《ƘADDARAR RAYUWA》Q page 7
Advertisement
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Writing by
Zaynab bawa
Follow on
Page 7
Wata matashiyar mata ce mai cikeda kamala azaune a palour wacce bazata wuce 45yrs ba duk cikar zatinta da kamalarta, da sauqeqqen yanayi da yanuna ajikinta amma hakan bazai hana kana kallon wannan matar ka hangi damuwarda take tattare da ita qarara ba
alamunta yananun hankalinta atashe yake kokuma tana tattare da wata cikekkiyar damuwa,
Tayi nisa cikin tunani sosai tadaura hannuwanta ta tallafo fuskarta tayi tagumi, sosai ta nitsa cikin kogin tunani
Har suka qarasa shigowa palourn batasan sun shigoba saida wata yar budurwa ta qarasa kusada ita ta ta6ata tana fad'in umma lafiya kuwa?
Tunda muka shigo hankalinki baya jikinki gabaki daya,
Wani abunne yafaru??
Babu komai ruma! Tafad'i atakaice,
Zata qara magana wacce suka shigo tareda ita ta katseta da fad'in A'a ruma kada kija zancen,
Kefa kanki kinsan tatsuniyar gizo bata wuce ta qoqi,
Zaunawa kusada ita ruma tayi tana fad'in nasani ummi,
Sannan ta sanya kanta akan kafad'ar matanda take zaune tace" umma dan Allah kiyi hakuri kisawa ranki sanyi,
Kowani dan Adam da kika ganshi da tasa qaddarar mukuma tamu qaddarar kennan tanan Allah ya jarabcemu,
Nasan dole mu kasance cikin damuwa amma umma damuwar idan tayi yawa sai tazo ta haifar mikida wani ciwon ayi d'a kwance uwa kwance,
Umma kiyi addu'a kawai Allah zai fiddamu,
Nisawa wanda aka kirada umma tayi sannan tace ruma abun yana damuna,
Kullum ciwon halifaa gaba yakeyi baya raguwa,
Yanzu tsawon watanmu shida anan qasar magani anayi kamar ba'ayi, yanzu kiduba abunda yafaru shekaran jiya ban ta6a tunanin faruwar hakan ba, saboda bai ta6a aikata Wani abun makamancin hakaba,
Kinga kuwa abu gaba yakeyi,
Hawaye yana gangarowa akan fuskarta tace Allah mun tuba Allah ka yafemana,
Allah kajikan wannan bawa naka kabashi lafiya,
Advertisement
Tana kuka taci gabada fad'in
Wato shi halifa tasa QADDARAR RAYUWAR kenan?
Shekaru biyu baya babu wanda yata6a tunanin faruwar hakan,
Sanya tissue tayi tashare hawayenta
Sannan taci gabada fadin yaro mai cikeda nagarta kuzari dakuma jarumta yanzu shine ya dawo haka,
Taqarashe magana hawaye yana qara bin kan kumatunta,
Qarasowa waccar matan danaji ankirada ummi tayi tana fad'in yahyah kiyi hakuri ki daina kuka in Allah yayarda Haliifaa zai samu lafiya,
Mudai muci gabada addu'a Allah yana gani zaiyi mana maganin komai,
Jijjiga kai umma tayi na gamsuwa da maganar yar uwar tata tace,
Hakane sadiya amma ace samada shekara biyu kennan ana abu daya bbu canj?
Yanzu asibitoci wani irine bamu zagaba?
Hannu ummi tasanya ta shafa kafadun umma sannan tace" hakane yaya amma ai kinsan shi magani dacene,
Idan Allah yasa sai kiga andace,
Hakane umma ta amsa sannan tace shikenna Allah yabashi lafiya,
Amin su duka suka amsa,
Kushiga kushirya muwuce asibitin,
Toh suka amsa sannan duka suka miqe zuwa ciki,
Cikin qanqanin lokaci suka gama shirin suka fito,
Umma kam dama ashirye take dan haka suna fitowa suka fita zuwa wajan mota,
Driver wanda yasanda fitar dama yana jira suna fitowa ya bude musu qofa shiga sukayi kai tsaye yawuce dasu asibitin,
Bayan sun shiga asibitin kai tsaye suka wuce ward din
Wani daki suka mufa mai kyau sosai ga dukkan alamu bakowani marar lafiya ake kwantarwa awanan d'akinba,
Da sallama suka shiga dukda kasancewar sunsan bawai zasu sami amsa bane,
Azaune yake akan gadonsa na marassa lafiya idonsa yana kan qofa,
Suna shiga yafara binsu ta kallo d'aya bayan d'aya kamar maison gano wani abun tattare dashi,
Umma dasauri tanufeshi tana fadin yarona nayi kewarka sosa,,,, bata qarasaba taji an qireta juyawa tayi domin ganin wacce tariqeta sai taga ummi,
Girgizaka mata kai ummi tayi sannan tace yaya kada ki qarasa kusa dashi kizauna daga nesa,
Advertisement
Kokin manta abunda yafaru shekaran jiya?
Jaa da baya umma tayi ta tsaya tana tunano abunda yafaru shekaran jiya,
Shaqeta halifaa yayi dakyar aka kwaceta,
Hawayene ya zubo mata ganin danta kusada ita amma babu halin taqarasa kusadashi,
Zama tayi akujeranda take facing dinsa, kallonsa takeyi cikin tausayawa,
Hannunsa tabi da kallo chain ne ad'aure a hannun wanda suke saqale ajikin gadon basuda tsayi yanda bazaiyi nisan zangoba,
Saboda tsayinsu iyakaci walwalarsa jikin gadonne,
Hawaye yana zuba a idonta tafara fadin sannu haliifaa sannu,
Allah zai baka lafiya in sha Allah
Binta da kallo kawai yakeyi amma baisan mai take fadaba,
Saboda babu hankali ajikinsa, da dukkan alamu kansa yana ta6e, yana famadq rashin hankali,
Amma yanayinsa bai nuna hakanba, kayan patients ne ajikinsa bbu alamun qazanta ko wani abun haka,
Amma kuma dai kasan bai cikin hankalinsa,
Umma tana kallon sa batasan lokacinda hawaye yake zuba a fuskarta ba,
Ruma ne taqaraso tana fadin umma wannan hawayen kidaina zubdashi,
Nasan koda yaya haliifaa yana cikin hankalinsa baya son ganin hawayenki, yanzuma nasan saida baida halin fadi amma hakan bazaiyi masa dadiba,
Ummi ne tace yaya wannan jarabawace kuma kaddarace dan Allah kiringa daure zuciyarki.
Tsowon shekaru biyu ace ana abu daya amma kin kasa kwantarda hankalinki,
Babu abunda Allah bai bamu ba bbu ta yanda ya ragemu ,
Idan kika duba tako ina Allah yayi mana budi mulki da dukiya, ilimi dakowani fanni, duk wani abunda mukeso arayuwarnan zamu sameshi har indai dukiya zata iya badashi, har in kuma ilimi zai badashi toh munada shi kokuma zamu sameshi,
Amma kuma saiya dauke mana abu daya acikin zuri'armu wanda yayi hakanne ya jarabcemu ya nuna mana dukiya ko ilimi da muke dashi bazai siya mana komaiba,
Dukiyarmu takasa samawa yaronmu lafiya abunda zamuyi shine kawai mu komaga ubangijinmu mu roqeshi shine zai fiddamu daga cikin quncinda muke ciki,
Sannan kuka bashi zai bashi lafiyaba,
Yaya dan Allah kizama mai dauriya,
Toh umma tace kawai,
Suna zaune wajan kusan 2hour saiga doctor yashigo shida wani dan matashi wand bazai wuce 35years ba,
Qarasa shigowa sukayi shida likitan
doctor ya qaraso suka gaisa da umma,
Shikuma wannan mutumin ya tsaya wajan ummi sukayi magana sanda suka dan dauki lokaci har doctor yagama abunda zaiyi yafita,
Sannan yaqarasa wajan umma da takardu ahannunsa.
Gaida umma yayi cikin ladabi sannan yace hajiya duk wani shirye-shirye daya kamata anyishi yanzu haka wad'annan takardunne zuwa jibi in sha Allah zamu koma komai ya kammala.
Miqawa umma takardun yayi tasanya hannu ta kar6a,
Nuna mata yanda zata sanya hannu yayi ya kar6a ta sanya tamiqa masa ya kar6a yafice,
Awajan suka wuni zubur sai magarib suka koma gida,
Akwana biyu suka gama duk wani shirye-shirye na komawa kasarsu,
Washe gai jirginsu zai tashi zuwa gida,
Ummi da ruma ne sukayita shiga kasuwa wajan sayayyar abubuwanda zasu buqata,
Ita kuma umma tana gida ko asibiti"
Washe gari da safe jirginsu yatashi bayan anyiwa haliifaa allurar bacci na iya tsawon awanninda zainkaisu gida,
Ahakanma sanda suka taho da nurse mai duba lafiyarsa,
Tunda suka tashi har jirginsu ya sauka bai tashiba."
Bayan sun sauka motoci nagani masu yawan gaske sunzo taryansu,
Kowanne kagani acikin jama'arda suka zo taryansu fuskarsa cikeda fara'a da dukkan alamu jama'ar suna daukin ganinsu."
✔️ote
Comment
Share
Follow
To be continued
Zaynab Alabura
Advertisement
- In Serial20 Chapters
A Queen of Ruins
Some people just want to watch the world burn. I'm not one of those people. Some people see the world as something to be saved, and brought to heights never before imagined. Again, not me. What kind of person am I? I'm a Queen, plain and simple. Lots of people, noble and commoner alike, often complain about life being a cruel mistress, or something similar. When I hear those complaints, I can only laugh, or look at them in contempt. Life is simple, you only need to let yourself take the path you are meant for. Me, I was born a bastard, lived with my mostly sadistic half-siblings, among people who thought I was naturally inferior. And look at me now. *********** I do not claim ownership of the picture
8 185 - In Serial19 Chapters
Interview With the Hattoris
Yuko Hiragi is an aspiring journalist. She goes about her internship with hopes of scoring a big scoop so that she can be set with a nice job after she graduates college. When she gets an opportunity to interview the corrupt and powerful Jensen Skagg, her dreams of fame become dashed when he is murdered before her eyes by a mysterious assassin. She is soon thrust into the dark world of murder and intrigue as she is hosted by the ancient and powerful Hattori family.
8 129 - In Serial9 Chapters
The First's Apostle
Another one down. He wiped the sweat from his brow, once again cursing his luck. Out of anyone, this had to happen to him... Michael had just gotten his shit together, he even went back to getting an education. Just a normal sixteen year old boy. Now he was sent to the middle of fucking nowhere, to fight things that didn't exist. Hell, he wasn't even sure he was allowed to be here. The goddess wasn't exactly being secretive about that. Probably another way to have him depend on her. She had him in the palm of her hands and he wanted to jump off. He knew he'd be dead without her help though, just for now he had to play along. He had to follow orders.
8 402 - In Serial7 Chapters
Conquest
Out of nowhere and a time that no one could remember, the dungeons came to be. Bringing with it wondrous new into the world but also equally dangerous terrors lurking within its corridors. Of the countless said to have spawned from nowhere, 5 had risen to the challenge against the human species. The rest destroyed due to their own weakness, only these 5 still stand in this era and each ruled by 1 great family. And now, a fresh adult male would soon join the exalted ranks of those that brave the dangerous corridors of the dungeons. Aiden Smith, the soon to be a S ranked Adventurer. If only that was true, perhaps life wouldn’t be so hard. Inspiration from domain warz and phantasmal party , very irregular releases and my first release, let the criticism begin! Pics not mine.
8 63 - In Serial6 Chapters
Precisive hunter
David goes to bed after a depressing day grieving over a lost friend, however he wakes up to a new world with magic, a system, and more! Note:The Title is a placeholder. The Picture is a placeholder. I am not a professional writer, please critique the series as you see fit. This is probably going to be a cliche dumpster fire. Thanks for any support. Word count per chapter: 1000 - 3500.
8 171 - In Serial43 Chapters
Chosen [Gift]
A fantasy world, Odessia. The God-dess of this world grants every single person with their very own [Gift] at the age of 7, giving them a skill or ability to shape their paths in life around. One young boy gets everything taken away from him when he's given the only [Gift] that the very religious nation of Enradica sees as the highest of blasphemies: [Choose Your Own Path]. In a different world a woman reads the future of the boy, and becomes the God-dess's angel in order to change his fate, even at the cost of her sanity. This is the story Noth and his angel, in their struggle for survival against a crooked theocracy.
8 198

