《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 15
Advertisement
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Writing by
Zaynab bawa
Follow on
Page 15
A hankali ta d'auke idanuwanta daga kansa gabanta yana tsananta faduwa, yayinda taji qirjinta yayi mata nauyi,
Shikam sadam bai dauke idanuwansa daga kantaba bai kuma qarasa wajanba,
Ahaka najeeb yaqaraso ya siya abunda zai siya jikinta duk yabi yayi sanyi tazuba ta miqa masa,
Kudin ya miqa mata ta girgiza kai alamun bazata kar6a6a
Da mamaki najeeb ya kalleta yana fad'in kudinkefa nake miqa miki zatonsa ko bata gane mai yake nufi ba, qara girgiza kanta tayi cikin sanyin murya tace eh nasani kabarshi kawai,
Babu yanda najeeb baiyi ta kar6aba amma fir taqi haka yataho yana mamakinta,
Yaqarasa wajan machine din yana fadawa sadam,
Sai alokacin sadam ya kauda idanuwansa daga gareta yadubi najeeb ya ta6e baki baice komaiba yahau kan machine d'insa,
Bin bayansa najeeb yayi shima yahau bai qara juyawa wajantaba ya tada mashin dinsa suka bar wajan,
Wasu hawaye masu d'umine suka zubo daga idanuwan sawwama,
Hannu ta sanya ta share hawayen fuskarta taci gabada aikinta,
Ko babu komai tadanji sanyi cikin ranta saboda ta tabbata yafara saukowane har yazo wajan dukda cewa bai qarasoba,
Koma dai yayane yau abunda takeji yadan ragu,
Share hawayen taqarayi daya qara zubowa,
Ita kad'ai tana aiki tasamu kanta da sakin murmushi,
Shikuwa sadam nasa wajan fess yakejin ransa sanyata a idanuwan dayayi kad'ai ta d'ebe masa kewarta dake addabarsa, barinma tsakanin jiya dayau, sosai ya kalli kewarsa akwance akan fuskarta,
Kamar yanda suka zo yana tuqi ahankali haka suka taho ahankali zuciyarsa gabaki daya tana cikeda annashuwa,
Sa'i-sa'i yake sakin murmushi,
Ta6oshi najeeb yayi yana fad'in lafiya kuwa?
Sadam baice masa komaiba saima qara maida masa murmushin yayi,
Ganin haka yasa najeeb yin shiru har suka isa babu wanda ya tankawa wani,
Ana shirin yin magrib sadam yakoma gida, agida yayi sallah,
Yana zaune hotonta ne kawai yake fado masa arai saiya lumshe ido yayi murmushi,
Duk da bawani magana ne ya hadasuba amma yau kam sadam yayi kwanan farin ciki,
Zafinda yakeji cikin ransa duk babu."
Itama sawwama nata wajan abubuwan da sauki yau kam,
Ko babu komai ta sanyashi a ido tasan yana cikin qoshin lafiya,
Sannan alamu yanuna yafara sauka,
Akowani irin lokaci zai iya saukowa gabaki d'aya."
Kafin weekend ya qare kullum sai sunzo amma shi daga gefe yake tsayawa sai najeeba ya qarasa,
Idan ya harde hannu akirji sai yahau aikin kallonta har sai najeeb yasiyo yadawo sannan sutafi, kuma har lokacin taqi kar6an kudinsu, ganin haka yasa najeeb idan bata kar6aba Sai kawai ya ajiye mata yatafi."
Advertisement
Ranar monday tareda najeeb suka koma school,
A school sadam yayi magrib,
Yakamo hanya, yau kam sadam da niyyarsa tazuwa wajanta koda sallama ce tashiga tsakaninsu,
Wajanta ya nufa lokacin yasameta tana tattare kayanta tagama sana'arta yaqare dawuri,
Nesa da ita ya ajiye mashin dinsa ya tattaki ya qaraso wajanda take,
Sallama yayi da sauri ta juyo jin muryarsa,
Bakinta yana rawa ta amsa sallamarda yayi mata, adan daburce ta daura da fadin ina wuni?
Lafiya ya amsa yabude baki zaiyi magana kafin ya qarasa yaji siririyar muryarta ta daki dodon kunnuwansa da fadin ya qare, ita azatonta awarar yazo siya,
Toh kawai ya amsa atakaice baibar wajanda yakeba bai kuma juyawaba yana tsaye,
Itama shiru tayi takasa aikata komai."
Tsugunnawa yayi a gabanta nan gabanta yahau dukan uku-uku
Cikin sanyin murya yace" nayi miki tambaya na nemi alfarma wajanki amma ban samu koda guda d'aya cikin abunda na buqataba,
Dafarko na dauki fushi sosai akan abunda yafaru, daga baya nazo nayi realinzing kowani mutum da irin yadda yake tafiyarda rayuwarsa,
Kowani dan adam akwai abubuwan acikin rayuwarsa,
Duk wanda kaga ya aikata wani abun na tabbata akwai dalilin aikatawa,
Bazan tilastakiba bazan takuraki akan saikin fadamin dalilinki ba,
Amma inaso kisani wallhy banida niyyar cutar dake, banida mugun nufi akanki,
Wanima bazan iya cutarwaba balle ke da haka kawai nake ganin kimarki da girmanki a idona,
Nasan akwai abubuwa arayuwa wanda suka zama sirrin mune, kokadan bazamuso wani yasaniba, balle daya kasance har yau bakisan koni wayeba, nasan wannan abune mai wuya kisake jiki da mutuminda bakisanshiba, awancan lokacin yakamata na fahimci hakan,
Amma nagaza fahimtar hakan,
Dole zanci wani iri har indai da gaske nake na damu dake iringa kallonki ahaka baki zuwa makaranta,
Bance sana'arki ko neman na kanki yazama aibuba nasan kowa da matsayinda ubangiji ya ajiyeshi,
Lokuta da dama zuciyata takan nusar dani akan narabuda ke nadaina shiga duk wani harkokinki saboda bakyason hakan amma na gaza,
Zuciyata atsarkake take akanki,
Bansan daliliba bansan mai ubangiji yake nufiba Allah yagani shine yahada jinina dake, magana bawani shiga tsakanina dake takeyiba amma Allah yasanyaki cikin mutane masu mahimmanci arayuwata kuma bazan iya cewa ga daliliba,
Kamar qanwata haka nake jinki bazanso aikata mugun abu akankiba,
Dan Allah kiyi hakuri kidaina nuna wannan tsoron nawa kokuma rashin yarda afili hakan zaisa nayi nesa dake koda banso hakanba,
Saboda duk yanda naso in kyautata miki idan naga hakan zai cutar dake dole zanja jikina,
Advertisement
Shiru sawwama tayi tana sauraron kalamansa zuciyarta take tayi mata zullumi shin da gaske yakeyi tana daya daga cikin mutane masu muhimmanci arayuwarsa? Har cikin zuciyarsa yayi wannan maganar kokuma dai kawai ya fadetane?
Amma kuma alamu yanuna mata daga qasan zuciyarsa maganar take fitowa,
Hawaye taji yafara gangara akan fuskarta,
Ganin hawaye akan fuskarta ya sanyashi runtse idanuwa yana fad'in subhanallahi wani zafi yaji acikin zuciyarsa ganin hawayenta dai-dai yakeda tarwatsa duk wani farin cikinsa, cikin sanyin jiki yace dan Allah kibar wannan kukan idan nine nayi alqawari bazan qara takura mikiba,
Girgiza kai tayi tace ni baka takuramin ba, hasalima ban dauka zam sami muhimmanci arayuwar wani irin hakaba,
Kamar yanda kafada kowani bawa da tasa qaddarar kowani dan adam da jarabawarda ubangiji yake aiko kasa,
Ni tawa Qaddarar kenna,
Zuwana makaranta bazai zama maslaha a halinda muke cikiba,
Baka takuramin kuma baka ta6a takuramin ba,
Nidai kawai banaso karinga sanya kanka cikin al'amurana dayawa, rayuwa tana da sirri, kowani dan adam yanada sirri, bai dace ace nafada maka sirinaba,
Nisawa yayi sannan yace idan bakyso nabari bazan ringa qoqarin sanya kainaba,
Amma dole in damu da halinda kike ciki,
Jijjiga kai tayi sannan tace nagode da kulawa Allah ya biyaka da mafificin alkhairi,
Amin ya amsa sannan yace har yanzu bansan sunanki,
Qasa tayi da kanta tace hafsatu sawwama,
Ma sha Allah kawai ya furta,
Ni zan tafi zan iya dawowa gobe? Ya tambaya,
Dasauri sawwama tad'aga masa kai,
Murmusawa yayi sannan yace nagode sawwama, kanta yana qasa kawai tayi murmushi,
Sallama yayi mata yatafi yayinda ran kowannensu yake cike fall da farin ciki,
Awannan ranar dukda cewa cikinsu babu wanda yasan mai yakeji gameda d'an uwansa amma dai sun san sunyi kwanan farin ciki,
Sadam koda yazo school tunanin maganganu sawwama najiya kawai yakeyi, da nutsuwa sosai atattare da yarinyar maganganunta akwai hankali aciki,
Idanta furta kalma idan kaduba zaka samesu a mazauni yanda yakamata a ajiyesu,
Najeeb ne ya qaraso lokacin sadam yayi nisa cikin tunani har yazauna baisanda isowarsaba,
Saida ya ta6ashi sannan yadawo daga tunanin yajuya ya dubeshi,
Kai najeeb ya d'aga masa yace lafiya?
Babu komai sadam yabashi amsa atakaice,
Ehem dama nasan amsar kenna babu komai babu komai,
Kullum dai zancen kennan,
Wai sadam har yanzu bamu kai matsayinda yakamata ka fadamin sirrinka bane?
Nayi shiru koda zata fadamin amma shiru kaki fada kuma nasan abun yana damunka,
Barin kashi aciki baya maganin yunwa,
Daka furtamin wata qila na iya sama maka mafita,
Kasanni sadam kasan halina bana boye maka al'amurana idan ina neman shawara kai nake fara tinkara,
Yanda na daukeka sadam ba haka ka daukeniba amtsayin dan uwa na ajiyeka wanda zan iya sharing damuwata dashi amma kai ba hakaba,
Iska sadam ya furzar sannan yace me kakeso nace maka najeeb,
Kace komai inajinka, najeeb yafad'a,
Najeeb ni kaina bansan mai yake damunaba,
Wata yarinyace
Zaro ido😳 najeeb yayi yace yarinya?
Eh lallai yace sai kuma yahau dariya,
Bata rai sadam yayi nan da nan zuciyarsa tahaura sama,
Banson rashin mutumci najeeb ina ga irinta nan kace nafad'a maka damuwtaa nafara fadi kahau yimun dariyar iskanci,
Mtseww yaja tsaki,
Dakewa najeeb yayi yace" kayi hakuri nabari,
Bata rai yayi yace shikenan ai yawuce,
Cin serious najeeb yayi yace dan Allah kayi hakuri Allah nabari,
Sanda yadan dauki lokaci kafin yaci gabada fad'in,
Wata yarinyace najeeb wallhy tausayinta nakeji tana cikin wani irin hali da zaran na ganta cikin damuwa kokuma wani abun bacci kauracewa idanuwana yakeyi
Banida aiki sai tunaninta da halinda take ciki,
Kowacce magana tafad'i takan tsaya min arai,
Nadade banji mutuminda tunaninsa ya zamanmin jikiba irinta,
Najeeb koda abun 6acin rai tayimun 6acin ran yakan shafi kowa da kowa,
Nakanji zafin kowa abu kadan akaimim zan farajin haushin mutum,
Ta dalilin son ganinta yasa nake skipping lactures,
Ranar sanda nayiwa mummy qaryan test akanta,
Nan yaringa yiwa najeeb expressing abubuwanda yakeji akanta, sannan yadaura da fadin najeeb bansan mai yake damunaba,
Bansan dalilin duk wannan damuwarba,
Jijjiga kai najeeb yayi yace wato duk wannan tarin dalilin daka lissafomin bakasan menene dalilin hakanba?
Gyada kai sadam yayi,
Miqewa najeeb yayi yana kallon zancen sadam ma rainin hankaline,
Aishi ba qaramin yaronda har zai kasa gane mai yake damunsa bane,
Kallonsa sadam yayi yana fadin ina kuma zakaje na tambayeka maimakon ka bani amsa shine zaka fice,
6ata rai najeeb yayi yace Allah sadam abunnaka harda tsantsan rainin hankali yanzu kacemun bakasan abunda yake damunkaba?
Gyada kai sadam yayi yace wallhy babu rainin hankali awannan lamarin najeeb dagaske nakeyi,
Tsantsar gaskiya najeeb ya hango a idon sadam hakan yasa ya koma ya zauna,
Yadubi sadam yace" sadam son yarinyarnan kakeyi,
Zaro ido sadam yayi atsorace yace so kuma?
Kai ina A'a."
✔️ote
Comment
Share
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial22 Chapters
Mistbound: Eternity
The world is said to be formed out of duality of man. Good and evil, right and wrong, light and dark. And with duality, comes conflict. A meaningless clash of ideals results in pointless wars. Azlan is wanderer who doesn't falls in either category. Tired and done with the redundant world, he lives his secluded life, hunting monstrosites for coin in the crumbling province of Mountaliya, situated in the land of Forsa. The premise follows Azlan as he explores the province, experiencing the culture and its people as they try to stand unshaken amidst a cold and unforgiving world. The story is a dark fantasy that is a balance of action and world building but most importantly, it follows the people going about their daily lives. The world has entered a state of stasis, there are no high stakes, no glory to be had, only a decaying realm of ice remains. Everyone awaits for Heaven's descent, an event prophesied to bring the world out of stasis, by granting the champion of the event a wish. Heaven Shall Descend. I wanted to write a high fantasy story that doesn't focuses too much on Magic and Swordfights, but rather interactions between people, a bit of politics and ideals. This is my first attempt at writing something this huge, please let me know if you see mistakes or any problems in general, so I can learn from them. (The cover picture is from the year 1818, "Wanderer Above the Mist" by Caspar David Friedrich). I also write Short stories set in the same shared universe. You can read them here: Dark Fantasy Short Stories.
8 172 - In Serial12 Chapters
Cata Maestra
Hey. I'm Maestra.Life sucks. It's a fact everyone knows, and something I've experienced twice. But want to know something else?Death sucks even more. Especially when you're alive to remember it, and only it.And that's the only thing that keeps me going. ----------------------------------------------------------------- Yo, welcome to my first attempt at making a story. Feedback would be very highly appreciated, so feel free to leave criticism where you see fit. Also posted on ScribbleHub!
8 130 - In Serial36 Chapters
Summoning Our Country - NHS Kai
CONTENT WARNING: Japanese ultranationalism, language, gore depictions, obscene scenery Off to the Orient lay a massive ocean that separated the bellies of the great continents of Eurasia and the Americas. In between the global juggernauts that were the United States of America and the People's Republic of China was a state home to 120 million people and the world's third largest economy. But things often don't go as hoped. The nation of Japan suddenly wakes up to the heavens above them having been rewritten in what seemed like divine premonition. A familiar, yet otherwise alien world awaited them beyond the shores that had kept them safe. As the vices of globalization threatened to wreck havoc and condemn the Japanese state into obscurity, it was up to newly elected Prime Minister Takamori Hideaki and his administration to face this challenge of epic proportions. Paying homage to みのろう's Summoning Japan (Nihonkoku Shoukan, NHS) as a fan-made work, this story will also follow Japan, but explores a completely different world. Now helmed by a named Prime Minister, Japan will wade the murky waters of the new world as it struggles to come to terms with its issues. Also available on Wattpad, Scribble Hub, and Fanfiction.net
8 233 - In Serial21 Chapters
Monarch of the Darkness
The heir of the darkness is bornI am different as I am uniqueNo one can stop nor suppress meEven when there is no hope nor wayI shall not falterAs I am HaydenMonarch of The Darkness-----This is the story of a human from earth who traveled through space and time and arrived in another world. He was different from anyone as he couldn't progress in the same way as the others. With the help of a mysterious system, he overcame his difficulty and started a new journey to become the strongest in the world. I will be posting this original story on webnovel.com and Royalroad.com
8 172 - In Serial18 Chapters
The Dragon Fiend
A young orphan addicted to xianxia novels receives a jade pearl and three throwing knives in a pawnshop and killed and reincarnated by a dragon god. He appears in the middle of a civil war and resurrects in the body of a dead son of one of the martial families. Watch his journey from an orphan to a martial expert aspiring to be an immortal.Volume 1: Prologue-Chapter 14
8 88 - In Serial11 Chapters
the dungeon that made me
Two best friends get stuck in a dungeon and are forced to kill all monsters to survive. This is a story of Ranmaru and Sasha snd how life is like in a dungeon.
8 103

