《RAYUWAR HUSNA (hausa novel)》part 28 &29
Advertisement
🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹
*RAYUWAR HUSNA*
🌹🌹🌹🌹🌹🌹
🌹
*TAMBARI WRTER'S ASSOCIATION*
*_🔱((Home of Expert and Talented writers, da tambarinmu muke tafe domin kawo gyara da cigaban Al'umah))_*
*TWA*
*WRITTEN BY ZAYNAB_* _(zeexee)__
🅿️:2️⃣8️⃣-2️⃣9️⃣
_Bismillah_
Su Husna sun koma school, amma bata fara zuwaba, dan karayen ta ta, a hannun dama yake, so zaman gida take.
Kaman kullum, tana kwance akan gaddon ta, sai ga kira ya shigo wayarta, tana dubawa, sai taga sunan Halima, sai ta daga. Sai sukayi sallam, Halima tace mata suna son suzo ne, indai tana gida.
Ina gida, ina zani.
Toh sai munzo, ahada mana kayan dadi fa?
In Sha Allahu, ku kwantar da ankalin ku.
Yauwa matar yayanta.kafin tabata amsa, Halima ta katsai kiran.
Tin randa sukazo, kwana biyu da fixing din date, tafada masu komai, suka fara zolayan ta da matar yayan ta.
Yanzu dai bari tatashi taje ta fadama Umma, sanan ta neman masu anything suci, dan bazata iya amfani da hannun ta ba sosai, dan haryanzu yana mata radadi.
Tana kan girki, sukace mata su na bakin gate. Sai tace su shigo. Tana jin sallama, ta fito daga kitchen da gudu, taje tayi hugging dinsu.
Sannun ku dazu.
Yauwa matar yayan ta.
Sai tahada rai. Banace muku ku daina kirana sunanna ba?
Baza mu daina ba. Aisha kenan ta amsa.
Aaah, matar yayanta bada kanki asare. Halima tafada
Saitayi wani irin smile.
Hahh, wannan irin smile din fa? Aisha ta tambaya.
Ai tana fada mana dawayo ne, cewan ta bada.
Ae ai nabada. Tinda zamuyi aure. Tana fada ta hada rai.
Duk sukayi dariya. Daganan sukaje dakin umma suka gaishe ta. Umma taji dadin ganin su sosai. Daga nan sukaje dakin Husna, saita kawo musu drinks da snacks.
Please kuyi hakuri, abinci yakusan dahuwa.
Kut haka zaki rinka wa yayan ki, inya ce kiyi griki, bazakiyi ba har sai ya dawo? Halima ta tambaya.
Keh bana son rainin hankali fa, yau shai kuka kirani din, ai da kuna son abincin dawuri, sai ku kira dawuri.
Adai je akawo mana.
Ya kuke son in kawo muku? Naga alaman bazaku ci abincin ba yau.
Haka suka ita argue, har sanda suka farajin kaurin abinci. Da gudu suka je kitchen.
Suna gama ci, suka fara hira. Sunata mata hiran school.
Suna cikin hira, wayar Aisha tayi ringing, saita daga.
Shikuma Mubarak ya dawo, da Mubarak ya shiga cikin gida, yaje ya gaida umma. Ita kuma bata fada sa kawayan Husna sun dazo ba. So yana gama gaidata, ya tashi yawuce dakin Husna straight. Yana son yayi sallama kenan, yaji muryan Aisha, tana I love you too.
Haba sai zuciyan Mubarak yafara bugawa, so Husna nada saurayi, bancin shi yana nan yana mutuwan sonta, ita tana chan tana soyayya dawani. Sai kawai ya bar wajen yana huci. So haryanzu Husna bata fara son shi ba?
Advertisement
Su Husna ko suna can sunata zolayan Aisha. Allah sarki Husna, batasan yayanta ya fassara ta ba.
Su Halima sun dade sosai, sai kaman 5 suka bar gidan. Suna tashi, suka je suka sallami Umma, daga nan Husna ta raka su, bata dawo ba harsanda suka samu keke.
Suna idar da sallan Isha, ita da umma na zaune a dinning, suna shirin cin abinci, ta tambayi umma inda yayan ta yake.
Baki ganshi bane?
Ae, naga yau morning kake, ya kamata ace yadawo.
Ai ko yadawo tun karfe biyu. Amma kuma tun lokacin daya dawo ya gaishe ni, ban kara sa shi a ido ba.
Toh! Ina yaje kenan.
Ko zaki duba dakin sa ne?
Owk toh. Tana isa bakin kofar, tayi sallama.
Yana ji, amma yaki amsa mata. Sanda yaji tayi sau uku sannan ya amsa, sai ya bude kofar.
Ya akayi. Ya tambaya ba yabo ba fallasa.
Hmmm, tindama naga banganka bane, shine umma tace nazo naduba ka adaki, kuma gashi lokacin cin abinci yayi.
Toh gashi kin ganni, shikenan ko, kuma zanzo inci abinci duk lokacin da na so.
Ae. Amma yaya miyasa kake amsa min haka ne?
Ya nake amsa maki haka?
Ae, naga ko dan wasan nan dakake min ne bakayi ba.
Wasa! Kije wajan wanda kike sonsa yamiki wasa.
Bangane ba?
Bazaki gane ba ai. Tinda bake ke jin yande nake ji ba.
Toh yanzu mena make.
Ai bazaki sani ba. Ni ina nan kullum ina mutuwan sonki, kullum ina adduan Allah ya nuna min ranan dazaki zama tawa, kullum ina adduan Allah ya cire miki son Faiz, kiga yanda nake sonki. Ai ko ban fada miki ba, yanda nake miki, ai yakamata kigane ai, do you know how I feel, amma keh kina can kina fada ma wani kina son shi.
Maganan shi ya matukan bata mamaki sosai. Yaushe ita ta fada ma wani tana son shi. Amma fa 2 umma tace yadawo ko, kuma su Aisha nan a lokacin. Kardai yaji lokacin da Aisha ke waya da saurayinta ne.
Okay yanzu baki da bakin magana ko?
Nifa yaya bana son haka. Yaushe nace mawani ina son shi?
Ai bazaki sani ba. Kullum ina nan ina ji da ciwon sonki, amma ke kina can kina son wani. Waini arayuwata, one sided love zan rinka yi ne?
Yaya karinka confirming kafin kayi magana please.
Oww inrinka confirming ko, wai ke yaushe wannan kwakwal wan nan naki zai baki cewa ina son, yaushe zuciyanki zata fada miki ina sonki. Hahh, amma ina zaki sani tunda kina son wani.Abinda nake so dake yanzu, shi ne, kifita min adaki.
Duk abubuwan da Mubarak ya fada, yasa jikinta yayi sanyi. Ita bata taba tunanin ya fara sonta ba, ita tayi zaton duk kulawan dayake bata sabida condition dinta ne, kuma ya faranta ma umma rai .Wallahi yaya bana son wani.
Advertisement
Ae nasani, naji, kibar min daki.
Wallahi yaya bani bace, Aisha ce fa take magana da saurayinta?
Wata Aishan kuma?
Aisha kawata.
Yana jin haka ji wani irin kunya ta kama shi. So duk fushin dayake yi abanza ne. Kai amma yabada kansa, yanzu tasan ya damu daita. Yanzu zata fara mai nonsense.
Gaskiya yaya am disappointed. Tana fadan haka, tabar dakin.
Ya kika dade haka.
Bakomai, hira kawai muke.
Toh shikenan. Shi bazai fito yaci abinci bane?
Bansani ba?
Toh kije ki kara kiran shi.
Umma ai zai zo, yasan lokacin da muke cin abinci ai. Kumama ba fada mai.
Sai umma ta kalaita, tace ko kunyi fadan ku na sabo ne?
Haba umma mun rinka fada kenan? Mubarak yafada
Aww ashai kana jin mu. Ai nayi zaton kunyi fada ne.
Me zai samu fada, ana zaune kalau?
Nasani?
Muci abinci please, wallahi yunwa nake ji.
Acici kawai.
Na kaika.
Ya isa haka, kowa yayi facing din abincin sa. Umma tafada.
Suna gama ci, kowannan su yakoma daki.
Yaushe yafara sona ne?
All this time fa banyi noticing ba. Ya akayi haka, nida nake saurin noticing, ya akayi nayi slow wannan lokacin.
Amma ba Farida yake so ba, so yaushe ya fara sonta.This is interesting. Allah yasa dai ba show yakeyi ba.
Haka rayuwa taci gaba. Amma duk lokacin da Mubarak ya tambayi Husna ko tana sonshi, saitayi shuru, shi kuma shurunta na kona masa rai amma ya yaiya, dole ahankali zai koya mata sonsa. Shi kam yanzu ya tsumu acikin soyayyar ta. Kawai shi he can't wait for her to be his, kuma Alhamdulilah yanzu saura three weeks, so he can't wait.
*GARIN SULEJA, SECOND GATE.*
Husna ta koma gida, an fara shirye shirye, amma bai kai na lokacin auranta da Faiz ba. Yanzu ne ma tunanin Faiz yake zuwa mata fresh a memoryn ta. Inta tuna da conversations dinsu, sai tayi kuka. Harta tuna da lokacin da yakirata, kuma Salifa na wajen, take ce mai ita ashirye take, masu shiri na can sunayi. Ashai zasu rabu da rabin ranta. Inta tuna da text messages dinsa, sai ta zubar da hawaye. Allah sarki *Noorul Qalbi* . Allah yajikanka da Rahma, ya kai haske kabarinka. Kuma ko wa zan aura, bazan taba mantawa da kai ba.
Yau biki saura kwana daya. Gidan su yacika sosai. Duka cousins dinta sun zo, harda su Halima da Aisha. Taji dadin ganin kowa sosai. Sun sha hira kafun kowa yafara barci. Da taga kowan nan su na barci, sai ta tashi daga kwance ta zauna. Yanzu fa ita ba auran ke damunta ba, karshima yazo ya tafi ya barta. Dan ita tsoro take sosai. Kawai saita fara kuka. In shima ya mutu ya barta fa, shikenan, bazata kara aure ba. Haka ta ita kuka, har barci barawo ya dauke ta.
Shiko Mubarak, bakinsa ya kasa rufuwa. Yana tajin dadi. Shikenan gobe fa taza tasa. Kawai yanzu matsalar sa shine yanda zai cire mata son Faiz a zuciya. Amman shi yayi alkawari, sai ya koya mata sonsa, da har zata manta da zancen Faiz. Ya nata tunanin yanda rayuwar auran su zata gudana, bai san lokacin da barci barawo ya dauke sa ba.
Jamaa sun taru sosai, gurun daurin aure. Masha Allah, an daura auran Mubarak Musa Yero, da Asmau Abdallahi kan sadaki *****.
Ana fadama Husna, tafara wani shafin kuka na daban. Allah sarki last year, haka aka daura auranta da rabin ranta. Kuka take na fitan hankali. Kowa dai yaganta, zaiyi zaton ko tana kuka ne irin na amare, amma ita kadai tasan abinda ke damunta. Kukan nata ma sai yakaru lokacin data ga iyayen Faiz da yayansa, da kuma kannan sa. Allah sarki rayuwa kenan. Su twins ma dasuka ganta, sanda sukayi hawaye. Suda suke jin dadin cewa ita ce matar yayan su, ashai matar wani ce. Kawai auranta dayayen su na passing of time ne. Gaskiya sunso Husna sosai, amma Allah baiyi zata zama daya daga cikin familyn su ba.
Sharp sharp aka akai amarya, tunda gari mai nisa zaa kaita. Amma kafin aka samu aka fita da ita taga gida, ansha danbe, tanata kuka tana rungumai da Ammi. Da kyar aka samu aka wuce da ita.Suma iyayen Faiz, fatan alheri suka mata, da kuma Allah yasa nan shine wajan zamanta.
Motoci na nan suna jiran su, so suna sauka a airport, basu wani bata lokaci ba suka wuce gidan Hajiya Zayanb. Nan zaa fara kai amarya, kafin akaita gidanta.
Ana gama komai, aka kaita gidanta, daman gidan bayi da nisa da gidan umma. So anan new GRA Bauchi yake . Gidan yayi kyau sosai ba karya. Gaskiya gidan abun azo agani ne.
Ita dai Husna duk abunda mutani keyi bai damai ta ba. Ita dai taga yau dinnan ya wuce, kuma yayanta na raye.
Da kowa yawatse, Mubarak ma yayi sallam da abokanan sa, ya shiga gida, da normal abubuwan da ake siya na first night din aure. Husna najin mostin sa, zuciyarta tafara bugawa. Shikenan shima ya kusan mutuwa. Tana jin ya murda kofar dakin, ta saki wani ihu, shikenan shima ya mutu.
_Thanks for reading, please comment. It's your comments that motivates a writer._
Love💖
_Zeexee_ 🌹💜💖💞
Advertisement
- In Serial7 Chapters
Pouch and Bloodied blades
Ter is a Tiv Demi-god born from a powerful ancestral spirit and a female sacrifice that survived where she should have died. He was ostracized growing up and eventually sold to the slave traders to be taken across the ocean. He meets Uche on the ship and they bond over the shipwreck that Uche unwittingly causes. Shunned by his people, he is content to roam the world with his companions; living his life to the fullest while also seeking out his sire. Uche is of royal blood, consecrated to the gods at birth. His house is betrayed by his father’s cousin and exterminated. Uche is sold to slavery instead of murdered for fear of possible repercussion due to his connection to the spirits. Uche is concerned with cultivating himself to godhood. He seems to hold no animosity for his past but has developed an aversion for needless slaughter and conquest. Sarauniya (Amina) is a princess of the great empire of Zazzau who is on the journey to gain power by any means necessary. Her goal is to be acknowledged by the empire’s governing council and crowned Empress in her own right. She faces the moral dilemma of what to do with her younger brother who is currently in line to inherit after displacing her. Will she forsake immortality for the opportunity to rule the Zazzau Empire and change the lot of all the women in her time? Or will she become a free immortal? Join the trio as they will wander across the continent and interact with various African cultures, deities and legends on their journey to ascension.
8 172 - In Serial20 Chapters
Creation Records
A boy got reincarnated in Another World. With the power he regained from his forgotten past, he used it to create a mighty force. Will he become an Anti-Hero that would dominate the new world? And will he become the world's strongest? This is a story of a boy reaching the top of the world as he recovers the memories of his mysterious past.
8 122 - In Serial11 Chapters
Not So Bold
A store clerk wakes up one day in a body not his own. Then wakes up back in his bed, it was just a dream. Right? He soon finds himself living a duel life, bouncing between his mundane life as a shelf stuffer and a strange new one. One where he has floppy ears and itty bitty paws. Notice of Hiatus: At the moment I'm going though a bit of turbulence and won't be able to update for a while. I'm also unsure about weekly/monthly releases. I'm considering writing a large group of chapters then posting them all at once or otherwise setting up releases in a way that makes sense. I'm still figuring out how to go about this particular endevor and thank you for your patience.
8 94 - In Serial54 Chapters
The Samsara Dirge: Adventures in Post-Apocalyptic Broadcasting
It was not the apocalypse anyone expected. They called it the Changes. (Which might sound boring, though it was no such thing!) During this time, reality itself was suspended. Anything could happen, and often did. Who could have anticipated flying turtles, lighter than air futons, the appearance of the color slurkle, or the eradication of differential calculus? After a year and a half of such wonders, it all stopped. The world was not the same, nor the people in it. Why had it happened and how did it end? Would it return? No one knew. Silverio Moreno, irrepressibly optimistic host of one of the most popular post-apocalyptic gameshows, wants answers. And the truth might just bring in his highest ratings yet!
8 499 - In Serial73 Chapters
IMAGINES ❤️
Random imagines about you and Kendall Jenner. Feel free to request some stories. Thank you guys! GXG only. G!F but no smut. 😂 I don't know how to write it. Just kidding! There's SMUT inside. 👌🏼
8 194 - In Serial11 Chapters
Braden x Oc
8 119

