《ƘADDARAR RAYUWA》Page 4
Advertisement
QADDARAR RAYUWA*
*بسم الله الرحمن الرحيم*
Haske writers association💡
Zaynab bawa
Follow on
Page 4
Da asuba babansu da kansa yatashesu suyi sallah,
harda qananun yaran kowa sanda yatashi babansu yajasu sallah suka gabatar, addu'oi yaketa yimusu kala-kala akan Allah yakawo musu dauki cikin lamarinsu dakuma kariya cikin rayuwarsu, byan sun idarda salla sauran kuma suka koma d'aki itakuma tafito tafara share-share na gida da wanke-wanke da sauran ayyuka kafin mahaifiyarta tafito tagama komai halima tana tayata suka hade cikin gidansu tass,
Dama daii sukam ba daga nanba sunada talauci kam gashi gidannasu na talakawane kurmus amma sunada tsabtar gaske komai masu ataltale yake,
Duk rashin kyawu na gidan amma idan suka shareshi suka taltaleshi saiya baka sha'awa."
Mamansu tafito lokacin suna surfa gero wanda zasuyi kunun karyawa,
Sannu tayi musu suka gaidata sanna sukaci gabada aiki, kicin tawuce sun shareshi tass-tass sun daura ruwan zafi akan wuta,
Suna gama surfawa suka bushe suka wanke,
Barshi sukayi yadan bushe sannan suka dakeshi cikin qanqanin lokaci suka gama,
Aka dama kunu mamansu tabasu naira ashirun suka siyo sugar,
Dalam-dalam haka sugan tayiwa kunun amma ahakan sukasha domin rabonsu da samun karyawa mai kyau kamar hakama an d'an dauki lokaci,
Sai dai idan babansu yasamu ciniki mai kyau sannan ya siya musu koko da qosai na karyawa."
Da wuri mama tagama shirinta tsaff na fita anguwa da hindatu kawai tafita tabar sauran agida sanda taja kunnen sawwama akan takulada qannenta,
Sannan ta jaddada mata akan kada tabarsu da yunwa dukda tasan cewa bazata barsunba amma taqara tunasarda ita, akan ta dafa musu shinkafa,
Tana fita kuwa kamar jira sawwma takeyi tashiga dakinda babansu yake ajiye baronsa yadauko baqar leda,
Shinkafa ta gwada tiya biyu tafice, domin aiwatarda nufinta da takwana dashi cikin ranta,
Shago tatafi can ta aunar sannan ta auno mudun waken suya da duk wani abunda zata buqata tadawo gida,
Gyara waken tayi takai markad'e ta tace tadaura, wasu dan lokuta kadan tahad'e awaranta, tazauan ta soya, miyar jajjage tayi ta zuba akai ta juye a bokiti tafita,
Advertisement
Aqofar gida tazauna dake gidansu bakin titine hanyar wucewar jama'ane, kuma akwai shaguna agefen titin,
Lokaci kadan tadauka tafara ciniki, lokacinda baifi awa biyuna gefen gidansu akwai almajirai, haka sukayita siya mai goma mai biyar tana zaune anan harta siyar aqofar gida bata motsa ko'inaba,
Batayi zaton qarewarsa dawurina amma ganin yaqare yasanya,
Bata zaunaba takoma kasuwa ta auni wanda yafi nada yawa,
Abinci tafara daurawa qannenta domin gargadin mahaifiyarta tadace kada tabarsu da yunwa,
Dake tanada zafin nama wajan aiki, lokaci qalilan tadauka tagamawa qannenta abinci, sannan tafara aikin awara, har yamma taci mata bata gamaba,
Tunani tafaryi tasan har indai tayi tazuba cikin bokiti irinna datsu ba lallai tayi ciniki ba saboda yamma tayi, wata dabarace tafado mata dan haka tahad'a murhu aqofar gida tafara suya,
Abundai alhmdllh sai dai ace sam barka tafara ciniki dake wajen akwai karancin masu abun siyarwa, kuma akwai yawan shagunaan sana'a, har magrib ta risketa awajan tana suya tana cinikinta.
Dake baba shima yafita dawuri bai san mai yake faruwaba,
Yafice zuwa gidansu daga nan yabiwa mama yagaida nata mahaifan, sannan suka kamo hanya,
Ana kiran magriba mama da baba suka doso layinsu daga nesa suka hangi sawwama zaune bakin murhu da yara akanta suna jira azuba musu,
Ganinta haka mamaki ya kamasu babu wanda ya'iya magana acikinsu suka shige ciki,
Ita kama batama luradasuba kanta yayi zafi wajan saida awara,
Sanda taga anfito a sallah sannan tatura yaro yakira mata halima zata dawo yin sallah,
Halima tafito ta kar6eta, ita kuma tatashi tanugi gida da sallama tashiga gida kanta tsaye batareda wani tunaninba,
Aqofar d'aki ta samesu alamun sun idda sallah, gabantane yafadi ganinsu sun dawo dan batayi zatoba, ad'arare ta qarasa kusa dasu tana fad'in mama, baba sannunku da dawowa,
Sannu baba ya amsa, mama kuwa batama kulataba dauke kanta tayi daga kallonta, sawwama tana kallon yanayin mama jikinta yayi sanyi sosai, babane ya katseta da fadin je kiyi sallah kidawo zamuyi magana,
Miqewa tayi har tana tuntu6e ta dauki buta tashiga bayi tayi tsarki tafito tayi alwala ta gabatar da sallah,
Advertisement
Koda tadawo agefe tazauna cikin nutsuwa tace" baba gani"
Kallonta yayi cikin nutsuwa yace" mamana me nake gani?
Mamana tallan kika koma yi?
Mamana bakiga illar wannan tallar bane?"
Mamana talla tayiwa rayuwarki illa amma baki fahimci hakanba, mamana kinason qara jefa kanki cikin wani halinne?
Ko shawarata kona mahaifiyarki baki nemana lokacinda zaki fara wannan abun,
Mamana idan abunda nake kawo muku yagazane zan qara qoqari,
Nasan hakuri kawai kukeyi da duk wani abunda nake kawo muku,
Zan qara qoqari inakawo muku fiyeda na baya,
Mama wacce tunda baba yafara magana batayi maganaba sai yanzu tace"
Aiso take ta nuna cewa iyayenta sun gaza sun kasa daukar d'awainiyarta bari tafita itada kanta ta nema,
Mama taqarasa maganar cikin zafin raii,
Girgiza kai sawwama tahauyi hawaye na zuba a idanuwanta,
Cikin muryar kuka ta zakud'a kusada mahaifanta tafara fad'in,
Baba dan Allah kuyi hakuri wallhy ba nufinaba kenan,
Baba kokadan ban raina abunda kake kawo manaba,
Baba a kullum tausayinkane cikin raina jiya ban iya runtsawaba saboda tunanin halinda jiya kadawo aciki,
Baba banyi haka dan 6acin rankaba nayi hakane dan taimakonka,
Juyawa tayi wajan mama tace mama dan Allah ku yafemin,
tana fadin haka taqara sanya kuka bata ta6a tunanin cewa mahaifanta zasu dauki zancen hakaba da bata faraba, dan babu abunda taqi jini irin 6acin ransu,
Kukanda takene yasanya duka jikinsu yayi sanyi koda bata fadiba sun san halinta sun san halin d'iyarsu sunsan sawwama bazata ta6a yin haka danta nuna cewa mahaifanta sun qaza ba, tayi hakanne kawai danta taimaka musu, amma dole su nuna 6acin ransu saboda ta fahimci halinda takeson jefa kanta aciki,
Da halinda tafad'a abaya, sannan su sanya mata tsoron wanda zai faru nan gaba,
Jikinsu yayi sanyi sosai suka gaza magana
Ido kawai suka tsira mata tana kukanta babanta yarasa mai zai furta shidai yana tsoron yaqara barinta talla akaro na biyu,
Dakyar ya'iya daurewa yafara fadin naji na fahimceki mamana, ina gudun qara faruwar abunda yafaru abayane, saboda kowani mahaifi zaiso kare d'iyarsa kada wani abun yasameta, ni nagaza akaro na farko banso nakara bari wani abun yasameki, tunda kinga ni nakasa kareki kiyi haquri ki taimakeni wannan karon na kare rayuwarki,
Zuciyata bazata iya juran wani abun yaqara samunkiba."
Girgiza kai kawai sawwama takeyi,
saida tadan tsagaita kukan sannan tafara fadin mama baba kuyi hakuri dan Allah ku yafeni bazan sakeba,
Tausayintane yaqara kamasu,
Har cikin zuciyar mama take tausayin diyarta kuma tana sonta sosai akullum takalli d'iyarta ta tuna abunda yafaru da'ita takanji tausayinta da soyayyar diyarta cikin ranta,
Shikenan yawuce Allah yayi miki albarka, amin ta amsa da dishasshiyar muryarta."
Suna zaune awajan sukaji kiran sallar isha'i hakan yayi dai-dai da shigowar halima,
Ta miqawa sawwama kudin cinikin da tayi tawuce domin yin alwala,
Daukan kudin sawwma tayi tamiqawa mahaifinta batareda tace komaiba tamiqe tana mai qara basu hakuri tashiga d'aki ta gabatarda sallar isha'i sannan tazauna tunani,
Abunda yafaru abaya yake tariyo mata tabbas tasan cewa dole hankalin mahaifanta yatashi sosai duk da cewa har yanzu bawani shekaru garetaba amma zuwa yanzu tafara gane illar da rayuwarta take ciki,
Abunda yafaru abaya ne yake tariyo mata lallai ta tabbata wannan mutumi ko wanene shi babu d'igon imani cikin zuciyarsa, idan akayi la'akari da shekarunta a wancan lokacin,
Nisawa tayi afili ta furta kalmar Allah ya'isa wanda tun lokacin data fahimci illar yayi mata take furtawa,
Akullum yafad'o mata sai tayi masa Allah ya'isa,
Kuma tanada yaqinin ako'ina yake wata rana Allah zai amsa addu'arta yayi mata sakayya akan abunda yayi mata,
Ta tabbata idan Allah yatashi kamashi sakayyarda zaiyi masa sai yafi wanda yayi mata munin gaske,
Hawaye taji yana zuba akan kumatunta ta share afili taqara furta ya Allah kamar yanda ya sanyani da mahaifana kuka,
Ya Allah ka sakamun,
Jingunuwa tayi da bango haka har bacci yadauketa azaune,
Sai da kannenta suka shigo sannan suka tasheta tagyara kwanciyarta takwanta saboda gajiya nan da nan bacci yaqara dauketa."
Asuba tagari
Lockdown🔐
To be continued
Zaynab Alabura
✔️ote
Comment
Share
Follow
💞💕
Advertisement
- In Serial654 Chapters
The Summoned Monster That Is Summoning Another Monster
Have you ever thought a monster that has a job of a summoner and a tamer
8 1229 - In Serial113 Chapters
Memorabilia of the Iron Princess
One world, split by time and war. One girl, torn between her past and present. Miles below Earth’s surface an android soldier wakes, eager to take the place of her fallen predecessor and fulfill her role in helping mankind retake the planet. Except the rules have changed, and she hasn't got the memo. When she discovers the central database has been mysteriously crippled, God Gier 11 finds herself emerging into a world changed beyond her recognition and clueless as to how it has come to be. But before she can work out why coffee no longer exists in this strange new place, 11 stumbles heart-first into a gorgeous elf with a smile that makes her head spin, a crazed vampire claiming to be a relative, and an ancient conspiracy that threatens to unravel the fate of humanity and everything 11 thinks she knows about herself. Caught between duty and desire, waging war and pioneering the first cappuccino, 11 must make full use of her newfound autonomy to uncover the secrets of her past and save the people she has come to care about. But without the excuse of being an emotionless machine, will she be able to cope with the truth of what she really is, and the things she has done?
8 181 - In Serial18 Chapters
A Mighty Conqueror
"I found out, the greatest ones. The best. The most prolific ones, were all momma's boys. Yea, afraid of their mother. Napoleon, Alexander, Genghis Khan." Mike Tyson on the Greatest Conquerors. Well, this is a cultivation story about a momma's boy. Will he conquer the known world? Maybe, just maybe. Atuel had heard many stories. All had said that the worst days were accompanied by rain, thunder, and dark clouds lead by powerful winds. Yet, he had found it to be the exact opposite in reality. On the brightest, most peaceful day, did his father disown him and throw his mother out of their home. It was on a sunny afternoon that he went from the honored son of the City Lord, to the untouchable son of the witch. Said witch was his mother, the kindest soul he had ever seen. Instead, it was the Saintess that had schemed for his mother's demise that was filled with a black heart, enchanting the people with a nice smile and kind words. All to take his mother's position as Head Wife. Now, he and his mother must struggle to live and rise from the ashes of their societal death. New and powerful must they be, or death will only meet them with extreme prejudice. I suck at synopsises... No harem. No spitting blood. And certainly no jade beauties... maybe a few jade beauties... Okay okay! There will be jade beauties! But no spitting blood! I will not negotiate!
8 178 - In Serial9 Chapters
Back Cat Time
"Natasha is a young woman who works as a handmaid for a noble named 'Samus'. However, illness eventually wins against him and Natasha is sent to her former Master's son, a young man named "Milo". A new life awaits her there, but Natasha must hold her head high. However, her life changes drastically when she learns about the dream of her new Master, Milo... A future she could never have foreseen, but a future you could not have foreseen either."
8 158 - In Serial12 Chapters
Resident Evil 2 x Male Reader (Trapped In A Game)
You were a huge fan of the Resident Evil series and played every game it has. One day when you started playing Resident Evil 2 Remake, your console and power went out then soon found yourself in Raccoon City. You knew that you had to get through the game to escape and get back to your world. However, things that you encountered were not as you were expecting.
8 154 - In Serial14 Chapters
LIKE AN IDOL•MYUNGJIN
Myungie: HA HA HAYou funny boiThat was really funny broI laughed Idk who is this idol but I like himGive me his name and I ll stan him later But now please send a real photo of youJinu: to be honest,Its me :") ***•B×B•texting+written parts***-COMPLETED-
8 161