tafiya yana binta abaya,
Yarinyace qarama amma komai nata anutse take yinsa har yanda take taka qafafunta cikin nutsuwa komai nata atsare yake,
Nutsuwarta tana d'aya daga cikin abunda yake fisgarsa yakejin kullum tana qara shiga ransa,
Sanda suka kai qofar gidan sannan tatsaya tace barina shiga nayi masa magana,
Kai ya gyada tashiga ciki ta sanarawa baba qarasowarsa,
Baba bai dauki lokaciba yafice,
Atsaye yasameshi sadam yana kallonsa ya tsugunna qasa cikin girmamawa yana gaidashi,
Amsawa baba yayi cikin sakin fuska,
Yana fadin madallah mamana ta sanar dani abunda yake tafe da kai, to shine nace mata inaso mudan zanta ni da kai sai naji ta bakinka,
Waqa bakin mai ita tafi dadi, yanzu saika yimun bayani inaji duk da tayimun bayani amma zanfison ji daga bakinka,
Cikin jin kunya sadam ya sanarwa baba abunda yake tafe dashi,
Baba yace toh yanzu aina kake sannan kuma inason sanin sunan mahaifinka dakuma yanda kuke zama,
Ko d'ar babu sadam ya sanar dashi abubuwanda ya kamata ya sani gamedashi,,
Jijjiga kai baba yayi yace toh banqi takaba sadam amma baka ganin cewa kai din ba sa'an aurenta bane? Ina nufin kwarya tabi kwarya tanemi dan uwanta talaka marar galihu irinta baka ganin hakan zaifi, duba da yanda ya kasance cewa kai qaramin yarone, idan kai kagani kanaso kana ganin wajan mahaifanka baza'a samu matsala ba?
Girgiza kai sadam yayi yace baba nikam tunda ni na ganta ina sonta ai babu komai, dama kuma yanzu ina karatune baifi saura shekara daya da rabi nagama ba,
Advertisement
Idan nagama nasan lokacin bazan samu matsala daga wajansu ba amma yanzu koda naje musu da zancen ban rigada nagama makaranta ba bazasu amincewaba,
Jijjjiga kai baba yayi yace naji dad'i daka fito ka fadmin gaskiyarka,
Hakanne yasa nima yanzu zan fito nafad'a maka iya gaskiyata,
Abunda nakeso kasani shine ita Qaddara abace marar tabbas zata iya zuwa maka mai kyau kokuma marar kyau,
Qaddara bata wuce kan kowaba sannan kuma ita rayuwa daka gani kowa da irin tasa Qaddarar,
Qaddarar rayuwa mafi yawanci kowa saiya fuskanceta wasu ta kasance musu mai kyau wasu asakin haka,
Babban abun shine muyi imani akanta mai kyau ko marar kyau,
Mu sanya aranmu cewa ubangijine yake daurowa bawansa kaddarar,
Jarabawace ya jarrabeka,
Tabbas akwai qaddara mai muni data faruda mamana,
D'agowa sadam yayi yana dubansa gabaki d'aya jikinsa yayi sanyi ya qagu yaji mai akeson fada masa,
Nisawa baba yayi sannan yaci gabada cewa ba ita ta za6awa kanta hakanba, bakuma ita tadaura kanta hakanba ubangijine ya sanya wannan Qaddara ta fad'o cikin rayuwarta,
Sadam Shekarun baya da suka wuce babban al'amari yafaru da sawwama nisawa baba yayi sannan ya saukarda numfashi sannan ya furzarda iska mai zafi ga dukkan alamu abunda yakeson fadi yayi masa nauyi,
Cikin sanyin jiki sadam yake dubansa gabaki daya yanzu yashiga wani yanayi, zuciyarsace ta hau bugawa fargabarsa d'aya kada baba ya furta masa bazai iya bashi auren sawwama ba,
Baba ne yaci gabada magana, anta6a yiwa sawwama fyade shekarun baya da suka wuce,
Runtse ido sadam yayi jin yanda maganar ta dukesi,
Bai bude idonsaba yaji baba yaci gaba da fad'in,
Sawwama bata cuci kowaba kuma bata zalinci kowaba amma ita anyi mata zalinci mafi muni,
An 6ata mata rayuwarta,
Hawayene suka taru tabb a idon sadam cikin jin zafin abunda yafaru da sawwama yace baba kuma ba'a dauki mataki ba?
Babu matakin da aka dauka. Saboda koda zamu dauki mataki bamusan wayeba, koda munsan waye bamuda halin yin shari'a dashi,
Baba yadubeshi yace" sawwama tnada tarbiya tanada hankali sosai,
Tanajin zafin abunda yafaru da ita fiyeda kowa aduniyarnan, sawwama tanada kyawawan halaye d'abi'unta masu kyaune, bawai danna kasance mahaifin sawwama ba A'a duk wanda yake tareda ita zai fad'i kyakkyawan halinta."
Nafada maka wannan abunne saboda har indai neman aurenne dagaske tabbas ya kamata kasani, sirrinane nida iyalaina,
Kaje ka yankewa kanka hukunci,
Ka yanke duk wani abunda zuciyarka ta ayyana maka bazan hanaka ba zan fahimceka,
Saboda ba kowa bane zai iya daukan wannan al'amariba,
Idan ka yanke shawarar ci gabada nemanta Alhamdulillah sai muyi muku addu'a idan kuma ka yanke shawarar rabuwa da ita dan Allah ina roqonka daka dauke kafa daga wajanta dan Allah kayimun wannan alfarmar banason ganinta cikin wani hali,
Ganinka zai iya sanyata cikin wani hali,
Sannan ina neman alfarma d'aya har indai ya kasance zaka rabu da ita ina roqonka daka rufamun sirrina,
Duk duniya idan kacire ita da mahaifiyarta dani babu wanda yasan wannan zancen sai kai dana fadawa,
Inba ace yakamata kasaniba bakina bazai iya furtawa kowa wannan zacenba,
Dan Allah ka rufamin sirrina wanda ya rufa asirin wani Allah zai rufa masa nasa,
Har indai kabud'e duniya tasani kowa da irin kallonda zaiyi mata, wani bazai dauki hakan matsayin Qaddara ba, kowa da irin fahimtarda zaiyiwa lamarin,
Sadam bai iya cewa komaiba har baba yayi masa sallama yakoma ciki,
Sadam ya dade awajan dakyar ya iya d'aga kafarsa yabar wajan."
Baba bayan ya shiga gida yakira sawwama zuwa d'akinsu,
Itada mama yabasu labarin duk abunda yafaru sannan yadaura da fadin mamana inaso ki sanyawa ranki samu da rashi na Allah ne banaso kishiga damuwa ga duk wani irin hukunci dazai yanke inaso kidauka rubutaccen al'amarine duk abunda Allah ya rubuta saiya faru,
Kina zaune mijinki zai riskeki, idan kuma Allah ya rubuta cewa mijinkine babu makawa kota wani irin hali saiya zama mijinki,
A gaskiya na yaba d hankalin yaron sosai yanada nutsuwa irin mijinda nakeyi miki fata kenan akoda yaushe,
Amma idan hakan bai yiwuba inaso ki sanyawa ranki salama. Allah shi yafimu sanin abunda yafi dacewa damu,
Jijjiga kai sawwama tayi kalaman mahaifinta yasa taji sanyi cikin ranta,
Godiya tayiwa babansu sannan ta miqe tatafi,
Bayan ya fita mama tadubi baba tace duk wanda ya aikatawa sawwama wannan aiki Allah bazai barshiba.
Sai Allah yayi mana sakayya mai muni shi ya cuci rayuwarta shine yasamu cikin wannan zullumi da taraddadi,
Shine ya jefe rayuwarmu cikin tunanin zai yiwu ko bazai yiwuba. Amma babu komai Allah yana ganinsa kuma zaiyi mana sakayya,
Nisawa baba yayi sannan yace wannan haka yake, koma wayeneshi bai kyautatawa rayuwarmuba bai duba irin halinda muke cikiba ya qara jefamu cikin wani halin amma babu komai da sanin Allah."
✔️ote
Comment
Share
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial13 Chapters
World fusion: Chaos
An event of immesureable proportions took place. Our world fused with another one. The laws of the world, the geography, the living beings... Everything changed. And it was just the beginning. Nothing serious, 1 release per week at best.
8 197 - In Serial42 Chapters
Condemned
“The human body is a fragile thing. But the soul... The soul is malleable. Easily tainted. All it takes is one drop of blood to dye it all red.” Long ago, in a time remembered only by a few, the seven lords of Syvernia, led by the Great Hero Ludwig, ended the Great Calamity that plagued humanity for as long as time itself. It was the dawn of a new age of man. . . until the thirst for more poisoned the new lords. Slowly, the thread that held humanity together loosened and a thick haze consumed the lands between. Mysterious vanishings, supernatural forces, and silence warns of a looming threat inside the coat of fog. Though the struggle of the realms did not interest Leor, for he was condemned as a Purblight, until he took a seemingly simple job: escort Alden to Lightendale and collect the handsome reward, a reward that would let him live the rest of his life with ease. But it’s never that simple, especially for someone who denounced the Gods. All his life, death followed Leor everywhere he went, cutting down his friends and family. When his first love died at the hands of an agent of light, he was prepared to throw everything away until a mysterious voice promised him a chance for retribution and a chance to bring her back by completing the seven trials. Thrown into the realm's struggle against the approaching haze and themselves, will Leor, a Purblight and an acquaintance of tragedy, use the very power he disdains to accomplish his goals? This is the rewrite of my novel: Condemned; I changed it to past tense and added/ took out some ideas from the original. This is essentially the first draft since I'm writing as I go. Also, there might be or might not be Gore, Sexual, or Traumatizing content. I only put it there for a disclaimer in case I want to add it. I have no set release schedule yet, but I'll try to post once every 2 week. Thanks for your patience.
8 184 - In Serial19 Chapters
Missteps - Book Two
Adventure. Coin. Danger. Treasure. Ready to truly start their adventuring careers, the seven members of M.A. traverse more of their world. As they navigate the dangers inherent of the unknown, they're also besieged by the dangers within. Kerri's mark remains an ever-present threat, Lia's memories bring up truths she'd never experienced, Iados still can't visit the ocean for fear of being dragged away, and Jun is still out to prove himelf to his god. Who knows where fate will lead them, or what challenges will be put in their way. Book Two of this fantasy campaign-style tale has our heroes dive further into a world inspired by classic roleplaying adventures, and the unpredictabily of dice. Patreon: https://www.patreon.com/misstepsstory Discord: https://discord.gg/fQECFhBjV7 Twitter: https://twitter.com/MisstepsStory Facebook: https://www.facebook.com/misstepsstory Instagram: https://www.instagram.com/misstepsstory/
8 140 - In Serial16 Chapters
for Khiara
(Completed) poetry and prose for a girl i probably should stop writing for(Copyright © 2016 by vanillaVDE)
8 95 - In Serial11 Chapters
// Girls // The 1975
❝ 'cause they're just girls, breaking hearts. ❞ - The 1975, girlsfinished: may 1, 2014©girlwiththeredshoes 2014
8 92 - In Serial63 Chapters
Little Bit Of Trouble (Jungkook Fanfic) ✔
I had just recently lost my job, and was becoming borderline desparate. I had eaten through all of my savings and was down to my last bit of money when I got an opportunity from my best friend. He knew of a live-in position where I would be payed well to be a caregiver. I leapt at the opportunity, not realizing how big of an impact it would have on my life.❗Warning: Includes smut and adult content❗*This is an AU. In no way shape or form are any of the characters a reflection on BTS' real personalities/mannerisms/orientations. The characters are entirely a work of fiction. I do not "ship" the members in reality.*#1 littles - 5/18/18#1 little - 5/21/19#1 btsjungkook - 1/26/20#1 kpopfanfic - 6/15/21
8 298

