《ƘADDARAR RAYUWA》Page 4
Advertisement
QADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Zaynab bawa
Follow on
Page 4
Da asuba babansu da kansa yatashesu suyi sallah,
harda qananun yaran kowa sanda yatashi babansu yajasu sallah suka gabatar, addu'oi yaketa yimusu kala-kala akan Allah yakawo musu dauki cikin lamarinsu dakuma kariya cikin rayuwarsu, byan sun idarda salla sauran kuma suka koma d'aki itakuma tafito tafara share-share na gida da wanke-wanke da sauran ayyuka kafin mahaifiyarta tafito tagama komai halima tana tayata suka hade cikin gidansu tass,
Dama daii sukam ba daga nanba sunada talauci kam gashi gidannasu na talakawane kurmus amma sunada tsabtar gaske komai masu ataltale yake,
Duk rashin kyawu na gidan amma idan suka shareshi suka taltaleshi saiya baka sha'awa."
Mamansu tafito lokacin suna surfa gero wanda zasuyi kunun karyawa,
Sannu tayi musu suka gaidata sanna sukaci gabada aiki, kicin tawuce sun shareshi tass-tass sun daura ruwan zafi akan wuta,
Suna gama surfawa suka bushe suka wanke,
Barshi sukayi yadan bushe sannan suka dakeshi cikin qanqanin lokaci suka gama,
Aka dama kunu mamansu tabasu naira ashirun suka siyo sugar,
Dalam-dalam haka sugan tayiwa kunun amma ahakan sukasha domin rabonsu da samun karyawa mai kyau kamar hakama an d'an dauki lokaci,
Sai dai idan babansu yasamu ciniki mai kyau sannan ya siya musu koko da qosai na karyawa."
Da wuri mama tagama shirinta tsaff na fita anguwa da hindatu kawai tafita tabar sauran agida sanda taja kunnen sawwama akan takulada qannenta,
Sannan ta jaddada mata akan kada tabarsu da yunwa dukda tasan cewa bazata barsunba amma taqara tunasarda ita, akan ta dafa musu shinkafa,
Tana fita kuwa kamar jira sawwma takeyi tashiga dakinda babansu yake ajiye baronsa yadauko baqar leda,
Shinkafa ta gwada tiya biyu tafice, domin aiwatarda nufinta da takwana dashi cikin ranta,
Shago tatafi can ta aunar sannan ta auno mudun waken suya da duk wani abunda zata buqata tadawo gida,
Gyara waken tayi takai markad'e ta tace tadaura, wasu dan lokuta kadan tahad'e awaranta, tazauan ta soya, miyar jajjage tayi ta zuba akai ta juye a bokiti tafita,
Advertisement
Aqofar gida tazauna dake gidansu bakin titine hanyar wucewar jama'ane, kuma akwai shaguna agefen titin,
Lokaci kadan tadauka tafara ciniki, lokacinda baifi awa biyuna gefen gidansu akwai almajirai, haka sukayita siya mai goma mai biyar tana zaune anan harta siyar aqofar gida bata motsa ko'inaba,
Batayi zaton qarewarsa dawurina amma ganin yaqare yasanya,
Bata zaunaba takoma kasuwa ta auni wanda yafi nada yawa,
Abinci tafara daurawa qannenta domin gargadin mahaifiyarta tadace kada tabarsu da yunwa,
Dake tanada zafin nama wajan aiki, lokaci qalilan tadauka tagamawa qannenta abinci, sannan tafara aikin awara, har yamma taci mata bata gamaba,
Tunani tafaryi tasan har indai tayi tazuba cikin bokiti irinna datsu ba lallai tayi ciniki ba saboda yamma tayi, wata dabarace tafado mata dan haka tahad'a murhu aqofar gida tafara suya,
Abundai alhmdllh sai dai ace sam barka tafara ciniki dake wajen akwai karancin masu abun siyarwa, kuma akwai yawan shagunaan sana'a, har magrib ta risketa awajan tana suya tana cinikinta.
Dake baba shima yafita dawuri bai san mai yake faruwaba,
Yafice zuwa gidansu daga nan yabiwa mama yagaida nata mahaifan, sannan suka kamo hanya,
Ana kiran magriba mama da baba suka doso layinsu daga nesa suka hangi sawwama zaune bakin murhu da yara akanta suna jira azuba musu,
Ganinta haka mamaki ya kamasu babu wanda ya'iya magana acikinsu suka shige ciki,
Ita kama batama luradasuba kanta yayi zafi wajan saida awara,
Sanda taga anfito a sallah sannan tatura yaro yakira mata halima zata dawo yin sallah,
Halima tafito ta kar6eta, ita kuma tatashi tanugi gida da sallama tashiga gida kanta tsaye batareda wani tunaninba,
Aqofar d'aki ta samesu alamun sun idda sallah, gabantane yafadi ganinsu sun dawo dan batayi zatoba, ad'arare ta qarasa kusa dasu tana fad'in mama, baba sannunku da dawowa,
Sannu baba ya amsa, mama kuwa batama kulataba dauke kanta tayi daga kallonta, sawwama tana kallon yanayin mama jikinta yayi sanyi sosai, babane ya katseta da fadin je kiyi sallah kidawo zamuyi magana,
Miqewa tayi har tana tuntu6e ta dauki buta tashiga bayi tayi tsarki tafito tayi alwala ta gabatar da sallah,
Advertisement
Koda tadawo agefe tazauna cikin nutsuwa tace" baba gani"
Kallonta yayi cikin nutsuwa yace" mamana me nake gani?
Mamana tallan kika koma yi?
Mamana bakiga illar wannan tallar bane?"
Mamana talla tayiwa rayuwarki illa amma baki fahimci hakanba, mamana kinason qara jefa kanki cikin wani halinne?
Ko shawarata kona mahaifiyarki baki nemana lokacinda zaki fara wannan abun,
Mamana idan abunda nake kawo muku yagazane zan qara qoqari,
Nasan hakuri kawai kukeyi da duk wani abunda nake kawo muku,
Zan qara qoqari inakawo muku fiyeda na baya,
Mama wacce tunda baba yafara magana batayi maganaba sai yanzu tace"
Aiso take ta nuna cewa iyayenta sun gaza sun kasa daukar d'awainiyarta bari tafita itada kanta ta nema,
Mama taqarasa maganar cikin zafin raii,
Girgiza kai sawwama tahauyi hawaye na zuba a idanuwanta,
Cikin muryar kuka ta zakud'a kusada mahaifanta tafara fad'in,
Baba dan Allah kuyi hakuri wallhy ba nufinaba kenan,
Baba kokadan ban raina abunda kake kawo manaba,
Baba a kullum tausayinkane cikin raina jiya ban iya runtsawaba saboda tunanin halinda jiya kadawo aciki,
Baba banyi haka dan 6acin rankaba nayi hakane dan taimakonka,
Juyawa tayi wajan mama tace mama dan Allah ku yafemin,
tana fadin haka taqara sanya kuka bata ta6a tunanin cewa mahaifanta zasu dauki zancen hakaba da bata faraba, dan babu abunda taqi jini irin 6acin ransu,
Kukanda takene yasanya duka jikinsu yayi sanyi koda bata fadiba sun san halinta sun san halin d'iyarsu sunsan sawwama bazata ta6a yin haka danta nuna cewa mahaifanta sun qaza ba, tayi hakanne kawai danta taimaka musu, amma dole su nuna 6acin ransu saboda ta fahimci halinda takeson jefa kanta aciki,
Da halinda tafad'a abaya, sannan su sanya mata tsoron wanda zai faru nan gaba,
Jikinsu yayi sanyi sosai suka gaza magana
Ido kawai suka tsira mata tana kukanta babanta yarasa mai zai furta shidai yana tsoron yaqara barinta talla akaro na biyu,
Dakyar ya'iya daurewa yafara fadin naji na fahimceki mamana, ina gudun qara faruwar abunda yafaru abayane, saboda kowani mahaifi zaiso kare d'iyarsa kada wani abun yasameta, ni nagaza akaro na farko banso nakara bari wani abun yasameki, tunda kinga ni nakasa kareki kiyi haquri ki taimakeni wannan karon na kare rayuwarki,
Zuciyata bazata iya juran wani abun yaqara samunkiba."
Girgiza kai kawai sawwama takeyi,
saida tadan tsagaita kukan sannan tafara fadin mama baba kuyi hakuri dan Allah ku yafeni bazan sakeba,
Tausayintane yaqara kamasu,
Har cikin zuciyar mama take tausayin diyarta kuma tana sonta sosai akullum takalli d'iyarta ta tuna abunda yafaru da'ita takanji tausayinta da soyayyar diyarta cikin ranta,
Shikenan yawuce Allah yayi miki albarka, amin ta amsa da dishasshiyar muryarta."
Suna zaune awajan sukaji kiran sallar isha'i hakan yayi dai-dai da shigowar halima,
Ta miqawa sawwama kudin cinikin da tayi tawuce domin yin alwala,
Daukan kudin sawwma tayi tamiqawa mahaifinta batareda tace komaiba tamiqe tana mai qara basu hakuri tashiga d'aki ta gabatarda sallar isha'i sannan tazauna tunani,
Abunda yafaru abaya yake tariyo mata tabbas tasan cewa dole hankalin mahaifanta yatashi sosai duk da cewa har yanzu bawani shekaru garetaba amma zuwa yanzu tafara gane illar da rayuwarta take ciki,
Abunda yafaru abaya ne yake tariyo mata lallai ta tabbata wannan mutumi ko wanene shi babu d'igon imani cikin zuciyarsa, idan akayi la'akari da shekarunta a wancan lokacin,
Nisawa tayi afili ta furta kalmar Allah ya'isa wanda tun lokacin data fahimci illar yayi mata take furtawa,
Akullum yafad'o mata sai tayi masa Allah ya'isa,
Kuma tanada yaqinin ako'ina yake wata rana Allah zai amsa addu'arta yayi mata sakayya akan abunda yayi mata,
Ta tabbata idan Allah yatashi kamashi sakayyarda zaiyi masa sai yafi wanda yayi mata munin gaske,
Hawaye taji yana zuba akan kumatunta ta share afili taqara furta ya Allah kamar yanda ya sanyani da mahaifana kuka,
Ya Allah ka sakamun,
Jingunuwa tayi da bango haka har bacci yadauketa azaune,
Sai da kannenta suka shigo sannan suka tasheta tagyara kwanciyarta takwanta saboda gajiya nan da nan bacci yaqara dauketa."
Asuba tagari
Lockdown🔐
To be continued
Zaynab Alabura
✔️ote
Comment
Share
Follow
💞💕
Advertisement
- In Serial41 Chapters
Millisecond: Superspeed is a curse
In a world of superheroes, Milly awakens her power as a speedster but finds herself slowly drifting away from everyone due to her new perception of time when it turns out that her super speed doesn’t come with an off-switch. Updates every two weeks. At the start of middle school, Milly is excited to finally gain some much-wanted independence by enrolling at Arkwright Academy, an all-girls boarding school far away from her childhood home. Once there, she'll have to deal with new friends, feelings, superheroes/villains, mysteries, and most of all her own power threatening to alienate her from everything else. What to expect:After a brief flashforward to get a feel for Milly's power once she awakens it, we'll start the story at the beginning of the school year.The story will involve: Poorly supervised teens, exploration of superpowers, cute lesbian/yuri romance, superheroics, and struggle. Cover Art by: Skyheartz (@Skyhe_arts on Twitter)
8 198 - In Serial44 Chapters
The Realm Beneath: A Dungeon Story
This is the story of a dungeon, not a reincarnated soul or a human trapped in a soul gem, but a dungeon. Born as a dungeon, it lives as a dungeon, and kills like a dungeon. Guided only by its experiences, vague ideas and knowledge from somewhere else and the mysterious system that greets it upon awakening it strives to build and live and learn. Immerse yourself in the tale as you read about the dungeon and the adventurers that challenge its depths, puzzles, traps and creatures. Read about the realm beneath as a world comes to life within a mountain in the centre of the land. Forests, swamps, deserts, tundra and more can all be found in the cavernous chambers that blossom with life. Author's note. There is an overarching plot that is more than just the dungeon getting bigger. I will be uploading at least one chapter a week until furthur updates on my schedule get posted and hopefully more once I finish off the other book i'm working on. You can expect me to try and craft unique challenges and floors, stuff you most likely haven't seen before in dungeon books whilst still having a hopefully decent plot. I can't promise much about it but I will certainly read all the comments, respond where appropriate and take on board suggestions. I promise to keep you updated and not drop away without saying anything. I would consider this to be part of the writers pledge but if circumstances force my hand I may have to drop it. (no plans) A Note on tags: Profanity: Not excessive but where i find appropriate. Gore: Well that depends how well I do my job doesn't it. If I can paint a vivid picture that has the potential to be gory, then my writing may be to an acceptable quality. Traumatising content: Again, this depends on my skill as a writer, I guess I hope you find it traumatising - no that’s not right. Well you know what I mean anyway. Hopefully I can paint a vivid picture in your mind that makes the book all the more special.
8 199 - In Serial6 Chapters
Necromancy Domination
"I hope I wake up in another world." Leon hoped as he stared at his blank ceiling. His eyes got heavier and heavier and everything became dark. [WELCOME NEW PLAYER!] ... This is the story about a man who never belonged in his world and wished to be where he belonged. Wishing to fulfill his dreams of acquiring FAME, MONEY, AND WOMAN! with his class being [Necromancer] that normally humans shouldn't possess. With his army of his own summoning; he will conquer (and probably fuck) every beautiful woman he sees, acquire every money he gets reward, and be famous amongst the lands!
8 87 - In Serial33 Chapters
The Legacy of a Pirate
In a universe where magic is the driving force of every planet. One would think that being able to use magic was up to luck, but in reality, it is all calculated. A new power was born from the people unable to use magic, but they would not know until later that the consequences were fatal. A fierce pirate traveled the boundless universe in search of his reason of being. He lived like a king with countless people under him in his crew. People everywhere feared the mere mention of his name, but no one would know that he also wasn't able to use magic until a particular incident. To the ones he loved, he was a saint. And to the ones he hated he was cruelest of demons. However, he would, unfortunately, breathe his last breath under the combined efforts of unknown powers. His reincarnation will inherit his power, and his countless enemies spread across the cosmos! Will he discover the truth about his unique gift?! This is my first story I ever made public, and criticism would be much appreciated as I am not so good with grammar!
8 206 - In Serial9 Chapters
Absolute Power
A story about a teenager named Aarav trying to find his place in the world, while trying to make it a better place to live. NOTE: Please remember the word 'TRYING'. Guys I have edited the prologue and uploaded it after I uploaded the fourth chapter. Although the story hasn't changed much, I have tried to make it flow smoother. Added a few more details to the life of Aarav and stuff like that. Might wanna take a look at it. P.S. - Guys this is my first story. I am trying to learn English better but since I don't have enough money for books, courses or tutors, so your criticism and support will have to do. This is my first time, so please be gentle. P.P.S. - I selected harem in tags because generally people who like it tend to be more chill. Right now I have a rough sketch till the second volume and there are only two female leads.
8 148 - In Serial30 Chapters
Mr. Professor [A Jeon Jungkook FF]
This story revolves around a normal university student who's pretty good at academics but in practical life, she's a failure. She often gets caught in an unpleasant situation with her newly appointed History Professor. The Professor is usually a kind guy but exceptionally weird towards her. He's had a gray past that made him numb to every emotion.Both of them were not bothered by each other unless their lives took a drastic turn and now, their fates Kare entangled with each other.What's going to happen? Do heavens have ulterior motives? Are their lives going to be shattered or, are they going to heal each other?WARNING- CONTAINS SMUT (18+)YOU CAN GIVE A TRY TO MY STORIES. I'LL TRY NOT TO SHOW YOU REPEATED CONTENTS!
8 216

