《ƘADDARAR RAYUWA》Page 4
Advertisement
QADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Zaynab bawa
Follow on
Page 4
Da asuba babansu da kansa yatashesu suyi sallah,
harda qananun yaran kowa sanda yatashi babansu yajasu sallah suka gabatar, addu'oi yaketa yimusu kala-kala akan Allah yakawo musu dauki cikin lamarinsu dakuma kariya cikin rayuwarsu, byan sun idarda salla sauran kuma suka koma d'aki itakuma tafito tafara share-share na gida da wanke-wanke da sauran ayyuka kafin mahaifiyarta tafito tagama komai halima tana tayata suka hade cikin gidansu tass,
Dama daii sukam ba daga nanba sunada talauci kam gashi gidannasu na talakawane kurmus amma sunada tsabtar gaske komai masu ataltale yake,
Duk rashin kyawu na gidan amma idan suka shareshi suka taltaleshi saiya baka sha'awa."
Mamansu tafito lokacin suna surfa gero wanda zasuyi kunun karyawa,
Sannu tayi musu suka gaidata sanna sukaci gabada aiki, kicin tawuce sun shareshi tass-tass sun daura ruwan zafi akan wuta,
Suna gama surfawa suka bushe suka wanke,
Barshi sukayi yadan bushe sannan suka dakeshi cikin qanqanin lokaci suka gama,
Aka dama kunu mamansu tabasu naira ashirun suka siyo sugar,
Dalam-dalam haka sugan tayiwa kunun amma ahakan sukasha domin rabonsu da samun karyawa mai kyau kamar hakama an d'an dauki lokaci,
Sai dai idan babansu yasamu ciniki mai kyau sannan ya siya musu koko da qosai na karyawa."
Da wuri mama tagama shirinta tsaff na fita anguwa da hindatu kawai tafita tabar sauran agida sanda taja kunnen sawwama akan takulada qannenta,
Sannan ta jaddada mata akan kada tabarsu da yunwa dukda tasan cewa bazata barsunba amma taqara tunasarda ita, akan ta dafa musu shinkafa,
Tana fita kuwa kamar jira sawwma takeyi tashiga dakinda babansu yake ajiye baronsa yadauko baqar leda,
Shinkafa ta gwada tiya biyu tafice, domin aiwatarda nufinta da takwana dashi cikin ranta,
Shago tatafi can ta aunar sannan ta auno mudun waken suya da duk wani abunda zata buqata tadawo gida,
Gyara waken tayi takai markad'e ta tace tadaura, wasu dan lokuta kadan tahad'e awaranta, tazauan ta soya, miyar jajjage tayi ta zuba akai ta juye a bokiti tafita,
Advertisement
Aqofar gida tazauna dake gidansu bakin titine hanyar wucewar jama'ane, kuma akwai shaguna agefen titin,
Lokaci kadan tadauka tafara ciniki, lokacinda baifi awa biyuna gefen gidansu akwai almajirai, haka sukayita siya mai goma mai biyar tana zaune anan harta siyar aqofar gida bata motsa ko'inaba,
Batayi zaton qarewarsa dawurina amma ganin yaqare yasanya,
Bata zaunaba takoma kasuwa ta auni wanda yafi nada yawa,
Abinci tafara daurawa qannenta domin gargadin mahaifiyarta tadace kada tabarsu da yunwa,
Dake tanada zafin nama wajan aiki, lokaci qalilan tadauka tagamawa qannenta abinci, sannan tafara aikin awara, har yamma taci mata bata gamaba,
Tunani tafaryi tasan har indai tayi tazuba cikin bokiti irinna datsu ba lallai tayi ciniki ba saboda yamma tayi, wata dabarace tafado mata dan haka tahad'a murhu aqofar gida tafara suya,
Abundai alhmdllh sai dai ace sam barka tafara ciniki dake wajen akwai karancin masu abun siyarwa, kuma akwai yawan shagunaan sana'a, har magrib ta risketa awajan tana suya tana cinikinta.
Dake baba shima yafita dawuri bai san mai yake faruwaba,
Yafice zuwa gidansu daga nan yabiwa mama yagaida nata mahaifan, sannan suka kamo hanya,
Ana kiran magriba mama da baba suka doso layinsu daga nesa suka hangi sawwama zaune bakin murhu da yara akanta suna jira azuba musu,
Ganinta haka mamaki ya kamasu babu wanda ya'iya magana acikinsu suka shige ciki,
Ita kama batama luradasuba kanta yayi zafi wajan saida awara,
Sanda taga anfito a sallah sannan tatura yaro yakira mata halima zata dawo yin sallah,
Halima tafito ta kar6eta, ita kuma tatashi tanugi gida da sallama tashiga gida kanta tsaye batareda wani tunaninba,
Aqofar d'aki ta samesu alamun sun idda sallah, gabantane yafadi ganinsu sun dawo dan batayi zatoba, ad'arare ta qarasa kusa dasu tana fad'in mama, baba sannunku da dawowa,
Sannu baba ya amsa, mama kuwa batama kulataba dauke kanta tayi daga kallonta, sawwama tana kallon yanayin mama jikinta yayi sanyi sosai, babane ya katseta da fadin je kiyi sallah kidawo zamuyi magana,
Miqewa tayi har tana tuntu6e ta dauki buta tashiga bayi tayi tsarki tafito tayi alwala ta gabatar da sallah,
Advertisement
Koda tadawo agefe tazauna cikin nutsuwa tace" baba gani"
Kallonta yayi cikin nutsuwa yace" mamana me nake gani?
Mamana tallan kika koma yi?
Mamana bakiga illar wannan tallar bane?"
Mamana talla tayiwa rayuwarki illa amma baki fahimci hakanba, mamana kinason qara jefa kanki cikin wani halinne?
Ko shawarata kona mahaifiyarki baki nemana lokacinda zaki fara wannan abun,
Mamana idan abunda nake kawo muku yagazane zan qara qoqari,
Nasan hakuri kawai kukeyi da duk wani abunda nake kawo muku,
Zan qara qoqari inakawo muku fiyeda na baya,
Mama wacce tunda baba yafara magana batayi maganaba sai yanzu tace"
Aiso take ta nuna cewa iyayenta sun gaza sun kasa daukar d'awainiyarta bari tafita itada kanta ta nema,
Mama taqarasa maganar cikin zafin raii,
Girgiza kai sawwama tahauyi hawaye na zuba a idanuwanta,
Cikin muryar kuka ta zakud'a kusada mahaifanta tafara fad'in,
Baba dan Allah kuyi hakuri wallhy ba nufinaba kenan,
Baba kokadan ban raina abunda kake kawo manaba,
Baba a kullum tausayinkane cikin raina jiya ban iya runtsawaba saboda tunanin halinda jiya kadawo aciki,
Baba banyi haka dan 6acin rankaba nayi hakane dan taimakonka,
Juyawa tayi wajan mama tace mama dan Allah ku yafemin,
tana fadin haka taqara sanya kuka bata ta6a tunanin cewa mahaifanta zasu dauki zancen hakaba da bata faraba, dan babu abunda taqi jini irin 6acin ransu,
Kukanda takene yasanya duka jikinsu yayi sanyi koda bata fadiba sun san halinta sun san halin d'iyarsu sunsan sawwama bazata ta6a yin haka danta nuna cewa mahaifanta sun qaza ba, tayi hakanne kawai danta taimaka musu, amma dole su nuna 6acin ransu saboda ta fahimci halinda takeson jefa kanta aciki,
Da halinda tafad'a abaya, sannan su sanya mata tsoron wanda zai faru nan gaba,
Jikinsu yayi sanyi sosai suka gaza magana
Ido kawai suka tsira mata tana kukanta babanta yarasa mai zai furta shidai yana tsoron yaqara barinta talla akaro na biyu,
Dakyar ya'iya daurewa yafara fadin naji na fahimceki mamana, ina gudun qara faruwar abunda yafaru abayane, saboda kowani mahaifi zaiso kare d'iyarsa kada wani abun yasameta, ni nagaza akaro na farko banso nakara bari wani abun yasameki, tunda kinga ni nakasa kareki kiyi haquri ki taimakeni wannan karon na kare rayuwarki,
Zuciyata bazata iya juran wani abun yaqara samunkiba."
Girgiza kai kawai sawwama takeyi,
saida tadan tsagaita kukan sannan tafara fadin mama baba kuyi hakuri dan Allah ku yafeni bazan sakeba,
Tausayintane yaqara kamasu,
Har cikin zuciyar mama take tausayin diyarta kuma tana sonta sosai akullum takalli d'iyarta ta tuna abunda yafaru da'ita takanji tausayinta da soyayyar diyarta cikin ranta,
Shikenan yawuce Allah yayi miki albarka, amin ta amsa da dishasshiyar muryarta."
Suna zaune awajan sukaji kiran sallar isha'i hakan yayi dai-dai da shigowar halima,
Ta miqawa sawwama kudin cinikin da tayi tawuce domin yin alwala,
Daukan kudin sawwma tayi tamiqawa mahaifinta batareda tace komaiba tamiqe tana mai qara basu hakuri tashiga d'aki ta gabatarda sallar isha'i sannan tazauna tunani,
Abunda yafaru abaya yake tariyo mata tabbas tasan cewa dole hankalin mahaifanta yatashi sosai duk da cewa har yanzu bawani shekaru garetaba amma zuwa yanzu tafara gane illar da rayuwarta take ciki,
Abunda yafaru abaya ne yake tariyo mata lallai ta tabbata wannan mutumi ko wanene shi babu d'igon imani cikin zuciyarsa, idan akayi la'akari da shekarunta a wancan lokacin,
Nisawa tayi afili ta furta kalmar Allah ya'isa wanda tun lokacin data fahimci illar yayi mata take furtawa,
Akullum yafad'o mata sai tayi masa Allah ya'isa,
Kuma tanada yaqinin ako'ina yake wata rana Allah zai amsa addu'arta yayi mata sakayya akan abunda yayi mata,
Ta tabbata idan Allah yatashi kamashi sakayyarda zaiyi masa sai yafi wanda yayi mata munin gaske,
Hawaye taji yana zuba akan kumatunta ta share afili taqara furta ya Allah kamar yanda ya sanyani da mahaifana kuka,
Ya Allah ka sakamun,
Jingunuwa tayi da bango haka har bacci yadauketa azaune,
Sai da kannenta suka shigo sannan suka tasheta tagyara kwanciyarta takwanta saboda gajiya nan da nan bacci yaqara dauketa."
Asuba tagari
Lockdown🔐
To be continued
Zaynab Alabura
✔️ote
Comment
Share
Follow
💞💕
Advertisement
- In Serial37 Chapters
Smoldering Embers
Unjustly, he was put in prison. He carefully managed the spark within, waiting for a chance when it suddenly appeared. Towers sprang up all around the world, without any disturbance, as though they had always been there. A change was coming but for him, it was a chance to get his revenge. Release schedule: For now I will be trying 3 chapters/ week. Chapter Size: Around 2k words. The cover is not mine. Shout out to the artist who made the amazing thing: https://unsplash.com/photos/xXj3ctfRmvw
8 59 - In Serial7 Chapters
Necromacy - Dark World
(Ne-Cro-Mah-See)Isekai meets Dark Fantasy in this tale of a world saturated in decay and darkness. Upon experiencing a strange dream, a young man finds himself in a world of perpetual darkness. For six days and nights the sun will not rise and creatures of the dark move in the abscence of light.Pulled into an unfamilar, hellish place he must now navigate this dark world while trying to make sense of his new environment and all the inhabitants (dead, deadly or otherwise) that he encounters.
8 184 - In Serial34 Chapters
Descendants of a Dead Earth
In the future, Man has traveled the Cosmos. In the future, Man has discovered many other races. In the future...Man has no home. 200 years after the great war that destroyed Earth, humanity struggles to survive; fractured, divided, wanted by no one. Until Maggie, of the Tinker Clan, makes a discovery, setting in motion a chain of events that could change everything.
8 179 - In Serial37 Chapters
The Last God (Excerpt)
This is an excerpt of the upcoming novel The Last God. Everyone cheered the day the world ended. Everyone cheered the day he saved the world. Cael Cavanaugh did not. Cael Cavanaugh survived the brutal invasion of his home and is now living with his family and adopted siblings on the ashen lands of the west. He rescues people from a fate that eclipses death and is the bridge between a rebel group that will stop at nothing to achieve its goals, and a tyrannical government that treats those who have not been reborn as dregs. But when Cael inadvertently sets off the end of the world, he will have to choose between a government that could avert world annihilation but that holds sinister motives, or the equally vicious rebel group that would sacrifice everyone for what they call liberty, even those Cael holds dearest. How far would you go to save the world?
8 65 - In Serial30 Chapters
Expensive Mistakes
(Based off the webcomic Ghost Eyes by Mr. Circus Papa) "Will you be staying at the church for Christmas?""I promised I would return for holidays, so yes.""Great! See you then!" Tobias Schneien moved out of the church as soon as he turned eighteen. He hated even thinking about the place he grew up in. Nevertheless, he promised he'd return on holidays.Emilio Murkmere began working as a nurse at the hospital a year and a half ago. Things had been pretty uneventful. Until one Christmas. An AU based off of writing prompts my friend and I found on Pinterest.(Cover art by IzzoSStv on Devianart. https://www.deviantart.com/izzosstv/art/Tobias-x-Emilio-806882628)
8 216 - In Serial7 Chapters
DESIRE.
THAT ONE SONG FROM DEFTONES. ( tbhk oneshots, discontinued srry )
8 207

