《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 8
Advertisement
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Writing by
Zaynab bawa
Follow on
Page 8
Cincin rundon jama'ane na gaske sannan kuma ba qananun mutane bane,
Gabaki d'aya suna tsaye jiran fitowar Haliifa kawai sukeyi, burin kowanne daga cikinsu haliifa yafito su ganshi ya samu lafiya,
Kowannensu ya maida hankalinsa wajanda mutane suke fitowa,
Gadonda haliifaa yake kwance aka fara turowa aka fito dashi daga cikin jirgin,
Sai umma agefen sa tana biye dasu, ummi da ruma suma duka suna biye dasu abaya,
Farin cikin da yake tattare da wad'annna mutane da sukazo taryansu ganin a irin halinda aka dawoda haliifa dukansu sai murnarsu ta koma ciki,
Dogara dake gefe suna kallon fitowarsu sukayi saurin qarasawa Wajan jikin gadon suka zazzagaye tako'ina suka rufeshi ruff yanda babu mai iya kallo abunda suka zagaye,
ahaka sukayiwa gadon jagora har izuwa bakin motar za'a shigardashi,
Wasu daga cikin mutanen airport din suka tsatssaya suna binsu da kallo saboda ga dukkan alamu wani babban mutum ne ya iso, kuma bamai cikekken lafiyaba,
Wasu sun tausayawa masa yayinda wasu suke alhinin komai yasameshi,
Wasu daga cikinsu sun san waneneshi saboda koda ganin wad'annan mutanen sun san yareema haliifaa kuma sunsan kwanakin baya ya haduda ciwo,
Wanda suka sanshi daga cikinsu sun tausayawa masa saboda sanin wanene haliifa dasukayi,
Halinsa mai kyaune baida mummunan hali, bai kumada girman kai ko wani jijji dakai,
Mutum ne mai sauqin kai
Shikuwa bai shiga harkan wani,
Zaiyi duk wani iya qoqarinsa na ganin cewa bai shiga hakkin waniba,
Amma yau shine cikin wani hali aciwonda ankasa gano kansa gabaki daya,
Rufe wajan sukayi gabaki daya har aka gama shigarda shi mota,
Sannan su umma kowa yashiga mota aka rurrufe,
Dogarawa kuwa suma nasu motocin suka shiga,
Duk da kasancewar kowani mota daya akwai dogari agaban motan dakuma drivern motan,
Daganan motoci suka d'aga sai cikin fada,
Advertisement
Acanma tako'ina ana jiran isowarsune suna shiga umma tabada umarni kai tsaye awuce shashinta,
Can suka wuce daga nan aka shigarda haliifa izuwa bangarenda yake tun kafin tafiyarsu,
Suma su umma suka shige domun hutawa."
Cikin d'an qanqanin lokaci labari ya karade cikin masarauta kaff akan dawowarsu haliifaa,
————
Macece mai cikakkiyar izza, isa dakuma d'agun kai yanayinta kadai ya isa ya nuna jiji dakai dake tattare da ita,
Akishingud'e take jikin wani d'an tuntu idanunta yana lunshe,
Shigowa d'akin jakadiya tayi da dan saurinta ga dukkan alamu maganace abakinta, tsugunnawa jakadiya tayi agabanta tana fadin takawarki lafiya ranki shi dade, Allah yaja kwana yaja zamani, uwargida wajan sarki, Allah yajikansa, mahaifiyar magajin gari,
bude ido wannan matar tayi ta dubeta sannan ta maida idonta ta lumshe ga dukkan alamu taji dad'in wannan kirari da akayi mata, amma bata nuna hakanba,
Jakadiya taci gabada fad'in"
Ranki shi dade' yarima halii,,, saurin d'aga mata hannu wannan matar tayi lokaci daya alamun 6acin rai ya bayyana a fuskarta,
ganin haka yasa jikin jakadiya yadauki rawa atsorace tafara fad'in agafarceni ranki shi dade.
Hannu kawai ta qara d'aga mata alamun ya isa haka,
tsawon lokaci batace komaiba itama jakadiya tana tsoron taqara magana tayi laify,
Tsawon lokaci jakadiya na zaune awajan
Kai kace ta manta cewa da mutumi kusa da ita amma sarai tana sane batajin maganane alokacin kawai saboda dan 6ata mata rai da jakadiya tayi,
Kuma dama koda ba'a 6ata mata ranba takanyi fiyeda hakama,
Jakadiya kuwa tayi shiru tana sauraron wannan mata jira takeyi abata izinin magana amma shiru,
An d'auki tsawon lokaci kafin tasake bude idonta ta maida taqare lumshesu,
Jakadiya harta cire ran da za'ai mata magana kawai sai can tajita tayi magana cikin izza, isa, sarauta, dakuma mulki kamar wacce take tsron buda bakinta tace" maike tafe dake?
Jadakidaya jin an tambayeta yasata saurin fadin ranki shi dade,
Advertisement
Haliifa sun dawo yanzu,
Saurin bude idanuwa wannan matar tayi tana kallon jakadiya,
Neman qarin bayani takeyi jakadiya tagane hakan yasa taci gabada fad'in,
Tunda naji alamun shigowarsu cikin masarauta naje na tsaya a hanyarda zata sadani da sashin mahaifiyarsa,
Mtseww wannan mata taja wani dan siririn tsaki saboda bayani takeso kai tsaye bawai atsaya jan lokaci ba,
Ganin takosa yasa jakadiya saurin dukar dakai tace"
Allah ya huci zuciyarki ranki shi dade amma yanda aka tafi dashi haka aka dawo dashi,
Jijjiga kai tayi alamun taji dad'in zancen sannan tayi mata alamun akan tatafi,
Tashi jakadiya tayi tatafi tabar wannan matar cikin farin ciki."
—————
Mai martaba yana zaune acikin d'akinsa,
Babbane sosai domin tsufa takamashi,
Ta bayyana ajikinsa, Qur'ani ne abude agabansa da dukkan alamu bai dade da gma karantashiba,
Yana zaune akan sallaya carbine ahannunsa yana lazumi,
Sallama akayi daga qofar d'akin ya amsa sannan yabada umarnin shigowa,
Shigowa tayi tazauna agefensa, itama dai tsufar ta kamata ga dukkan alamu matarsace,
Sanda ya idda abunda yakeyi sannan ya rufe qur'anin gabansa ya juyo ya dubeta,
Sannu da hutawa tafad'i,
Amsawa yayi sannan tadaura da fad'in,
Ranka shi dade yarima haliifa sun iso tun d'azu labari ya iskeni shine nace bari naje induba jikinnasa,
Nisawa mai martaba yayi sannan yace"
Jiki kam sai Godiyar ubangiji,
Yana fad'in haka ya miqe tareda alqur'aninsa zai maidashi mazauninsa,
Wajan littafai ya nufa kala-kala na addini ya ajiye qur'anin amazauninsa daban,
Miqewa itama matar tayi had'eda fad'in
Bari na shiga wajan yarima na dubashi,
Da kai ya amsa mata,
Hanyar fita ta nufa saboda taga alamun kamar bayason hayaniya,
Fita tayi ta wuce shashin umma,
Itada muqarrabanta,
Acikin falon umma sukayi masauqi,
Sannan jakadan da suke shshin suka shiga sanarwa umma da zuwannasu,
Fitowa umma tayi cikin ladabi ta zube gaban wannan matar tana kwasan gaisuwa,
Amsawa matar tayi ta tambayeta hanya da jikin yarima,
Amsa mata umma tayi da fad'in jiki Alhamdulillah,
Yanzuma haka yana bacci ne,
Jijjiga kai tayi sannan tace babu damuwa dama nazone kawoi nayi muku gaisuwa,
Allah ya qara masa lafiya tafad'i,
Amin umma ta amsa,
Sannan suna tashi suka tafi."
——-
Kusan duk wanda yake cikin masarautannan labarin isowar yarima haliifa ya iskeshi amma kuma wannan mata ita d'ayace ta taka sashinsu dan duba jikinsa,
Sai mai martaba wanda kullum dare sai ya tafi can tsawon lokaci yake eba yanayi masa adduo'i
Hakan yasa tunda suka dawo jikin sai yafi nacanma sauqi saboda bai sake attempting dukan wani ba,
Wannan kennan,
Mai martaba mutum ne shi mai addinin gaske,
Allah yabashi ilimi sosai babban malamine,
Idanda wani abunda yakeso fiyeda komai a duniya shine haliifa,
Saboda ko cikin matansa yafison kakar haliifa, Allah yayi mata rasuwa,
Haka cikin yaransa kaff yafison mahafin haliifa,
Shima Allah yayi masa rasuwa,
Haliifa kawai yake kallo yaji sanyi, saboda kallonsa yakan tuno masa da matarsa dakuma dansa, sonda yake yiwa matarsa da d'ansa saiya tattaro yadawo kan jikansa,
Kuma haliifa dik cikin jakannunsa yafi bashi kulawa, yafi yarda da hankalinsa da nutsuwarsa addni da iliminsa,
Halayensa na kirki yasa yaqara shiga ran mai martaba,
Kwatsam sai wannan rashin lafiya tazo tasamu haliifa,
Baqaramin tashin hankali mai martaba yashigaba,
Yanzu haka matan mai martaba biyu,
Yaransa kuma duka yanzu matane biyu maza amma duka mazan sun rasu, ahatsarin mota,
Mahaifin haliifa yabar d'a daya kacal haliifa,
Yayinda dayan kuma yabar yara biyu duka maza,
Wannan kennan,
Mai martaba ya dagewa haliifa sosai da addu'a har takaiga yanzu ko alamu ajikin haliifa bazaka gani cewa baida hankaliba,
Sai dai kawai baya magana baya kula kowa,
Idan zaka shekara kana masa magana baisan mai kake fad'iba,
Shi dai gashi nanne kamar mutum mutumi."
✔️ote
Comment
Share
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial37 Chapters
Avaunt
Cheis of Veraleigh the Necromancer is a hero renowned throughout the realms, but that doesn't mean her social life is doing all that well -- she'd rather hunt monsters and write new spells than deal with the unpleasant reality of her impending middle age. But when an ancient evil awakens, she just may have to make up her mind about what she wants out of life -- and deal with what life wants out of her.
8 237 - In Serial13 Chapters
Evolution Barricade
Kaden barely had a life; from a young age, he watched and studied diligently but failed to go anywhere in his life. An avid fan of isekai manga, he densely throws himself in front of a car when he's told he'll be living on the streets! The gods spare him but he soon finds out why - he's being given his very own miniature hell, doomed to be... a barricade! Kaden will be tasked to stop people; the more successful he is, the more he levels up and curries favor to grow. From a humble row of thorny grass, just how far will he go as a barricade!? Evolution Barricade is no longer active! This is because it served as the basis/concepting for another series I write, known as STEM: The Topical Dungeon. If you liked Evolution Barricade, please check it out here!
8 226 - In Serial181 Chapters
Forsaking Reality
I am a genius. My talent for fighting is peerless, yet my talent for destruction has reached the pinnacle. My family is gone. My friends are gone. Those dearest to me are gone. Everyone I know and love are gone. And yet I... I remain. For I am the sucessor to life. Yet, I will also be the one to end it. Current Release Schedule: At least 4 a month
8 160 - In Serial11 Chapters
Abhorrence
Set in a dystopian semi-futuristic world that is on the brink of collapse, in a time of great civil strife and unrest. Callum's world is flipped upside down as his awakening thrusts him into an unfamiliar world that abhorrently rejects him. New chapter every day around 10PM, often not on time though
8 104 - In Serial10 Chapters
Our Secret Affairs
Marinette Dupain-Cheng, in love with Chat Noir, in love with Adrien Agreste. At a party at the bourgeois mansion, she has an affair with Adrien Agreste. A secret Affair. It was forbidden, little do they know, their not the only ones keeping a secret.
8 81 - In Serial21 Chapters
I Reincarnated Into a Fictional Character
Asher is a simple guy bored with his life. He enjoys reading web novels about xianxia, wuxia, and the like. One day he decided to write one, just for fun. Midway the novel he became sick and died. When he woke up, he found out he was reincarnated as a fictional character in the novel he wrote. Since he was the one who created this world, will he survive it? Will he finish the story he started?
8 256

