《ƘADDARAR RAYUWA》ƘPage 1
Advertisement
*ƘADDARAR RAYUWA*
Zaynab bawa
Haske writers association💡
Alhamdulillahi Allah nagode maka daka bani damar fara rubuta wannan littafi kura kurenda zan rubuta aciki Allah yayafemin wanda nayi dai-dai kuma Allah yabani ladansa, Godiya ta tabbata ga ubangiji mai kowa mai komai daya bani damar dawowa mukuda wannan labari bayan hutun shekara d'aya."
Makaranta littafina inaso kusani shi d'an adam akullum tara yake bai cikawa goma, idan nayi kuskure cikin rubutuna ina maraba da gyara amma banda cin fuska,
Yawwa sannan kuma abuna gaba book dinnan yanada yawa kada nafara rubutu qananun magana su taso akan cewa inajan book kamar yanda yafaru abook dina na baya, Allah yasa mudace Amin."
Page 1
Iska sosai ake kad'awa yayinda ko'ina yadauki sanyi, qura ta lullu6e ko'ina yayinda aka samu karancin wucewar jama'a saboda qarfinda iskar take dashi, yanayinda ake ciki agarin yanayine mai cikeda ban sha'awa da d'aukar hankali
Domin iska busawa takeyi tako'ina ka dukkan alamu hadarine mai qarfin gaske yakeson had'uwa,
Ganyayyaki na bishiyoyi sai kadawa sukeyi suna bada iska mai dad'in gaske.*
Cikin qanqanin lokaci hadari yahad'u sosai garin yayi baqin qirin, daga nan gari yad'aure hadari yafara bugawa alamun kowani irin lokaci ruwa yana iya sauka."
Yanda hadari ya hadu alamu yanuna ruwa zai zuba sosai, duk wani mahaluki kamata yayi ace yanemi hanyar gida, saboda Allah kadai yasan lokacin tsayawar wannna ruwan idanya barke,
Wanda yake waje kuwa to tabbas hankalinsa bazai kwanta saboda gabaki daya hankalinsa zaiyi gidane.
D'an muskud'awa yayi akan y'ar yololuwar katifarsa, wanda yakejin bugawar hadari dakuma tsawa kamar wanda zai rusa gidan yafad'o akansa, saboda rashin qarfin ginin da dukkan alamu ginin yadade sosai gashi na qasane hattada rufun kwanon yatsufa yayi tsatsa,
Daga yanda yake kwance yana hango yanda hasken walqiya yake ratsowa ta bulellen bugun kwanan, ya tabbata yau idan akayi ruwannan d'akin sai yayi yoyo'
Nisawa yayi sannan yaSanya hannu ya lalu6o wayarsa itel mai torch wacce taji jiki sosai idan ka ganta a'ido bazakayi tunanin tana amfaniba,
Kunna torchin yayi sannan yajuya gefe ya dubi wacce take gefensa tana kwance, d'an bubbugata yayi yana fad'in daga kwanciya har kinyi bacci'
Cikkn muryar da take nunida tafara bacci amma baccin baiyi nisaba tace" tukunna dai,
Ajiye wayar yayi agefe yana fad'in kinga hadarine yahad'u sosai agarinnan yarinyarnan kuwa tadawo?
Nishi tad'anyi sannan tamiqe tazauna tana mutsutsuka idanuwa sanda tad'an watssake sannan tace" yanzun qarfe nawane?
Tara da kwtaa yabata amsa ayayinda yake kallon lokacin ajikin wayarsa,
Cikin halin rashin damuwa tace aii tanafin hakama domin tana kaiwa har da rabi ko wuce hakama,
Eh nasani amma yanzun hadarine agarin sosai, kuma wannan ruwa idanya barke Allah kadai yasan lokacin tsayawarsa, hankalinku bai kamata ya kwantaba sanin cewa diyarmu tana waje koda nine nake waje wannan lokaci na tabbata hankalina gida zaiyi, jira tayi sanda yagama maganar sannan ta muskutawa tace yanzu hakama tadawo tana d'akinta ai taga hadari bazata bari takai hakaba, idan tadawo nasan dakinsu zata shige dan idan nayi bacci kasan bata tashina, gyada kaii kawai yayi yakoma ya kwanta amma badan hankalinsa ya kwantaba."
Sauri-sauri takeyi tagama had'a kayanta takama hanyar gida saboda yanda hadari ke bugawa,
Ido tatsura ma wasu samari wanda ga dukkan alamu su take jira su gama su bata kwanonta takama hanyar gida,
Advertisement
Had'e jikinta tayi tatakure awaje d'aya saboda iska da akeyi ga wani irin sanyi da yake shigarta, sun d'an dauki lokaci kafinnan suka gama suka miqa mata, sauri-sauri ta kar6a tahad'e cikin kayanta takama hanyar gida, wani irin tsorone yashigeta tafiya takeyi cikin sauri saboda bbu kowa ahanya kafa tad'auke, ga kuma wani irin duhu da hanya tayi, wani lokacin sai hadarin yad'an harba kafinnan take hangen hanya,
Batayi auneba tajita ta buge mutum dasauri taja baya cikin tsoro saboda kokad'an bata lurada waniba itadai kawai taji ta bugi mutunme,
Wani irin nishi taji mutumin yanyi kamar wanda ake shirin zare ransa ga dukkan alamu baida cikkekken lafiya,
Gudu tayi niyyar arcewa dashi saboda atunaninta aljanine,
Amma ina kafin tayi wani yunkuri wannan mutumi yakamata wanda baya iya kallon fuskarsa saboda baqin da garin yayi,
Ihu ta kwala tana neman taimako amma babu wanda yajiyota saboda yanayinda garin yake ciki,
Sun batu tafarayi tana fad'in" dan Allah kuyi hakuri bansan ku bane awajan yasanyani nabi hanyar harna bugeku bansaniba, tana fad'in haka ita atunaninta cewa aljanine,
Ita bata saniba wannan mutumi wani nufi daban yake dashi akanta,
Cikin qanqanin lokaci yafara qoqarin aiwatarda mummunan nufinsa akanta, hakan yayi dai-dai da sauqowar ruwan sama, duk ihunta takeyi babu wanda yajiyota sakamakon ruwan sama dayake sauka da qarfi, har saida yagama aiwatarda nufinsa akanta."
Jin sauqowar ruwan sama gabaki d'aya sai hankalinsa yatashi, miqewa yayi yafita qauren d'akin yara yabude amma wayama bata ciki, qannenta ne kawai aciki,
Juyawa yayi dad'an sauria yana kwala kira, ummi! Ummi!
Ad'an tsorace tamiqe tana lalu6en torchinta wanda take gefenta, daukowa tayi ta kunna tafara bubbugawa saboda bettery din cikinta yayi sanyi domin harya fara ruwa, dakyar torchin takawo tatashi tafito, ganinsa ahaka cikin ruwa yana dukansa yasanya ta tsorata taba fad'in me yafaru??
Yarinyarnanfa bata dawowa,
Bata dawoba? ta maimaita zancensa qarfe goma har kusan da rabi ake nema, ad'an tsorace tace lallai ba lafiyaba duk dai bata wuce tara da rabi idanma ta gota kadanne,
Kinga dawo nan kizauna da yaran barina fita na dubata ya umarceta,
to tace sannan tabude qauren d'akin tashiga shikuma yafice domin nemanta, haka yabi hanya yana dubawa,
Wajanda take zamada tallanta tafara zuwa yasamu babu kowa awajan,
D'aya hanyar yabi wacce bata ita yazoba,
Ahankali yake tafiya yanayi yana duba tako'ina,
Gabansane yayi mummunan faduwa saboda hango mutum dayayi akwance can nesa dashi dasauri yaqarasa wajan aikuwa ya kalli d'iyarsaa kwance cikin wani irin yanayi,
Lakar jikinsane yadauke gabaki daya yakasa aikata komai a mutum mutumi yake jinsa,
Yafi 5minute ahaka zuciyarsa tanayi masa zogi da quna,
Tsugunannawa yayi ya cicci6eta yanufi gida bai tsaya bin takan kudin tallar ba balle kayan tallan, babu sallama yashiga gida' saboda qofar da buhu aka Rufe yasanya bataji mostsin shigowarsaba, ajiyeta yayi akan barandarsu wanda akayita da duddu6in laka,
Haka yazauna yazuba uban tagumi ya lula wata duniyar,
Jin shiru ga lokaci yaja yasanyata fitowa domin leqawa,
Arazane taqarasa wajansa tana kallon yarinyarta datake kwance, tana kallonta hankalinta yabata abunda yafaru, hannu tasanya akayi takwala qara tana fadin mun shiga uku mun lalace,
Sai alokacin hankalinsa yadawo kanta bai iya kulataba har tagama koke kokenta kusan awa daya sannan numfashin yarinyar yafara sauka da qarfi-qarfi,
Awannan dare mahaifan wannan yarinya sunga tashin hankali duk da kasancewar bacci 6arawone amma bai samu damar d'aukansuba,
Advertisement
Cikin dare mamanta tayi qoqari tadaure zuciyarta ta gyara d'iyarta."
Washe gari haka dukansu suka tashi da baqin ciki gashi babu wanda zasuyi blaming dan faruwar wannan abun domin kuwa kowa yanada nasa laifin akan tallan datakeyi,
Koda qannenta suka tashi dasafe suga ga yayarsu ahaka sun shiga tashin hankali,
Qaramar cikinsuce wacce bazata wuce 3yrs ba tadubi mamansu tana fad'in mama menene yasamu adda??
Koda mahaifiyarsu taji tambayar da d'iyarta tayi mata sai tadubi yarinyar kokadan batasan yanda zata yiwa yaran bayaniba,
Hasalima ita tafiso ta6oye abun cikin ranta saboda daga ita sai babansu da ita kanta yarinyar domin bataso koda makwafta su fahimci abunda yake faruwa,
Kamo yarinyar tayi zuwa jikinta sanna tace addanki batada lafiyane!
Meya sameta?
taji babbar cikinsu wacce aqalla zata iya kaiwa 11yrs tatambaya
Zazza6i tabasu amsa atakaice,
Sannan tadaura da fadin kuyi mata addu'a,
Hada baki sukayi wajan fadin Allah yasauwake, amin ta amsa sannan ta miqe,
d'akinta tanufa azaune tasamu baban yaran zama tayi gefensa cikin daurewar zuciya tace baban Hafsa yakamata katashi kafita haka nan, wannan zaman bazai kaimu ko'inab kaga dara tayi,
D'agowa yayi yadubeta cikin karyewar zuciya sannan yace" bazan iya fitaba ummi duk yanda kike tunanin wannan abun yawuce nan azuciyata,
Mun tarwatsa rayuwar d'iayarmu,
Duk wannan laifin nawane daban kasance mai biyawa iyalaina buqatava wanda har hakan takaiga daurawa d'iyata talla,
Cikin lallashi tace" baban hafsa kadaina daurawa kanka laifi kana iya qoqarinka wajan ganin ka biya mana buqatunmu,
Kumafa kasani idan Allah yarigada yarubuta faruwar abu bbu makawafa saiya faru, koda kuwa bata wannan hanyar ba, shidai abu kawai yakan kasance yanada sanadine amma faruwarsa rubutaccen al'amarine, jarabawace ta ubangiji addu'a kawai zamuyi mata Allah yabata lpy Allah kuma yabamu damar cinye jarabawarmu, Wannan QADDARAR RAYUWARTA kenan bamu isa canja mataba,
Yanxu katashi kafita kasamo mana abunda zamu d'aura domin kwayar hatsi babu acikin gidannan, sannan kuma ajikinta yayi zafi sosai dole zamu saya mata koda pracetamol ne,
Idan baka fitaba mutannen anguwa zasuyi zaton wani abun nikuma bana buqatar kowa yasan wannan lamari murufa kanmu asiri mu sirrinta wannan lamari, idan wasu sunyiwa abun fahimta maikyau wasu bazasuyiba kowa da irin nasa tunanin kowa kuma akwai fuskarda yake kallon lamari,
Sanyayyun magana tayita masa har Allah yasa hankalinsa yad'an kwanta yatashi yamiqe,
Wani d'aki yashiga yafito wheelbarrow da buhu, bude buhun yayi ya juye yalo acikin baho, wasu daga cikin yalo dinma harsun fara yanqonewa,
Wannan yarinya da bazata wuce 11yrs ba, matsowa tayi tafara wanke masa yalon tana zubawa akan wheell barrow din shikuma yamiqe yafara jerasu,
Yanayi yana fad'in Allah yayi miki albarka sadiya, amin ta amsa taci gabada wanke masa harta gama,
Sannan ya shirya kayansa yafita ita kuma sadiya takoma wajan y'ar uwarta saboda zazza6inta duk yabi yadameta,
Hannu ta sanya tata6a jikin y'ar uwar tata jikin yadauki zafi sosai,
Sannu tafad'a tana mai qara tausaya mata,
Sai can mahaifiyarsu tashigo tadubi sadiya tana fadin halima ungo nan tamiqa mata kofi, jeki gidan yawale ki kar6omin koko na ishirin kice idan babanku yadawo zan aiko mata, hindatu harta fara yimun kukan yunwa gashi yarku itama bataci komaiba idan tasha ko zazza6in zai fita,
Kar6an kofin tayi tafice mamansu tazauna gefen hafsa wacce take rawar sanyi dukda kasancewar yanxu ba sanyin akeyiba,
Amma dake ita zazza6ine yake damunta yasanya takejin sanyi sosai,
Hawaye taji yana zurara akan kumatunta yayinda take qarewa yarinyar kallo,
Abubuwa dasuka faruwane suketa tariyo mata aranta, duk cikin zantuttukanda suka dawo mata babu wacce ta tsaya mata arai kamar maganar surukarta wato mahaifiyar mijinta kakar yaran kenan,
Akullum koda zuwa gidan tayi nadan wani lokaci idanta kalli yaran sai tafara fad'in shikam hamisu yana shan wahala ko d'aya baida mataimaki yara mata Akullum damuwa suke zamowa bbu wata hanyarda zasu taimaki mahaifinsu, shiyasa har yanzu yakasa tara abun kansa,
Yara mata! Yara mata! Takan fadi hakan yakai sau uku sannan sai tace yara mata aii rayuwarsu hatsarine garadai namiji zai shiga ko'ina,
Nisawa tayi ta matse kwallarta akullum mahaifiyar mijinta tafadi wannan magana takan tsaya mata arai,
Ayau kam ta tabbatarda maganarta datake fadin yara mata rayuwarsu hartsarine akullum suna buqatar akillacesu,
Wata irin tsoro da faragabanebya d'areu cikin ranta ahankali ta furta wato idan kanada d'iya mace hankalinka bazai kwantaba har sai ranta akace yai gashi sunyi aure,
Nisawa tayi data tuna nata gida biyar da suke nan mata riras, d'aga hannu sama tayi had'eda fadin Allah kakaremin yarannan da kariyarka,
Sadiya tadan dauki lokaci bata dawoba tsakanin fitarta da yanzu Allah kadai yasan halinda mahaifiyarsu tashiga tunani kala-kala aranta jitakeyi kamar tatashi tabi bayanta' tana saka da warwara cikin ranta saiga sallamar yarinyar nan tashigo, sauqe ajiyar zuciya tayi domin tasamu sanyi aranta,
Miqawa mahaifiyarsu kunun tayi tana fadin mama wai akwai naira goma ranarda yaya hafsa ta kar6owa hindatu ba'a kaiba,
In sha Allahu za'akai mama tafadi sannan tace tashi ki daukomin kofi,
Miqewa tayi tadauko nata kofi ta zuzzzuba musu dukda bawani yawane dashiba amma hakan dai yaraba musu amma ita ko tunanin kantanma bataiba, dakyar tasamu hafsa tadan sha mata tanasha tana rarrashinta da fadin yawwa sawwmana in sha Allah sai Allah ya saka miki sha abunki,
Dahaka harta samu tadan sha,
Sai yamma sosai babansu yadawo,
Alhmdllh yadanyi ciniki bbu laify kamar ansan halinda yake ciki,
Tundaga hanya ya auno musu shinkafa yasiyo barkono da maggi da mangyda,
Sai alokacin kafin tasamu tadaura musu abinci yaran yunwa harta galabaitar dasu,
Saboda sun saba ko yaya idan mamarsu tayi abun sayarwa kafin yayarsu tafita dashi, sai sunci sannan idan babansu yadawo abunda yasamu sai adaura,
Magani suka bata tasha zuwa jimawa zazza6in yadan saketa."
Cikin d'an kwanaki Alhmdllh tawarware amma sai dai halinda suke ciki awannan gida abun baya misaltuwa domin kuwa tallanda takeyi yake dan taimaka musu, jarin babansun kadanne gashi sun
Cinyeshi acikinsu,
Ita kam hafsa sauda yawa takan zauna tayi tagumi tana tunani,
Idan mahaifiyarta tadan rarrasheta sai kiga ta ware tashiga cikin qannenta sun cigaba da al'amuransu,
Mahaifiyarta idan tazuba mata idanuwa takanji tausayinta saboda tasan yanzu bata wani san illar abunda yafaru da'itaba sai nan gaba idan tafi haka girma abun zaifi damunta,
Domin kwata-kwata aynzu shekarunta sha uku kacal."
Watannin sunja yayinda abubuwa dayawa sun canja amma yanayin samun gidan yau akwai gobe babu haka dai suketa ci gabada malejin rayuwarsu,
Amma kam rayuwa tayi musu zafi sosai."
____________________________________
Yanayin comment dinku yanayin yanda typing dina zaina zuwa muku
✔️ote
Comment
Share
To be continued
Zaynab Bawa
💕💞
Advertisement
- In Serial68 Chapters
Curse of the Forsaken
The betrayal and murder of a wise king chosen by the gods condemns all of mankind in the world of Althos to pending extinction at the hands of a terrible curse. Abandoned by the Gods, Fate and Hope, humanity descends into madness and immorality. Now, with most of humanity living as slaves of other races and the great human kingdom but a memory in legend, the scattered remains of the free humans cling desperately to a life worse then death. Prophecy spoke of their redemption and salvation, but as the years grind past, and humanity fades away, no sign of salvation appears. Unable to wait any longer, the last dregs of a once great people attempt to ignite prophecy on their own by summoning a young man against his will from modern day earth. Their goal is to coerced the young man into a fight for the survival of mankind in a fantasy world which is not his home. Unable to speak the language, not trained in the ways of combat, will he put his life on the line for these people who kidnapped him, or will he leave them to their fate? Surrounded by a human race warped by crushing poverty, desperation, and immorality, can he survive without losing his dignity and morality? With prophecy involved does he have a choice? Warning: Tagged 18+-this work contains mature scenes involving sexual content, torture, foul language, death, slavery, rape, cannibalism and horror. I apologize beforehand and suggest that you not read if you are offended by any of these topics. ***THIS IS THE FIRST BOOK IN A TRILOGY, THIS BOOK IS DONE AS OF 11/6/16; THE SECOND BOOK WILL BE POSTED IN JAN OR FEB 2017***
8 190 - In Serial23 Chapters
PANDORA. Hope Dies Last (ToG)
The first female was the last to die.Creation of the gods themselves, she was blessed with all the blessings...but little did she know that her existence was a curse. Within her, she held all evil, malevolence, and suffering waiting to be released at the sign of her weakening will.Sent force to the world of man with 'Curiosity', she caused the death of a world. Innocence is replaced by malice. Laughter with cries. Eternal life with mortality.Cursed for her very existence, she was the first to agree. Yet death doesn't come easily for one blessed by the deathless ones. Reborn through a greater will than the gods themselves, she is offered a chance to strike against greater powers.Reborn in a Tower of greater scale than worlds, what does she climb for? Fueled with vengeance, anger, and hatred she picks up her blade.All her blessings and curses armed against her enemies...she will see the gods fall no matter what. Her name? Pandora Despite the heavy beginning, this is a story about learning and development. The story's tone will gradually begin to lighten as her world grows brighter once more. Comedy elements included. AN: Due to the different setting, time, and plot of this fanfic from canon ToG, it can be considered more of an Original Story borrowing the world of ToG. Non-fans of ToG can read because all elements will be clearly explained and taken slowly. Enjoy! Fandom: Greek Mythology, Tower of God Disclaimer: I do not own Tower of God. That belongs to SIU and Webtoon. Image belongs to Crafterm, found on Creative Commons
8 80 - In Serial25 Chapters
Magic and Martial War God
Born with common talent, accidentally gets Supreme inheritance with the blood of his ancestor flowing in his body. He shall use Magic and Martial Arts to conquer the universe and create a future for humanity.
8 95 - In Serial12 Chapters
The Incipient Path to Demesne
Hidden from the world, the first and only VR game is being developed. By using various means, a group of talented friends manage to acquire access to the beta.Combining their skills and knowledge, they set out to rule the game, and the world thereafter.***On hiatus, will be completely rewritten.
8 92 - In Serial17 Chapters
Aro's daughter: Isabella swan
Isabella swan was left heartbroken by edward cullen. Broken and then raped by Laurent she is rescued by her father Aro volturi. And mate Cauis volturi.
8 188 - In Serial13 Chapters
{♡MCYT X READER ONESHOTS♡}
A/n:I won't be putting nsfw actions but there might (Might!) be some curse words so just a little warning =DThis is not the first story I made but it would be the first I might publish and finish.Also, small note, whenever I type something like this ---It means theres a short timeskip.
8 102

